Bayanai Game da Tsafi, Bokanci da Maita
بيانات حول السحر والشعوذة
Engr. Baba Magaji
B ÃKA DA SAURAN TAMBAYA
GAME DA
TS ÃFI, B ÕKANCI DA
MAITA.
WALLAFAR
ENGR. BABA MAGAJI .
1
1
GARGADI:
Wannan littãfi ba’a rubũtãshi d õmin a k õyar da ɗaya daga cikin tsãfi, bõkanci
ko maita ba, Jakar Magõri ce mai ɗauke da ɗibbul Anbiyã (Amincin Allah
Ya kasance a garesu).
Mawallafin yã rubũta wannan littãfi ne da nufin haskãwa sabõda abũbuwan
da suke cikin duffai su fito fili kõwa ya zama mai iya wãrewa tsakãnin
kyãwawa da mũnãnã:
1. tsakãnin karãma da tsãfi,
2. tsakãnin neman tsari da neman halaka ,
3. tsakãnin rõƙon Allah da rõƙon Aljani,
4. tsakãnin istihãra da dũbã ,
5. tsakãnin Kanbun baka da Maita ,
6. tsakã nin fasãhar zãmani da fasãhar matsãfa ,
7. tsakãnin harsãshe da Lãbãrin gaibu, Da sauransu.
Duk wanda ya karanta wannan ƙaramin littãfi, idan Allah Yã yarda, zai zama
gwani wajen banbancewa tsakãnin wa ɗannan abũbuwa da suka gabãta. Zai
zama Magõrin kansa da ka nsa.
Akwai buƙãtar mutum ya kasance yana mai jin tsoron Allah idan yana
karanta wannan littãfi, ya ƙãra tsoron Allah bayan yã gama karantãwa sannan
ya bi hanyar da nayi n ũni mafi dacewa da Sunnah.
Duk wanda ya karanta wannan littãfi sannan ya zã ɓi son ran sa (koma bãyan
yadda Sunna h ta zã ɓar), to ya tabbatar yã kauce ma hanya madaidaiciya.
Allah Ya kiyãye mu.
مِنْكُمْ مَنْ يُرِيدُ الدُّن ْيَا وَمِنْكُمْ مَنْ يُرِيدُ اْلْخِرَةَ
2
2
SADAUKARWA
Ga yan -uwa da abõkan arzi ƙi, ma’ab õta umarni da kyã wãwan ay yuka da
hani da ab ũbuwan ƙ i (waɗanda basu halasta ba ).
3
3
GABATARWA.
Da sunan A llah Mai Rahama Mai Jin kai, Mahaliccin Sammai da Kasa da
abubuwan da suke cikinsu –Wanda Ya sanar da mutum game da Na’ura mai
kwakwalwa ( Computer ). Tsira da aminci su tabbata ga fiyeyyen halitta
wanda bai fa ɗi wata magana son ransa ba –Muhammadu manzon Al lah
(S.A.W) – masanin da ya kõyar da dũniya ilimin da Allah (SWA) Ya sanar
dashi kamar yadda aka umarceshi . Allah Yayi da ɗin tsira ga iy ãlensa da
Sahabbansa gaba ɗayansu. Amincin Allah a garemu da b ãyin Allah Salihai.
Bayan haka, kasancewar a wannan z ãmanin namu, banba ncewa tsak ãnin
kyãwãwan dab ãru da suka sh ãfi neman tsari da m ũnãna suna ƙãra ɓõyewa a
cikin duhu, ana halasta m ũnãna kuma a ɗõra ganin ky ãwãwa m ũnãna, sai
naga ya d ãce in karanta ãyõyi daki -daki, kuma d õmin hanyar masu laifi ta
bayyana .
Ina r õƙon Allah Mai girma da ɗaukaka, Ya b ãni ikon bay ãni da zai fayyace
waɗannan bat ũtuwa da na ɗauko, har ya zan na gama amsa tambay õyin da
mai karatu zai iya tambaya.
Nã yi niyyar bay ãni a game da ts ãfi, bõkanci da Maita da dangin wa ɗannan
laifuka ba tare da jin ts õron wanin Allah (SWA) ba. In Allah Ya yarda, zanyi
bayãni akan wa ɗannan laifuka da danginsu kamar yadda Allah (SWA) Ya
bãni ikon fahimta. Zan k ãwo irin nau’in tsari da shari’a ta yarda da su, da
abũbuwan da marar l ãfiya zai aikata (ko a aikata masa ) domin neman samun
waraka. Dukkan wa ɗannan, halastattu in Allah Ya yarda.
Ina ƙara jan hankalin mai karatu, idan na bada misali nace Annabi (SAW) ya
hana, to yaji ts õron Allah, kar ya gwada wannan misãlin (kawai suna n ũni ne
don hanyar mai laifi ta bayyan a (ta fito f ĩli))! Kar ka fahimta da kuskure,
misali shine nace: idan b õkaye sunga taur ãro mai sifa kaza a sama sai suce
za’ayi ruwa kuma Annabi (SAW) yace duk wanda ya yarda da cewa an samu
ruwa sabõda tsayuwar taur ãro kaza to ya kafirta da sakon (musulun ci) da
annabi (SAW) yazo dashi. To anan kar mai karatu ya zama ya ɗau wannan
misalin (na ganin taur ãron) yana amfani dashi.
4
4
Ba lalle in kwatanta maka misãlan dai-dai ba, amma zanyi ƙõƙari in gwada
maka yadda zaka fahimci m ãlamin da b õkancinsa (s ãɓãnin ist ihãra) a l õkacin
da yake so ya maka (taimakon) wani magani (ko addu’a).
Gaskiya ce za n fayyace ba t ãre da ts õron kaidin mai kaidi ba, Kuma ka ce:
"Gaskiya tã zo, kuma ƙarya t ã lãlãce. Lalle ne ƙarya ta kasance
lãlãtacciya." (17:81)
Ka ce: "Ina yi muku wa´ azi ne kawai da kalma guda! watau ku tsayu
dõmin Allah, bibbiyu da ɗaiɗai, sa´an nan ku yi tunãni, bãbu wata
hauka ga ma´abũcinku (Annabi Muhammadu (SAW)) . Shĩ bai zama ba
fãce mai garga ɗi ne a gare ku a gaba ga wata azãba mai tsanani.
Ka ce: "Abin da na rõƙe ku na wani s ãkamako, to, amfãninsa nãku ne.
Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Allah, kuma shi Mahalarci ne a kan
dukan kõme."
Ka ce: "Lalle Ubangijina Yanã jefa gaskiya. (Shi) Masanin abũbuwan
fake ne." Ka ce: "Gaskiya t ã zo, kuma ƙarya (ta ɓata ɓat) bã ta iya ƙara
(kome) kuma bã ta iya d ãwõwa." Ka ce: "Idan na ɓace, to, inã ɓacewa
ne kawai a kan kaina …
Engr Baba Magaji .
bamagaj@gmail.com
27 Febuary, 2018.
(11Jimada II, 1439)
5
5
BÃBI NA FARKO
TSARIN FÃRA KAR ATU N LITTAFI .
Bismill ãhir Rahm ãnir Rahim. Wassal ãtu was salam ala Ras ũlullah (SAW).
Kafin mai karatu ya fara kutsawa cikin wannan littafi, yana da kyãwu ya sanya kayan
(sulke) da zasu taimaka ya shiga ya fito ba tare da s ãmun matsala ba. Kayan sulke anan
yana nufin ab ũbuwan da mutum zai sanya a cikin z ũciyarsa yayi ĩmãni da su, ĩmãni na
gaskiya . Ba t ãre da na kaika da nisa ba, ina nufin “Tauhidi”
1.1 TAUHIDI:
Yana daga cikin tauh ĩdi, na rub ũbiyya ! Tauh ĩdin rub ũbiyya (daga kalmar Rabbu –
Ubangiji) shine mutum ya yarda akwai Allah ( Ubangiji ). Ka yarda har cikin z ũciyarka
(kuma ba mai canza maka yardar) cewa Allah ne Ya halicci k õmai da k õme, kuma Shi
ɗaya ya cancanta a bauta maS a. Shi ka ɗai ya cancanta a r õƙa (ko meye) a wurinSa.
Shine Yake b ãda arzi ƙi (dũkiya) ga wanda Yaso, Shi ne Yake ƙaddar ãwar ab ũbuwa (su
kasance). Shi ne Mai warkarwa, Mai kar ɓan rãyukan halittu a l õkacin mutuwarsu.
Tauh ĩdi na Ulũhiyya , (daga ka lmar IL ÃHU) shine mutum yayi ĩmãni (har z ũciya) cewa
Allah Ka ɗai Shi ne IL ÃHU da zai bautawa kama r yadda Yayi umarni. Sallar mutum, da
yankansa (na zubar da jini) da (komai na) r ãyuwarsa, da mutuwarsa su zama ya sallama
su ga Allah Ubangijin t ãlikai. (wato ya kasance ba zai aikata komai ba sai kamar yadda
Allah (SWA) Ya ce a aikata). Neman tsari, nema n gãfara, neman mulki, kar ãtun
Alƙur´ãni mai girma, neman mafita da dukkan addu õ’i su kasance Allah –ILÃHU za a
nufa da su (ba wani gunki ba) .
Tauh ĩdin Sũnãye da Siffõ fin Allah, shine mutum ya taƙ aita yardarsa (im ãninsa) ga iya
Sũnãyen Allah da Siff õfinSa da suka zo a cikin Alƙur´ãni da ingantattun H adisai. Ya
kasance (ga mis ãli) ya yarda Allah (SWA) yana d a siffar Ji (Zai iya jin r õƙon mutum
daga k õ’ina a cikin d ũniya (sama da ƙasa)) kuma ba za a ƙirƙira wani s ũna a ro ƙeShi
dasu ba (Sai da s ũnayenSa da Yace naSa ne!).
Alhamdulill ãhi! wa nnan (tauh ĩdai uku) su ne sulke na farko, kuma t ũbali da zai baka
damar gane bayanen cikin wannan litt ãfi. Su ne nã’ũrõrinmu na tantance (neman tsari)
kyakkyawa daga m ũnãnã, da sauransu .
Sulke na biyu, ƙãri akan tauh ĩdi rub ũbiyya , mai kar ãtu ya yarda Alla h (SWA) Shi yake
ƙaddara dukkan k õmai, a lõkacin da Ya so . Mai kar ãtu yayi imãni cewa ts ãfin mats ãfi
baya t ãsiri sai Allah (SWA) Ya bari (abun ya faru) sab õda hikimarSa da cika
alƙawarinSa kamar yadda Ya rub ũta (tun asali) abun zai fãru ta wannan dalilin . kuma
Yana yin afuwa a bisa (rubũtattun ab ũbuwa) masu yawa.
6
6
Wajibi ne mutum yayi ĩmãni cewar duk wani hatsabibi (mats ãfi, bõka, m ãye, azz ãlumi)
bai fi ƙarfin Allah ba. "Kuma kada ka yi zaton Allah Mai shagalã ne daga abin da
azzãlumai suke aikatãwã. Abin s ani kawai, Yanã jinkirta musu ne zuwa ga wani
wuni, wanda idãnuwa suke fita turu -turu a cikinsa." (14:42)
Abu na karshe da mai karatun wannan litt ãfi zai amince shine ya yarda zai hanu da
dukkan ab ũbuwan da zan k ãwo haninsu daga Allah (SWA) a cikin Alƙur´ã ni, ko hanin
da zan k ãwo (cewa) daga Manzon Allah (SAW). Allah (SWA) Yana cewa:
Yã ku wa ɗanda suka yi ĩmãni! Ku kar ɓa wa Allah, kuma ku kar ɓa wa Manzo,
idan Ya kirãye ku zuwa ga abin da Yake rãyar da ku; Kuma ku sani cewa Allah
Yanã shãmakacewa a tsakãnin mutum da zũciyarsa, kuma lalle ne Shĩ, a zuwa
gare Shi ake tãra ku. (8:24)
Kuma Manzon Allah (SAW) yan a cewa : Duk abinda na haneku, ku n ĩsanceshi. kuma
abubuwan da na umarceku dasu, ku z õ dashi gwalgwadon abinda ya
sauwaka.
GARGA ƊI:
Dukkan wanda imãninsa ya gur ɓãta daga tauh ĩdi (na rub ũbiyya, ko na Ul ũhiyya, ko na
Sũnãye da siff õfin Allah) wajen aikin ibada , wannan shi ake cewa “Mushiriki” (w ãto
mai ha ɗa Allah (SWA) da wata halitta a wajen bauta). Kãfiri bai ma yi im ãni da
kaɗaitakar Ubangiji (Allah) ba, ballantana ya ƙudurta tauh ĩdi a cikin zuciyarsa.
Misãlin m ushiriki shine wanda zai yanka wata dabba ya ɗõra niyyar y ã zubar jininta
sabõda Allah Ya amsa addu’ arsa (ko yayi sadaka da wani n ãmanta) sannan sauran
nãman sai ya sarraf ãshi ta mum mũnar hanyar kyauta ga Aljanu (ya je gidan tur ũrũwa
ya zuba) cikon neman biyan bu ƙatarsa.
وَجَعَلُوا ّلِلِهِ ِمِها ذَرَأَ مِنَ اْلَْرْثِ وَاْلَْن ْعَامِ نَصِيبًا ف َقَالُوا هَذَا ّلِلِهِ بِزَعْمِهِمْ وَهَذَا لِشُرَكَائِنَا فَمَا
كَانَ لِشُرَكَائِهِمْ فََلَ يَصِلُ إَِلَ اّلِلهِ وَمَا كَانَ ّلِلِهِ ف َهُوَ يَصِلُ إَِلَ شُرَكَائِهِمْ سَاءَ مَا َيَْكُمُونَ
Kuma sun sanya wani rabõ ga Allah daga abin da Ya halitta daga shũka da
dabbõbi, sai suka ce: "Wannan (kason) na Allah ne," da riyãwarsu "Kuma
wannan na abũbuwan shirkinmu ne ." Sa´an nan (ka sani) Abin da ya kasance na
abũbuwan shirkinsu, to, bã ya sãduwa zuwa Allah, kuma abin da ya kasance
(wanda suka ce) na Allah, to, shĩ yanã sãduwa zuwa ga abũbuwan shirkinsu. Tir
da hukuncinsu! (6:136)
7
7
BABI NA BIYU
GAME DA TS ÃFI
Tsãfi (ko sihiri) ya kasu kashi daban daban. ba tare da cewar d õle sai an bayar da
ma’anar ts ãfi ba, zamu iya fahimtar menene tsãfi a lõkacin da muka ɗauko bay ãnin rabe
rabensu.
mats ãfa sukan yi tsãfi ne sab õda wassu dalilai kamar:
1. nũna bajinta .
2. cũtar da ab õkin g ãba.
3. neman s ãmun r ĩba ko cin nasara akan wani batu (kamar aure)
4. Sana’a.
5. Neman waraka daga wata jinya
2.1 TSÃFI SABÕDA NŨNA BAJINTA.
2.1.1 Tsãfi lõkacin wasanni :
Da yawan mats ãfa sukan yi tsãfi ne lõkacin wasanni sabõda su nũna bajinta, bajintar sai
ta jãwo musu ɗaukaka a wurin jama’a. A wani l õkaci (kamar ranar wani biki na al’ ãda)
akan t ãra jama’a mats ãfa su zo k õwa ya nuna irin kwarewarsa ta tsãfi, jama’a suyi ta
kũwa ana s ãmun nish ãɗi. Daga cikin sana’oin haus ãwa, akwai wa ɗanda w ãsanninsu ya
shahara da n ũne nũnen ts ãfi. Wasanni irin na wanz ãme, mafarauta da ma ƙera suna daga
na gaba -gaba a jerin wãsannin da ake nũna tsafe -tsafe. Mafi yawan tsãfi da akeyi a
lõkutan w ãsanni yana daga cikin nau’in tsãfi na rufa ido.
2.1.2 Tsãfi na rufã ido: tsãfin ruf ã ido yana f ãruwa ne a lõkacin da mutum ya zo da
wata da bãra wacce take ɓõye ainihin (ha ƙĩƙanin) yadda abu yake, sai mut ãne su ga abun
tsãfin nãsa da wata siffa da bashi da ita a z ãhirin gaskiya.
Mu ɗauki mis ãlin igiya. A zãhirin gaskiya, idan aka jefar da igiya ba z ata motsa ba,
kuma siffar igiya daban take da ta maciji. Mai tsãfin rufa -ido zai iya ya zo da wa ssu
dabãru (na sihiri) sai ya ar õ siffõfin maciji ya ɗõrasu akan igiya, sai mut ãne su ɗõra
ganin igiya t ã zama (kumurcin) mac ĩjiya tana m õtsawa.
Irin wannan tsãfi (na ruf ã ido da igiya) shi ne k ãfiran lõkacin Annabi Mũsa (A.S) suka
ƙwarai akai. Da irinsa ne suke t ãƙama da ganin cewa za su rinjayi Mu’ujizar Annabi
Mũsa (A.S) .
Yadda lãbãri n yake:
8
8
Lãbãrin Annabi Mũsa (A.S) da mats ãfa.
A lõkacin da Allah (SWA) Ya a iki Annabi M ũsa Alaihis Salam (da Ma nzanci) zuwa ga
mutãne n (zãmanin) Fir’auna, Y ã bã shi al ãmar (da ake kira mu’ujiza) da zai n ũna sabõda
mutãne su yarda da manzancinsa (idan sunga wannan alamar).
“Dãman Allah (SWA) Yana bawa Manzanni (Alama r) mu’ujiza , ba ɗaya
ba, sabõda ta kasance shaidar da idan mut ãne sun gani su yarda da
manzancinsu”
Yana daga Mu’ujiz õzin Annabi Mũsa (A.S), a duk lõkacin da yakeso ya n ũna
(mu’ujizar) idan yai Bismillah ya jefar da sandarsa sai ta zama mac ĩji! idan ya k ãma
macijin sai ya dãwo sanda rsa na asali. Wannan ba tsãfi bane, sanyewar Ubangijin halittu
ne ga Manzanninsa, wannan sanyewar da aka bãshi ita ake kira mu’ujiza.
Annabi Mũsa (A.S) da ɗan-uwansa H ãrũna, suka je wurin Fir’auna (kamar ya dda Allah
Ya umarcesu) sukace masa:
...Lalle mũ, Manzanni biyune na Ubangijinka, sai ka saki Banĩ Isrã´ĩla tãre da mu.
Kuma kada ka yi musu azãba. Haƙĩƙa mun zo maka da wata ãyã daga,
Ubangijinka. Kuma aminci ya tabbata ga wanda ya bi shiriya." "Lalle mũ,
haƙĩƙa, an yi wahayi zuwa gare mu, cewa azãba tanã a kan wanda ya ƙaryata,
kuma ya jũya bãya."
(Fir’auna) Ya ce: "To, wãne ne Ubangijinku? Ya Mũsã!" (Annabi Mũsa ) Ya ce:
"Ubangijinmu Shi ne wanda Ya bai wa du kkan kõme halittarsa, sa´an nan Ya
shiryar."
(Fir’auna) Ya ce: "To, mene hãlin ƙar nõnin farko?" (Annabi Mũsa ) Ya ce:
"Saninsu yanã a wurin Ubangijĩna, Ubangijĩna bã Ya ɓacewa kuma bã Ya
mantuwa." (20:47-52)
Haka dai Annabi Mũsa yayi ta bay ãni a Fir’aun a da mutãne nsa, daga karshe Fir’auna
yace: "Idan kã kasance kã zo da wata ãyã, to ka k ãwõ ta, idan kã kasance daga
mãsu gaskiya." Sai (Annabi M ũsa yace ga ãya ) ya jefa sandarsa, sai gã ta kumurci
bayyananne! Kuma ya fizge hannunsa (daga hamatarsa) , sai ga shi fari (fat, kamar
madara) ga mãsu dũbi!
(Nan danan akayi ƙus -ƙus), Mashãwarta daga mutãnen Fir´auna suka ce: "Lalle ne,
wannan, haƙĩƙa, ma tsãfi ne mai il imi." " Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku: To,
(amma) mene ne kuke sh ãwartawa?" Suka ce: "Ka jinkirtar da shĩ (kace ya dakata ba
yanzu ba) , shĩ da ɗan´uwansa, kuma ka aika da mãsu ga yyar mutãne a cikin garũruwa.
"Su zõ maka da du kkan matsãfi, mai ilmi." (sai ayi shawara) . (7:106 -112)
9
9
(Fir’auna ya jũyo) Ya ce: "Shin kã zo mana ne dõmin ka fitar da mu daga ƙasarmu
game da sihirinka (na tsãfi), yã Mũsã?" "To, lalle ne munã zo maka da wan i sihiri
irinsa. Sai ka sanya wani wa´adi (na lõkacin tãruwa) a tsakãninmu da tsakãninka ,
bã mu sã ɓa masa mũ, kai kuma bã ka sã ɓãwa (kar kowa ya sã ɓãwa lõkacin ), (mu
haɗu) a wani wuri mai dãcewa."
(Annabi Mũsa ) Ya ce: "Wa´adinku sh ĩ ne rãnar ƙawa (da ake adõ –kamar r ãnar
biki) kuma a tãra mutãne da hantsi." (20:57-59)
Kuma Matsãfa suka je wa fir´aunã (suka t ãru) suka ce: "Lalle ne, shin, Munã da ijãra
(lãdã da za’a biya mu) , idan mun kasance mũ ne marinjaya?" (Fir’auna) Ya ce: "Na´am
kuma lalle ne (ƙãri akan lãdã) kunã a cikin makusanta." (7:113 -114)
Rãnar ƙure maƙaryata (mats ãfa): Sai Fir´auna ya jũya, sa´an nan ya tãra
mugunyar dabãrarsa, sa´an nan kuma ya zo. (aka shirya waje, ya shiryu).
(Annabi) Mũsã yace musu, "Kaitõnku! Kada ku ƙirƙira ƙarya ga Alla h har Ya
tumɓuke ku da wata azãba. Kuma wanda ya ƙirƙira ƙarya, yã tã ɓe."
Kamar z ã su yarda da shawarar Annabi Mũsa , sabõda sun san lalle ƙaryar z ã su ƙirƙira;
Sai suka yi jãyayya ga al´amarinsu a tsakãninsu kuma suka asirta gãnawa
(gãnãwar sirri) . Suka ce : "Lalle ne wa ɗannan biyun (suna nufin Annabi Mũsa da
Hãrũna), haƙĩƙa masihirta ne (mats ãfa) sunã nufin su fitar da ku daga ƙ asarku
game da sihirinsu kuma su tafi da tabĩ´arku mafĩficiya." (abinda yafi d ãcewa) "Sai
ku ha ɗa dabãrarku sa´an nan kuma ku tafi a sahu guda, kuma haƙĩƙa, wanda ya
rinjãya, a yau, ya rabbanta." (20:62-64) sai suka d ãwo daga meeting na sirri ;
Suka ce: "Ya Mũsã! Kõ dai ka jefa, kõ kuwa mu kasance, mũ ne, mãsu jefãwa (da
farko) " Ya ce: "Ku jefa (ku fara jef ãwa)"
To a 1õkacin da suka jefa (wasu igiyoyi) , suka sihirce idãnun mutãne kuma suka
tsõratar da su; Kuma suka je da tsãfi mai girma."
kãfin mu ɗõra, mai kar ãtu ya l ũra da wannan ãyar Alƙur´ãni ta sama. A lũra da “ suka
sihirce idãnun mutãne kuma suka tsõratar da su; Kuma suka je da tsãfi mai
girma.” Amma me ya faru da suka sihirce idanun mutãne ?
"Sai gã igiy õyinsu (da suka jefa) da sandunansu anã sũrant ãsu a gare shi, daga
sihirinsu, lalle sunã tafiya da sauri.
10
10
Lalle sun aikata tsãfi mai girma igiyõyi da sanduna sun zama macizai su na tafiya da
sauri. har sai da mut ãne suka ts õrata. Sai (Annabi) Mũsã ya ji tsõro a cikin ransa.
Allah Ya ce (masa) : "Kada ka ji tsõro. lalle kai ne mafi ɗaukaka."
To, a lõkacin da suka jefa (igiy õyin suka zama suna tafiya da sauri sai Annabi ),
Mũsa ya ce: "Abin da kuka zo da shi sihiri ne. Lalle ne Allah zai ɓãta shi. Haƙĩƙa
Allah bã Ya gyãra aikin ma ɓarnata. "Kuma Allah Yanã tabbatar da gaskiya da
kalmõminSa, kõ dã mãsu laifi sun ƙi." (10:81 -82)
Sai Allah (SWA) Yayi wahayi zuwa ga Annabi Mũsã cewa: "Ka je fa sandarka (za ta
cafe abin da suka aikata. Lalle ne abin da suka aikata mãkircin masihirci ne kuma
masihirci bã ya cin nasara a duk inda ya je (20:69))" Sai gã ta tanã lãƙumar (tana ha ɗiye)
abin da suke ƙarya da shi! Gaskiya ta auku, kuma abin da suke ai katãwa ya ɓãci.
(7:117 -118)
Sai (Allah Yayi ikonSa) aka jefar da masihirtan sunã mãsu sujada, suka ce: "Mun
yi ĩmãni da Ubangijin Hãrũna da Mũsã." Ya ce: "Kun yi ĩmãni sabõda shi a
gabãnin in yi muku izni? Lalle shĩ, haƙĩƙa, babbanku ne wanda ya sanar da ku
sihirin! To, lalle ne zan kakkãtse hannayenku da ƙafãfunku a tarnaƙi kuma lalle
zan tsĩre ku a cikin kututturan itãcen dabĩno, kuma lalle zã ku sani wanenmu ne
mafi tsananin azãba kuma wãne ne mafi wanzuwar (azãba)."
Suka ce: "Bã zã mu fĩfĩta ka ba fauf au a kan abin da ya zo mana na hujjõji. Munã
rantsuwa da wanda Ya ƙãga halittarmu sai ka hukunta (duk) abin da kake mai
hukuntãwa, ai kanã ƙãre wannan rãyuwar dũniya kawai ne (ka mutu) ." "Lalle
mũ, mun yi ĩmãni da Ubangijinmu dõmin Ya gãfarta mana laifuffuk anmu da abin
da ka tĩlasta mu a kansa na sihiri. Kuma Allah ne Mafi alheri, kuma Mafi
wanzuwa." (20:70 -73)
Sa´an nan (duk da haka) bãbu wanda ya yi ĩmãni da Mũsa fãce zuriya daga mutãnensa,
a kan tsõron kada Fir´auna da shũgabanninsu su fitine su. Lalle, h aƙĩƙa, Fir´auna
marinjãyi ne a cikin ƙasa, kuma lalle shĩ haƙĩƙa, yanã daga mãsu ɓarna. (Alƙur´ãn 10:83)
To kã ji yadda l ãbãrin ya kasance tsakãnin Annabi M ũsa (A.S) da Mats ãfa. N asan ka ji
dãɗin wannan l ãbãri (daga Alƙur´ãni mai girma). Ab ũbuwan da z ã mu lũra dasu daga
cikin wannan lãbãri sune:
1. Matsãfa n Fir’auna sun zo da tsãfi mai girma .
2. Sihirce idanun mutãne su dinga ganin igiy õyi da sanduna (ko waninsu) suna
tafiya tsãfi ne babba.
11
11
3. Tsãfi yana ts õratar da mutãne (a lõkacin da suka ga wani abu ya canza zu wa wata
halitta)
4. Matsãfa sun san cewa tsãfi dabãrun ƙarya ne (yaudara ce).
5. Matsãfa suna tsãfi ne don su sãmu wani l ãda ko kusanci ( ɗaukaka /recognition )
Irin wannan nau’in sihirce id ãnuwan mut ãne su dinga ganin ab ũbuwan da ba haka suke
a zãhirin gaskiya b a shi ake cewa (sunansa) Sihiru t Takhyil . Mu ɗauke shi da sunan
rufã-ido.
kuma bisa l ũra da wannan lãbãri n ne masu fassara suka fassara ma’anar sihiri da cewa
shine:
sarrafa wani abu daga ha ƙiƙanin (siffarsa) ya zuwa wata sifa ta daban.
Wasu mutãne suka ce ai shine fitar da (siffar) ƙarya daga ainihin siffar gaskiya.
Bangar õrin Sihirin ( tsãfi) rufã-ido sune:
1. Mutum yana ganin abu marar m otsi (a ha ƙĩƙa) ya zama yana jujjuy ãwa.
2. Mutum ya ga ƙanƙanin abu ya k õma babba .
3. Mutum yaga wani abu ya riki ɗe (daga ha ƙĩƙanin sifar sa) yã kõma sifar wata
halitta
Da wa ɗannan bay ãnai da hujj õji (kafin mu zo ga wassu) zã muga cewa masu wasan
wanz ãme wa ɗanda suke kiran zab ĩra tayi tafiya, Matsãfa ne! masu maida wani abu J ãriri
Matsãfa ne! masu fitar da jini a jikin it ãce Matsã fa ne, da sauransu. ƴan farauta masu
yin z õmo, ko tãda zuma idan sun cire h ũlunansu duk Matsãfa ne.
tsãfin ruf ã ido bai tsaya a nan ba, ya gangaro ƙasa har wurin m ãtã da sam ãri. Idan aka
ba mutum wani kwalli (mai ha ɗe-haɗe wanda wassu suke kira idonki id õna) sai mutum
ya sanya ya rikide zuwa kyakyawa, to ya sani y ã yi tsãfi! sai ya t ũba ya daina.
Idan mace tayi ƙarin gãshi da ƙare-ƙaren tudun r õbõbi a wassu sassan jikinta har ta canza
kamanni mutãne suka ganta t ã kõma babba (daga ƙarama) ta yi tsãfi! Amma yã banbanta
da irin (babban) tsãfin tafiyar da sandararren abu.
Tsãfi n mãtã da ya sh ãfi kwalliya (wanda ya hala sta) shi ne na asali da ake yinsa da kayan
make -up (Ja gir a, jan b ãki da kwalli marar ha ɗi), lalle , warwaro ɗan-kunne da sar ƙa...
…kuma kada su bayyana ƙawarsu (kwalliyarsu) fãce abin da ya bayyana daga
gare ta, kuma su dõka da mayãfansu a kan wuyan r ĩgunansu, kuma kada su nũna
ƙawarsu (kwalliyarsu) fãce ga mazansu ko ubanninsu ko ubannin mazansu, ko
ɗiyansu, ko ɗiyan mazansu, ko ´yan´uwansu, ko ɗiyan ´yan´uwansu mãtã, kõ
12
12
GÃDALI (Yana kamã da Al’basa) mãtan ƙungiyarsu, ko abin da hannãyensu na dãma suka mallaka, ko mabiya
wasun mãsu bukãtar mãta daga maza, kõ jãrirai wa ɗanda. bã su tsinkãya a kan
al´aurar mãtã. Kuma kada su yi dũka da ƙafãfunsu dõmin a san abin da suke
ɓõyewa d aga ƙawarsu. Kuma ku tũba zuwa ga Allah gabã ɗaya, yã ku mũminai!
Tsammãninku, ku sãmi babban rabo. (24:31)
Yadda ake gudanar da tsãfin rufa ido:
Kafin mu duba yadda ake ha ɗa dabãrun tsãfin ruf ã ido, ga bay ãnin yanda ake gud ãnar
da tsãfin rufa ido.
➢ A lõkacin da mai tsãfi zai n ũna gwanintarsa ta tsãfi, bayan ya gama shiryo
kãyayyakin da zaiyi tsãfin da su, wani l õkaci zaiyi kir ãri (da alw ãshi iri iri) da
fãriyar nuna isa. Sannan sai ya karanta wassu s ũrũtai ya ambaci wassu s ũnãye (na
aljanu) yayi rantsuwa dasu sannan ya r õƙesu cewa su amsa masa su aikata masa
buƙãtarsa. Mis ãli yace su kawo masa j ãriri su saka shi cikin tsumma n da ya na ɗe.
ta irin wannan hany õyi ne tsãfin ruf ã ido yake gud ãna.
➢ Wasu masu wasan na tsãfi, an sanar dasu wasu it ãtuwa (ko g ãdali) wanda za su
shafa a jikinsu su taho filin wasa. matu ƙar basu
wanke g ãdalin ba (kuma basu shiga cikin gida ba),
sai suyi ta yanka jikkunansu wu ƙa ba z ã ta
yanka ba. Wannan ma tsãfi ne na ruf ã ido,
sabõda ana iya ɓãta tsãfin kuma akwai
ƙã’idar cewa ba za ’a shiga gida ba idan an
shãfa gãdalin . Ba mãmãki akwai wassu sharu ɗɗen.
➢ Wasu masu wasan tsãfi, dab ãra ce suke yi sai tsãfi ya gud ãna. Sukan sãmu b ũtar
duma (mai kama da tũlũ ) su cika da ruwa. bayan sunyi kir ãri sun um arci ruwa kar
ya zube, sai su kifa wannan butar b ãkinta ya kalli ƙasa. Sabõda rashin iska
(pressure ) ruwa ba zai fito ba.
Wasu kan s ãmu kw ãkwã, su hũda ƙaramar ƙ õfa ta yadda (da sirinji –allura) zasu
mãtsa ruwa (launin jini) su tura gãshi, sannan sai su tõ she ƙ õfar da cãkina (gyaɗa
wacce mata suka mãtse mayinta) . A lõkacin wasa, ɗan-kõronsu zai kawo wannan
kwakwar. B ayan sunyi kirãri sunyi ƙarerayi sai suce a fasa kwakwa za’a samu
jini da gãshi. Waɗannan dabaru ne da idan aka aikata a filin w ãsa tsãfi sunan su .
Niyyar wanda yayi wasan don y a nũna burgewar tsãfi ne. Dã yãsan kõw a yasan
13
13
wannan ba wani dabo bane, dã ba zai y ĩ shi a f ĩlin wasa don mutãne suji ts õronsa
ba.
➢ Mai litt ãfin “Sãrimul Battar” yace: An bãni lãbãri , wani ma tsãfi yakan ajiye
duwãtsu guda biyu ya karanta zaurencensa sai kag a duw ãtsun sun f ãra karo da
jũna kai k ã ce rãguna ne guda biyu. Ya ƙãra da cewa, an b ã ni lãbãri wani yakan
ajiye kwan kãza, bayan ya karanta kalm õmin tsãfi, sai kaga kwan yana
mirgin ãwa. Yace duk wannan irin tsãfin matsãfa ne da suke yi a bainar jama’a
sabõda neman ku ɗi ko neman birgewa.
➢ wani l õkaci, ma tsãfin rufa -ido yakan s ãmo wata l ãya daga wurin wani b õka (da
yake ce masa malam) sannan ya r ãtaya ko ya saka a ƙarƙashin k ãyan sana’arsa
sai mutãne su rin ƙa ganin girma da kyawun ab ũbuwan da yake sayarwa.
➢ Akanyi tsãfin rufa ido a dabb õbi masu fa ɗã (su daina ganin mutum ko su ganshi
da wata siffar ta dabba) a je wurinsu a aikata wani abu.
➢ irin L ãya da ake ce mata “B ã duhu” ko l ãyar ɓata dukkanninsu tsãfi ne. da dai
sauransu.
Yadda ake ha ɗa kãyan tsãfin rufa ido:
Duk k ãyan tsãfi da ka sani ana ha ɗashi ne ta hanyar da take tã sãɓawa Allah da
Manzonsa (SAW) .
➢ Wani yana bamu lãbãri n abõkinsa: Wata rana suna cikin hũtawa sai wani daga
cikinsu ya tambayi all ũra (yana so yayi amfani da ita). Ma tsãfin yace all ũra ka ke
so? sai ya m ãri gõshinsa, sai ga all ũrai sun le ƙo ta hancinsa. ya z ãro guda ya
mĩƙawa ab õkin nasa.
Da muka yi m ãmãki ta irin yadda ake ha ɗa irin wannan dab ãrar (kamar yadda
suke cewa) sai (mai b ãmu lãbãri n) ya ce ai da kitsen mutum ake ha ɗa wannan
asĩrin. Na ƙara wani mãmãki nace to yanzu ta ina suke s ãmun kitsen mutum, yace
ai ba w ahala, da zãrar ka s ãmu likita (idan suna aikin operation ) sai ya yanka
maka. Inn ãlillãhi wa inn ã ilaihi r ãji’un.
➢ Wata r ãna wani Basakkwace yana b ãmu lãbãri yace: wani m ãlami yace zai ha ɗa
masa (l ãyar) b ãduhu, ya gama nemo dukkan ab ũbuwan da akace ya k ãwo saura
fatar ba ƙar muse (kyanwa) da fakara wacce za’a yanka ayi rubutu da jininta, anan
ne (Basakkwace n) yace gaskiya bai iya wannan a ha ƙura.
Yadda ake ɓãta tsãfin rufa -ido
Da farko bai halatta mutum yaje wurin wasannin da ake n ũna bajintar tsãfi ba. Idan aka
ce bãbu wanda zai kalli wasan matsãfa to sai dai in su kalli j ũnansu.
14
14
Tsãfi n rufa ido bai c ika sh ãfan wani mutum na gefe ya cutar dashi ba, amma g ãlibi a
wurin kallon w asan tsãfi aljannu sukan shiga jikin mutãne (akan s ãmo aljani a wurin).
Matsãfa n wurin wasa sukan yi wani tsãfi daga gefe su ɓãtawa (ma tsãfi) mai wasa tsãfi
a lõkacin da yake n ũna bajintar tsãfi. Mutum ya warware (ko ya ɓata) tsãfin ma tsãfi idan
yayi wani tsãfi shi ake kira: warware tsãfi da tsãfi (sukan ce “karya tambaya ”).
warware tsãfi da wani tsãfi na daban har ãmun ne.
Wasu matsãfa sukan ɓãta tsãfin mai w ãsa a lõkacin da suka k õma gefe suka le ƙo mai
wasan ta cikin karyeyyar ƙotar g ãtari wacce aka ts ãfa. Wannan har ãmun ne.
Halastacciyar hanya ta ɓãta sihirin ruf ã ido (hanyar hanashi f ãruwa) ita ce, hanyar
karanta Ãyatul Kursiyyu . Idan mutum ya kasance yana da alwala, yayi ta karanta Ãyatul
Kursiyyu, ko Bismillah, ko kiran Sallah ko wata addu’a irin ta nem an tsari daga she ɗãnu
alõkacin da mai tsãfi zai fãra tsãfi, to aljannu ba za su samu damar halastar wannan
wurin ba ballantana su t aimaka wa ma tsãfin tsãfinsa ya gud ãna.
Mai litt ãfin S ãrimul Battar yace: Anyi wani ma tsãfi a wata al ƙarya, sai yazo cikin
mutãne da Alƙur´ãni yayi abinda yayi sannan ya karanta addu’ar kiran aljanu sannan
yace: Alƙur´ãni ka matsa ɓangaren d ãma, sai aga ya tafi da sauri wajen dama. sannan
sai ya sake cewa d ãwo ɓangaren hagu, sai Alƙur´ãni ya she ƙa zuwa ɓangaren hagu.
Mutãne suna ta mãmãki ganin cewa basa tun ãnin mai tsãfi zai yi wasan tsãfi da
Alƙur´ãni , har sai da ya fara haifar da fitina. A lõkacin da na samu lãbãri , sai na tafi
wurin da yake wannan wasa ni da wani saurayi. Na isa wurin na ƙãlubalanceshi akan
yayi wasan na gani , mutãne suna ta mãmãki . A lõkacin da yake shirye shiryensa, nace
da wannan saurayi ya koma gefe (cikin ƴan kallo) yayi ta karanta Ãyatul kursiyyu. Ni
kuma na tsaya ta gabansa ina maimaita Ãyatul Kursiyy u a cikin z ũciyata.
A lõkacin da ma tsãfin ya gama add u’ar kiran aljannu, yace: Alƙur´ãni ka matsa
ɓangaren d ãma, shirũ. Ya sake karanta addu’a yace: Alƙur´ãni ka matsa ɓangaren hagu ,
shirũ. Daga nan ramin ƙaryar ma ƙaryaci ya ƙure.
Shawara anan, idan wani mai tallen m ãgani yazo muku zai aikata wani tsãfi kafin ya
tallata muku da m ãganunnuwa, ku tsaida shi ku masa nas ĩha ya tafi abinsa. Idan ya zama
tilas ( sabõda kar ya halakar da mutãne n ku) sai a ɓãta masa tsãfi ta halastacciyar hanya
sabõda hanyar masu laifi ta fito fili (a g ãne cewa ma ƙaryata ne). Allah Y a sa mu dace.
15
15
FASALI:
DALILI NA BIYU DAKE SA MUTÃNE YIN TSÃFI:
2.2 Sabõda su cutar da wani (ko abõkin gaba )
Kamar ya dda sũnan yake, mafi yawan tsãfi ayau ana yinsu ne sabõda a cutar da wani
abõkin ad ãwa sabõda wassu dalilai kamar haka:
1. Rãmukon gayya ( rãmukon zalunci)
2. Tare wani daga ɗaukar hukunci (A rufe masa b ãki)
3. Hassada
4. Kĩshin ganin wani ko wata a mazaunin da ake (ko a matsayi guda)
5. Samun nasara akan ab õkin takara .
6. Damfarar wa nda ake son zalunta.
7. Mallakar ab õkin hul ɗa ko ab õkin zama.
8. Killace wani a wuri guda.
9. Zãlunci
10. Nũna isa (bankama)
Wadannan sune wassu daga cikin ab ũbuwan da suke sa ayi ma wani mutum (mace ko
namiji) tsãfi da akafi kiransa da ASIRI. Ga bay ãninsu dalla -dalla ( amma a takaice):
1. Tsãfi don r ãma zãlunci. (R ãmukon gayya):
Sau da yawa w assu mutãne n da wani ya zalunta (ko ya zambace su), sukan zabi ASIRI
ya zama ha nyar da za su rãma zaluncin da akayi musu ba tare da k õwa ya sani ba. Wani
yakan yi asirin da kansa (idan y ã sani, ko an gwada masa yadda zai yi) wani kuma yakan
je wurin wani m alami (masanin tsãfi) ya nemi ayi masa aiki sabõda wãne da ya z ãlunce
shi ya s ãmu matsalar jinya iri kaza.
Daga yau ka g ãne, duk wanda zai je wurin wani malami ya bu ƙaci ayi
ma wani (ko wata) asiri, to da wannan mala min da ya yarda zai iya
yin asirin, da kai da kaje, duk kun himmatu wajen aikata tsãfi! Da
sannu zamu ga hanyar da ake bi ayi asiri.
Idan mutum ya zalunce ka, kaga ba za ka iya hakuri ba (duk da cewa shi y afi alheri) ,
kuma baka z ãɓi ka ha ɗashi da huk ũma ba, to musulunci ya b ãka damar ka r ãma cutar
da akayi maka dai -dai da ita (b ã ta hanyar tsãfi ba!). Allah (SWA) Ya ce:
16
16
Kuma idan kuka sãka wa uƙũba (kuka yi r ãmuko) to ku sãka wa uƙũba da misãlin
abin da aka yi muku uƙũbar da shi. Kuma idan kun yi haƙuri, lalle shĩ ne mafi
alheri ga mãsu haƙuri. (16:126)
Wanda yayi ha ƙuri (ya y ãfe) Allah (SWA) Zai b ãshi lãdan ha ƙuri. Idan ya kasance ba
yanda mutum zaiyi ya r ãma, kuma a gaskiya baya so ya y ãfe, to sai yayi add u’a (ba irin
ta tsãfi ba). Ya r õki Allah akan Allah Ya s ãka masa . Yã zo a cikin hadisi cewar: Addu’ ar
wanda aka z ãlunta bata da hijabi (Kai tsaye Allah (SWA) Zai kar ɓa).
Mutum y ã kasance mai gaggawa! Gaggawar son ganin y ã rama z ãluncinsa (ramukon
gayya y ãfi na gayya) shi yasa mutum yake z ãɓan hanyar asiri (hanyar tsãfi). Sabõda ya
san r õƙon Allah (SWA) ba a gaggawar aga sakamako! Ba a tilasta wa Allah (SWA)
akan ya aikata wani abu. Tsarki ya tabbata gareShi kuma Ya tsarkaka ga dukkan
abubuwan da masu shirka suke aikatawa suke cewa r õƙon Allah ne.
2. Tsãfi don tare wani daga ɗaukar hukunci .
Wanna n ya kasance k ĩshiyar wanda na yi bay ãni a sama. A wannan karon, wani mutum
ne zai zalunci mutãne (dũkiyarsu) sannan yaje wurin wani malami wai don a sh ãshantar
da magana r, kar a sake tambayarsa game da zaluncin da yayi.
Masu yin irin wannan tsãfi sun ha ɗa da masu cinye d ũkiyar mar ãyu (sune masu cin wuta
a cikinsu) da azz ãluman da basa son biyan b ãshi.
A lõkacin da masu b ãshin suka zama da yawa yadda ba za’a iya sihirce ɗaya bayan ɗaya
ba, sai azz ãlumin ya nemi ayi masa asirin a jikinsa ya zama cewa ba mai iya tambayarsa
biyan bashi. Ko ya zama cewa idan ka tafi nemansa don ya biy ãka bãshi, ba za ku ha ɗu
ba. Irin wannan shi ake cewa asirin shãshãtau ko rufa b ãki ko sãɓãni.
Bahaushe yakan yi mis ãli yace: ko rumfu mutum ya ri ƙa sai sun ha ɗu. To k õ shin ganyen
rumfun yana iya zama asirin s ãɓãni? Idan har mutum yayi ĩmãni cewa idan ya ri ƙe rumfu
duk mai nemansa ba zai iya s ãmunsa ba, ya s amu matsala a tauhidin sa! Rumfu ba zai
iya amf ãnar da mutum ba (don kawai ka saka a cikin aljihunka a matsayin l ãya). Idan
kã riƙe rumfun ne maimaikon addu’ar Allah Ya maka s ãɓani wannan ba musulunci
bane, kar a yaudareka. Allah (SWA) baya taimakawa ayi z ãlunci ( a yi sãɓani), Tsarki
ya tabbata g areShi, Allah (SWA) tõna asiri Y ake sai ƙ aryar ma ƙaryaci ta ƙare. Kuma
Yã hana a taimaki juna akan ɓarna -a yadda yake cewa:
…Kuma kada ku taimaki juna a kan zunubi da zãlunci, kuma ku bi Allah da
taƙawa. Lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne. (5:2)
17
17
Kuma ya zo a cikin hadisin ƙudsiy: Allah (SWA) Ya ce: Lalle ne Ni na haramtawa
Kaina z ãlunci , kuma na sanya shi ya zama har ãmun a tsakaninku, KADDA KUYI
ZÃLUNCI !
إِنه اّلِلهَ َلَ يَظْلِمُ النهاسَ شَي ْئًا وَلَكِنه النهاسَ أَن ْفُسَهُمْ يَظْلِمُونَ
Lalle ne All ah ba Ya zãluntar mutãne da kõme, amma mutãnen ne ke zãluntar
kansu. (10:44)
Sabõda haka, duk malamin da yace zai iya taimaka maka akan a mance da z ãluncin da
kayi, ba Allah (SWA) zai r õƙa ba ( Allah (SWA) Ya tsarkaka akan Ya taimaki
azzãlumi ), a’a malamin zai taimaka maka ne ta hanyar tsãfi. Idan Allah Ya so sai tsãfin
yayi t ãsiri sabõda buƙatarka t a “nãfi son na biya a Ranar L ãhira” ta tabbata , sannan
laifinka na tsãfi (sa ɓon Allah) za a rub ũta shi.
3. Tsãfi don Hassada
Mahassada sukan yi asiri a wanda su ke masa hassadar c ĩ gaba. Ga mis ãli, wata mai
hassada takanyi asiri a ab õkiyarta don sabõda kawai t ã ɗarãta farin jini. Wani l õkaci,
haka kawai (don hassada da gad ãrar tsãfi) ma tsãfi zai ga wata (ko wani) ya ce ta cika
girman kai sai ya mata as iri.
➢ Cikin w annan shekarar, n ã samu lãbãri n wata mai hassada ga k ĩshiyarta wacce
take cinikin kunu (da s ãmun r ĩba). Ita kafin tun ãnin tsãfi ya zo mata, ta lallaba ta
zuba maganin ɓera a cikin balangadar kunun ta gwauraya. Kwanan mutãne uku
da suka sha kunun ya ƙare, a n kai wassu Asibiti, ita kuma asirinta y ã tõnu.
4. Tsãfi don k ĩshin ganin wani ko wata a mazaunin da ake tare (ko a matsayi guda) .
Bambancin wannan da hassada shi ne; abõkin zama ya riga ya cimma wani matsayi da
ba yadda za ayi dashi. Mis ãlin kishiya, abo kiyar zamanta ba yadda za tayi ta rabu da ita,
a dalilin haka wassu sai su nemi taimakon malami (mai tsãfi) akan yayi ƙõƙarin da zaiyi
kĩshiyarta ta bar gidan. Yana daga mis ãlin wannan, t ãshin wani daga wurin san a’arsa.
➢ Wata r ãna muna hira ina mai maganar matsalar samun wurin kasuwanci a tsakiyar
wurin ciniki, sai wani ab õkina yace ai baka sani ba, r õƙon Allah ake sai mutum
ya tãshi ka samu sh ãgo. Hasbunall ãhu wa ni’imal wakil.
Wani lõkaci wassu sukan ture na gaba da su a matsayin wurin aiki ta hanyar tsãfi sabõda
su zama sh ũgabanni. Dukkan wa ɗannan baya yiwuwa a samu nasara akansu ayi ikir ãrin
cewa Allah aka r õƙa. Allah dai Shi Ya ƙaddara nasarar! kuma tabbas, Zai yi hukunci da
sãkamako a tsak ãnin mutãne .
18
18
5. Asiri (tsãfi) don s ãmun nasara akan ab õkin t ãkara .
Wannan ya sh ãfi dukkan abinda mutãne biyu (ko sama da haka) suke nema tare. Tãkarar
siyasa (har ta sh ũgabancin k ãsuwa ko wata ƙungiya), ko neman aure ko neman sarautar
gargãjiya. Abin sani kawai addu’ar da ya kamata ka yi idan z ã kayi takara ita ce:
Ka c e: "Yã Allah Mamallakin mulki, Kanã bayar da mulki ga wanda Kake so,
Kanã zãre mulki daga wanda Kake so, kuma Kanã buwãyar da wanda Kake so,
kuma Kanã ƙasƙantar da wanda Kake so, ga hannunKa alheri yake. Lalle ne Kai,
a kan kõwane abu, Mai ĩkon yi ne." (3:26)
قُلِ اللههُمه مَالِكَ الْمُلْكِ ت ُؤِْتِ الْمُلْكَ مَنْ تَشَاءُ وَت َنْزِعُ الْمُلْكَ ِمِهنْ تَشَاءُ وَتُعِزُّ مَنْ تَشَاءُ
وَتُذِلُّ مَنْ تَشَاءُ بِيَدِكَ اْلَْْيُْ إِنهكَ عَلَى كُل ِ شَيْءٍ قَدِير
ƙulil l ãhumma M ãlikal mulki, t ũtil mulka man T ashã’u wa T anzi’ ul mulka mimman
Tashã’u, wa Tu’ izzu man T ashã’u wa Tuzillu man Tash ã’u. Bi yadiKal khairu innaKa
ala kulli shai’in ƙadir.
Karanta wannan addu’a (mutum yana mai im ãni da abinda yake karantawa) jaddada
tauhidin rub ũbiyya ne, sabõda haka shai ɗan zai yi nesa da mai karanta wannan kuma in
Allah (SWA) Y ã yarda ko mutum bai yi nasarar s ãmun mulki ba, ba zai s ãmu d ãmuwa
ba sabõda yayi ĩmãni Allah ne Mai bayar da mulki ga wanda Ya so.
6. Tsãfi sabõda damfarar wadda ake son z ãlunta.
Sau da yawa wassu kan sã a musu tsãfi don su damfari wani mutum. Masu damfara
sukan zo da ku ɗin ganye, ko wani abu na daban, ƙarshe su z ãlunci mutãne .
Masu neman b ãshin ku ɗi, ko wani abu a wajen wani t ãjiri, (wassu) sukan s ã ayi musu
taimakon asiri da zai sa bu ƙatarsu ta biya ba tare da jinkiri ba.
7. Asiri don mallakar ab õkin hul ɗa ko ab õkin zama.
Sau da yawa masu raunin ĩmãni sukan ce d õle ne mutum ya t ãshi ya tsaya sabõda kar a
rabãshi da maigidansa. A dalilin haka sai kaga mutãne suna neman ayi musu wani
taimako da zai sa ubang idansu ya s õ su matu ƙa.
Da yawan m ãtã sukan s õ su sãmu asirin mallake miji sabõda ya kasance mai yin ɗã’a
ga dukkan abinda suka b ãda shawara.
8. Asiri don killace wani a wuri guda.
A wannan karon, wassu maza (ma’aurata) kan yi asirin (tsãfi) a m ãtãyensu da sũna kafi.
Matar da aka kafeta za ta zama kamar baiwa marar ƴanci, ai ta cutar da ita yadda ake
so, zai zama b ã ta son fita zuwa s ãda zumunci ko ka ɗan, da sauransu.
19
19
Asirin ( tsãfin) Kafi bai tsaya anan ba, akan binne k ãyan tsãfi a turken dabb õbi sabõda a
hanasu barin wurin.
➢ Wata r ãna mu na hira da man õmi na, ina jajanta masa game da yawan s ãtar sh ãnu,
sai yace shi sh ãnunsa a waje yake ɗaure su, kuma idan har kaga ɓarãwo ya samu
damar tafiya da bi jiminsa to ka tabbata ya t õne turken ya tafi dashi. Amma
matuka r zai bar turken, to ko a m õta aka saka bijimin aka tafi dashi zai d ãwo!
Kasan dai wannan tsãfi ne! Akwai sauran bay ãni.
➢ Har yanzu akwai gid ãje da ake r ãtaye ƙahon rãgo ɗaure da wata lãya a bak in
mafitar gidan, na gan ĩ a wani gida a can Bulunkutu Abuja. A nce irin wannan
asĩrin kafin gida ne. A lõkacin da ɓarãwo ya zo fita da kayan s ãta, rãgo zai hanashi
fita daga gidan , ko ya ma ƙale a b ãkin ƙõfa sai an tarar dashi an sau ƙe masa kayan.
9. Asiri don Zãlunci
Haka kawai don z ãlunci, sai mutum yayi asiri (na tsãf i) ya cutar da wanda suka samu
sãɓani ka ɗan na c ãcar b ãki. Wassu kanyi asirin (tsãfi) don su samu nasarar z ãluntar
mutãne su sãce musu dukiya. (kamar masu s ãne (yankan aljĩhu) )
10. Asiri don n ũna isa (bankama)
Akwai wa ɗanda sukan yi asirin tsãfi a kansu don su kasance masu kwarjini, ana
girmamasu suyi ta bankamarsu babu mai iya tanka musu. Ance wassu har launi suke
canzawa –yau ka gansu far ãre, idan ransu ya ɓaci su rikiɗe baƙaƙe masu j ãjãyen
idãnuwa. Wassu har wuta ke fita daga bakunansu idan ransu ya baci, ƙananan sune masu
tãda ƙudan zuma su baza t ãro. Ran maza ya ɓaci!
2.2.1 Yadda ake gudãnar da tsãfi (asiri) a cutar da wani.
Dukkan dalilai da nayi bayani n suna sa ayi asiri a wani mutum, ana gud ãnar da asirin
ne ta hanyar Aljanu. Aljannu ke shiga jikkunan mutãne su han asu gud ãnar da abubuwan
da suka yi nufi. Akwai ƙãrin bayani a sashe na gaba.
Yadda ake ɓãta asirin cũtar da wani.
1. Hanya r Ruƙiyya:
Ruƙiyya hanya ce da ake karanta ãyõyin Alƙur´ãni a marar l ãfiya (g ãlibi wanda
aljani ya shiga jikinsa) don yana sauraro. Idan Aljani yana jikin wanda ake masa
ruƙiyya, zai yi magana ta bãkin marar lafiya, sai a tattauna da shi sannan a nemi
ya fita daga jikin marar l ãfiya kuma kar ya ƙara d ãwõwa. Ruƙiyya da wani kar ãtu
na dabam bai halatta ba. Akwai ƙãrin bay ãni.
20
20
GANYEN MAGARYA
2. Hanyar Azkar :
Azkar shine karanta addu’ õi (zikiri ko l ãzimi) waɗanda suka inganta daga
Manzon Allah (SAW). Sun ha ɗa da irin Azkar da ake karantawa a lõkacin da za’a
kwanta barci , da wanda ake karantawa idan za’a shiga wurin biyan bu ƙata (Toilet)
da sauransu .
3. Hanyar saur ãron karatun Alƙur´ãni.
Yawan sauraron karatun Alƙur´ãni mai girma yana taimak ãwa wajen l ãlãcewar
sihiri da ke jikin mutum. Idan har Aljani ya kasance a jikin mutum, karatun
Alƙur´ãni zai zama masa d ãmuwa da matsala sabõda haka shi da kansa sai ya fita
ya nisanci mutum.
4. Hanyar cin dabinon Ajwa :
Ya zõ a cikin Hadisi cewa wanda ya ci
dabinon Ajwa ɗan Madina guda bakwai
da safe (idan ya w ãyi gari), tsãfi ba zai
kãma shi ba a wannan r ãnar, In sha Allah.
Tsãfin mai sh ãshãtau ba zai k ãma mutum
ba a wannan ranar, da sauransu.
5. Hanyar sh ã da wanka da ruwan ga nyen magarya :
Za a samu ganyen magarya tsanwa ( green ) guda bakwai (7) a dandaƙa su a
tsakãnin duwãtsu biyu (a aza akan dũtse a daka da dũtse). Sannan sai a zuba ruwa
su wanke su cikin kwãn o. Sai a karanta Ãyatul Kursiyyu , da Falaƙi da Nãsi, da
ayõyin da sukayi maganar sihiri na cikin sũrõrin La’arãfi da Yũnus da Ɗãhã,
(ãyõyin da na shirya lãbãrin Annabi M
Duka a karanta a cikin ruwan . Sannan
marar lãfiyar ya kur ɓi ruwan sa u uku
yayi wanka da sauran ruwan.
Ance wannan yana mãganin nau’i kan
gõma kuma yana da tãsĩri ƙwarai ga
aka katangeshi ga iyãlinsa.
Allah (SWA) Yasa a dãce.
21
21
FASALI:
DALILI NA UKU DAKE SA MUTÃNE YIN TSÃFI:
2.3 N eman s ãmun r ĩba ko cin na sara akan wani kasuwanci.
Kasuwanci ya ha ɗa da duk wani abu da mutum yake s ã dũkiyarsa sabõda ya samu r ĩba
anan d ũniya ko a l ãhira (ko duka). Anan , neman aure yana daga cikin kasuwancin da
muke batu.
Akwai daga yan kasuwa da suke neman taimako da za i jãwo musu ab õkan ciniki
(customers ), sai a ba su wassu ƙulle-ƙulle su binne ko su rãtaya a wani wuri na
kasuwancinsu.
Direb õbin m õtõci, na f ãsinja ko na ɗaukan k ãya (wani lõkaci har na gida), sukan nemi
asĩrai daban -daban wanda zai taimaka musu akan hany a. Daga cikin as ĩran da direb õbi
suke nema akwai as ĩrin s ãɓãni tsakaninsu da ƴan-fashi, akwai as ĩrin bindiga, akwai
asĩrin kaucewa hatsari, sh ãshãtau, ruf ã ido da sauransu.
Masu san ã’ar w ãsanni irin na dambe, sh ãɗi, kõkawa kai harma da ƙwallon ƙafa
(footb all), sukan nemi as ĩrai daban -daban sabõda ya taimaka musu wajen s ãmun r ĩba ko
cutar da ab õkan wasa.
Wajen neman aure, wassu mutãne kan nemi taimako sai a b ãsu na tsãfi su mallake
zũciyar wacce z ã su aura , ko su mallake zũciyar wani da suke ganin zai kawo musu
matsala wajen samun nasarar auran yarinya r, ko uwar yãrinyar!
Wani lõkacin , abõkin tãkara da aka k ãyar (wajen neman aure) shi yake ganin ba a kyauta
masa ba, sai yasha alw ãshin ɗaukar mat ãkin haddasa matsala (ko hana auren) sabõda ya
rãma z ãluncin da yake ganin anyi masa. Wannan (tsãfi) ba shi ne hanyar da ya dace na
rãma z ãlunci ba.
➢ Anyi wani lõkaci , daga garin Azare aka tafi Maiduguri ɗaurin aure, a wurin ɗaurin
aure da aka t ãru, sai aka fito aka sanar da mutãne cewar Amarya … Allah (SWA)
Ya kar ɓi kwãnanta. Mutãne sunyi mãmãki n mutuwar l ãfiyayyar amarya a lõkacin
ɗaurin aure, kuma sun danganta sababin mutuwar da tsãfin wani daga cikin
manema n amaryar da ba’a kyauta masa ba. Na k ãwo wannan lãbãri ne sabõda
masu niyy ar ɗaukan mat ãkai idan wani mai ku ɗi ya ƙwãce musu mas õyiya, suji
tsõron Allah . Amma a kiy ãye m ũnãnan zato da ba’a tabbatar da su ba. Allah
(SWA) dai Shi ne Ya ƙaddara mutuwar amarya , kuma a wannan lõkacin . Allah
(SWA) muke r õƙo Ya y ãfe mana ab ũbuwan da r ãyukanmu suke riya mana.
22
22
➢ Wassu sun b ãda lãbãri n cewa an ã yin Y ãsin (As ĩri da S ũratu Y ã sĩn) a wani abu n
sayarwa don a damfari mai saya ya saya da ts ãda. Da zarar tsautsayi ya sa mutum
ya taya (ya f ãra ciniki) to zai kãmu da ciwon z ũciyar da b ã zai barshi ya h ũta ba
sai ya sayi wannan abun k õmin tsãdarsa.
Duk irin dabãru na m ãgani da za’a gwada wa mai sana’a , ta jũri gwauraya wa a cikin
abin sayarwa da niyyar k ãma masaya, wannan tsãfi ne. M ãtã masu sakawa (a a bincin)
mazajensu m ãganin mallaka ko na wani abu daban, wannan tsãfi ne.
Kasuwanci irin na wãsã da dabb õbi masu fa ɗa (ko kisa) g ãlibi yana tattare da tsãfi. Masu
wãsa da maciji, kadõ, kũra da sauran n ãmun daji (sau dayawa) sukan ha ɗa da tsãfi
wajen k ãmo dabb õbin, sarraf ãsu da kuma a lõkacin wasa .
2.3.1 Yadda ake gudãnar da asirin sãmun nasa rar kãsuwanci.
Duk da cewa lãbãri muke ji, ance wassu masu w ãsa irin na dambe, sukan na ɗe hannunsu
da lãya a ciki wacce zata taimaka musu su g ĩgĩtar da ab õkin dambe a lõkacin da suka
bugeshi. Masu sh ãɗi kuma , ance sukan yi as ĩrin ne a jikin b ũlãlarsu. Idan suka zabga
wa mutum wannan b ũlãla mai asirin, mutum yana iya mutuwa idan d ũkan y ã zo (dai-
dai) da ƙarar kw ãna.
Kamar direb õbi kuma , wani lõkacin dãgã ce (g ũrun damtse) za su mur ɗa idan suna son
aikata wata ts ãtubar (kamar idan suna son sh ãshãtau ya fara aiki). Mafi yawansu sukan
yi amfani da bante (ko rigar singlet ) mai ɗauke da lãyu n rubũtun dukkan Alƙur´ãni da
kuma sauran f ãtun dabb õbi da sauransu.
Mai asirin ri ƙe ɓarãyi, yakan kira wassu sun ãye (na aljannu) a lõkacin da lãya rsa take
jikinsa, sannan sa i yace kãmasu ƙasa! Sai ɓarãyi su kafe a wuri guda.
Dukkan asirai da ake ya zama an cusa ma wani mutum s õyayya ko kiyayyar wani abu,
akan gud ãnar dashi ne ta hanyar wakilta Aljani. Wani lõkacin Aljanin zai zauna a jikin
wanda akayi masa asirin yai ta azabt ar dashi da rashin kwanciyar hankali, wani lõkaci
kuma Aljanin kan zo ya tafi ( lõkaci lõkaci ).
2.3.2 Yadda ake ha ɗa asirin s ãmun r ĩbar k ãsuwanci:
Asiri irin wanda ake ba direb õbi da ƴan kãsuwa, g ãlibinsu lãy ũ ne ko g ũrũ waɗanda aka
haɗãsu ta hany õyi irin na tsãfi. Wani lõkaci akan rubuta lãyun ( ãyar Alƙur´ãni mai
girma) da jinin tsuntsu a rufa da wata f ãta a binne a wurin k ãsuwanci sabõda mutãne
suna zuwa (sayen k ãyan) da sauri kamar tsunts ãye.
Ma’ab õta wasanni irin na dambe da sh ãɗi kuwa, ha ɗin as ĩrinsu yakan kai har su binne
wassu k ãyan fa ɗansu a cikin kabari na tsawon wani lõkaci .
Kamar bante kuwa, bay ãnin hanyar ha ɗãshi tana da tsawo. Bay ãni yana gaba.
23
23
2.3.3 Yadda ake ɓãta asirin samun nasarar k ãsuwanci .
Kamar asirin da ya sh ãfi sõyayyar d õle (ko ƙiyayya) da dukkan asirin da ake ganin ana
gudãnar dashi ne ta hanyar wakilta Aljani, ana ɓãtashi ta hanyar ru ƙiyya da sauran
hany õyi da nayi bayani a fasalin da ya gab ãta wajen yadda ake ɓãta asirin cutar da wani.
Neman ts ãri daga m asu irin wannan asirai kuw a, mutum zai ku ɓuta da yardar Allah
(SWA) idan yana bin ũmarnin Manzon Allah (SAW) kamar karanta addu’ar shiga
kasuwa , yin sadaka da sauransu.
Manzon Allah (SAW) yace: Wanda ya fa ɗã, a cikin kasuwa (ko in zai shiga a wani
hadisin) :
Lã ilãha illallã hu wahdahũ lã -sharĩka lah, lahul mulku wa lahul hamdu, bi
Yadidihil khairu Yuhyĩ wa Yumĩtu wa Huwa ala kulli shai’in ƙadĩr.
Allah (SWA) Zai rubũta masa kyãwawa dubu -dubu kuma Ya gõge masa mũnãnã dubu -
dubu. Kuma Ya gina masa gida a cikin Aljannah. (Tirmidh i ya rawaito)
هَذِهِِ إِن ِ :ف َقَالَِ السُّوقِِ فِِ وهم صحابته بعض أتى -وَسَل مَِ عَلَيْهِِ اّلل هِ صَل ى- الن بِ ِ إن
النسائي رواه(ِ”ِبِلص دَقَةِِ فَشهوبهوهَا وَالْكَذِبهِ الل غْوهِ ُيهَالِطههَا السُّوقَِ
Manzon Allah (SAW) yace: Ita wannan kãsuwa wargi da ƙarerayi suna cãku ɗa da
ita. Ku gaurayata (kuna bĩbiyanta) da (yin) sadaka.
Sauran bayani a game da kãsuwa (cikin harshen lãrabci) zaka sãmeshi a cikin hu ɗuba
idan ka bibiyi wann an akalar !
24
24
FASALI:
DALILI NA HUDU DAKE SA MUTÃNE YIN TSÃFI:
2.4 N eman waraka daga wata jinya .
A dalilin wata jinya, Mũsa mman wacce ta sh ãfi bugun aljani, mutãne sukan f ãɗa cikin
aikata tsãfi cikin sani ko rashin sani. Warware tsãfi da wani tsãfi na daba n har ãmun ne.
Masu sana’ar ɗõri (gyaran karaya), wasunsu kan yi amfani da m ãganunnuwa da aka
haɗa ta hanyar tsãfi. Kwararrun masu ɗõri sukan iya ɗõra mutum daga gidajensu ba tare
da sun taba jikin mutum ba . Wannan kuwa ba zai ta ɓa yiwuwa in ba ta hanyar wa kiltar
da Aljanu ba. Zaka fahimci cewa tsãfi ne a lõkacin da aka tambayeka sunan wanda ya
karye da sunan mahaifiyarsa ko ranar haihuwarsa. Bayani yana zuwa nan gaba .
Duk wanda ya yarda aka ɗõra waninsa daga wani wuri ba tare da an ta ɓa jikinsa ba, ya
tabbatar ya biya ku ɗi an ɗõra ɗan-uwansa ta haryar tsãfi.
➢ Akwai ma ɗõri da ya sharara a shekarun b ãya, a garin Azare, a koda yaushe yazo
dũba marar lafiyar da ya ɗõra za kaga ya sar ƙafa y ãtsunsa y ã dunƙule, yana
karanta ab ũbuwan da b ãmã ji yana t õfawa a kan y ãtsun. Irin wannan ru ƙiyya
harãmun ce a musulunci.
Wanzamai masu k ãciyar saka wando, mafi yawansu suna ha ɗa maganin kasa -kaifin ne
ta hanyar tsãfi, Sannan kuma su ƙara da wassu dab ãrun na tsãfi.
2.4.1 Yadda ake gudãnar da likitanci ta hanyar tsãfi.
A lõkaci n da mai m ãgani yayi nufin ɗõra mai karaya daga gida, zai tambayi adireshin
majinyaci sannan ya t ũra aljani domin yaje ya ɗõrashi. Cikin dare, za’a ji majinyacin
yana ta ihu kamar zai halaka, a lõkacin ne aljani yake gudanar da ɗõrin majinyacin.
Wani lõkac in ma, mai-ɗõri zai bada lõkacin da za’a rirriƙe majinyacin .
Mai m ãgani yana iya ũmartar aljani ya shiga jikin mutum ya cire wata cuta da take
damunsa a cikin ciki. Aljani kan iya cire wani kulle -kulle da aka dasa a jikin mutum ko
aka binne a cikin gida, a mma fa ka sani! Aljannu basu san gaibu ba , kuma ma ƙaryata
ne!
➢ Na ta ɓa jin lãbãri , anyi ma wata sihirut tafriƙ sabõda a rabata da saurayin da zai
aureta. Aljanin da aka wakilta da wannan aiki shi ya shiga jikin saurayin ya sanya
HIV na ƙarya, sannan ya canz a tun ãnin iy ãyen yarinyar. Karshen lãbãri , ta hanyar
ruƙiyya aljanin ya bayyana wannan, kuma ya cire HIVn. An gwad a saurayin daga
baya babu HIV kuma anyi auren a lõkacin da Allah (SWA) ya ƙaddara.
25
25
2.4.2 Yanda ake ha ɗa kayan asirin likitanci (na tsãfi) .
Duk hanyar da ake bi a ha ɗa gwuiwa da aljannu su ne hanyar asirai na m ãgance
cututtuka ta hanyar tsãfi. Mai m ãgani yakan yi tur ãre (hay ãki) kafin yazo duba marar
lafiya. Wani lõkacin yakan b ãyar da tur ãren ne a rin ƙa yi ma marar lafiyan. Akwai
turãren iska (w ato tur ãren korar aljannu) akwai tur ãren korar maciji daga wuri da
sauransu. Turaren da aka hadashi ta hanyar tsãfi ko yinsa yake haifar da wani dabo,
wannan tsãfi ne. Muna ɗauke da sauran bayani.
Bãbu war aka a cikin m ãganin da aka ha ɗãshi da najasa (a lõkacin haɗashi ko a lõkacin
da za’a sh ãfa). Har ãmun ne a r ãtayawa y ãro fãtar kũra don tayi masa m ãganin fits ãrin
kwance.
➢ Duk da cewa ban san m ãganin da za’a ha ɗa ba, ina cikin manya ana zancen
ƙãrewar J ãkuna (Jakkai) a cikin al ƙaryu, sai wani masarauci yace: Ai kwanannan
da muna neman kãshin J ãki sai da aka tafi can wajen …… aka samo.
Duk asirin da aka ha ɗa da k ãshin j ãki tsãfi ne! ka biyo ni sannu a hankali.
2.4.4 Yadda ake ɓãta sihirin likitancin tsãfi.
Sau da yawa, aljani kan ɓãta aikin da aka wakilt ãshi, ko ya d ãwo yaci gaba da zama a
jikin majinyaci sai ya haifar da wani ciwon na daban. Irin wannan ana ɓãta shi ne ta
hany õyin Ru ƙiyya, Azkar da sauransu.
Abinda yafi d ãcewa, mutãne su rin ƙa lũra da irin hany õyin likitancin masu m ãganin
gargãjiya da m ãganun nuwa da ake ɗõrasu a kayi –hany õyin shafasu da yinsu da
sauransu.
Jinya jarrab ãwa ce, waraka kuma tana wurin Allah.
Allah (SWA) yana cewa:
Kuma lalle ne, Muna jarrabar ku da wani abu daga tsõro da yunwa da naƙasa
daga dũkiya da rãyuka da ´ya´yan itãce. Kuma ka yi bishãra ga mãsu haƙuri.
Waɗanda suke idan wata masĩfa ta sãme su, sai su ce: " Innã lillãhi wa innã ilaihi
rãji’un . (Lalle ne mũ ga Allah muke, kuma lalle ne mũ, zuwa gare Shi, muke
kõmãwa. )" (2:155)
Sabõda haka, majinyaci ya yawaita karanta “ Innã lillãhi wa inn ã ilaihi r ãji’un” shi ne
abinda yafi d ãcewa. Kuma sai Allah (SWA) Ya b ãshi sau ƙi a cikin gajeren lõkaci . Allah
Yasa mu d ãce.
26
26
FASALI:
DALILI NA BIYAR DAKE SA MUTÃNE YIN TSÃFI:
2.5 Neman ku ɗi (sana’ar b õkanci)
Masana la ƙani (kamar yadd a ake faɗa) sukan b ãyar da t aimakon asirai (na tsãfi) a b ãsu
abin sadaka. Kafin ka samu mai laƙani ya baka har gindinsa, ba ƙaramar bauta za kayi
masa ba ! Sai ka bauta masa (kamar yadda suke fada), ka masa biyayya k ãfin ya gaya
maka it ãtuwa da siddabaru da ake yi wani asiri ya gudana. Ko ƴaƴan masanin laƙani,
idan ba suyi biyayya ba, haka mai laƙani yake mutuwa da laƙaninsa (ba tare da ya bar
gãdon la ƙaninba).
Masanin laƙanai wanda ya d õgara da bayar da taimako (na m ãganin warakar wata c ũta
ko sã’a) a b ãshi ku ɗi ko kãji (abin sadaka), yakan j ũye ya zama b õka (mai d ũba) ko ɗan-
bõri. Idan har yana bu ƙatar zama bõka mai gani har hanji , to wannan sai ya ha ɗa da
maita.
Ilimin bõkanci, yana da yawan gaske kamar yadda za mu saurari bayani a babi bõkanci,
in Allah (SWA) Ya yarda.
2.5.1 Hukuncin matsãfi a shari’ar musulunci.
Matsãfi bõka ko waninsa, hukuncin laifinsa, a shari’ar musulunci shi ne kisa! Dukkan
malamai sun tafi akan haka banda Imãmu Shãfi’i, shi kan yace sai dai idan matsãfin ya
kashe wani ta hanyar tsãfi n asa.
Imãmu Mãlik (R) yace bã za a kashe matsãfi Ahlul -kitabi ba har sai idan ya kashe (wani)
da tsãfinsa. Amma musulmi idan ya yi tsãfi da kansa da maganganu da suke kãfirci ne,
ba sassauci, sai a kashe shi.
Idan matsãfi ya tũba ya daina tsãfi tũba na gaskiya! Allah (SWA) Zai kar ɓi tũbarsa kõ
da ya ta ɓa kashe wani da tsãfinsa, sai ya kasance ya fida daga cikin mushirikai (matsãfa)
waɗanda zã su tabbata a wuta. Allah (SWA) Ya tsare mu .
27
27
FASALI:
2.6 Game d a Ruƙiyya (Tõfi) .
الرقية: العوذة أو التعويذة الىت تقرأ على صاحب اْلفة مثل اْلمى أو الصرع أو اْلسد
طلبا لشفائه
Ruƙiyya ta kasance dukkan kar ãtu na neman tsari da ake karant ãwa a majinyaci sabõda
ya sãmu sauƙi. Irin wannan ruƙiyya, haus ãwa sunfi ƙiranta da s ũna “Tõfi”. Sau dayawa
akan kai yãro mai yawan kũka ( ɗan-yãye da aka cire daga nõnõ) wajen tõfi.
Ya kasance tun lõkacin j ãhiliyya ana yin ruƙiyya a majinyaci. Ya zõ a cikin littafi n
Sahihul Muslim daga Auf bn Mãlik yace: Mun kasance, tun lõkacin jãhiliyya, muna yin
ruƙiyya. Sai muka ce: Ya Rasũlullãhi me ka gani game da ita? Sai yace: ku bijirõmin
da ruƙiyyarku, Bãbu laifi ga ruƙiyyar da a cikinta bãbu (laffuzan) shirka.
Kuma daga Jãbir (R.A) yace: Manzon Allah (SAW) ya hana ruƙiyya sai Ãli Amru bn
Hazmi su ka zõ wajen Manzo (SAW) suka ce: Yã Ras ũlullãh! M ũ a wurinmu muna da
wata ruƙiyyar (tõfin) harbin kun ãma kuma gashi ka hana yin ruƙiyya! Yace sai muka
karanta masa ita, sai Manzon Allah (SAW) yace: Ban ga (wani) laifi ba (tare da ita),
daga cikinku wanda z ai iya taimakawa ɗan-uwansa to ya ta aikata (hakan).
Kunãma t ã harbi shũgaban wassu mutãne, sai suka tambayi Sahabba n da suka
bãƙuncesu ko da wanda ya iya ruƙiyya? Sahabbai suka ce akwai… daga cikin sahabban
ɗaya yayi masa tõfi da “ Fatiha ” har sai da ya den a jin zõgi kamar kunãma bata harbe shi
ba. Aka bãsu lãdan tumãki suka tafi. Da suka lãbãrta wa Manzon Allah (SWA) yadda
akayi sai yace “Me ya sanar daku cewa (ita Fatiha) tõfi (na kunãma) ne!!! ku sanya
ni cikin rabonku”
Mutum zai iya ma kansa tõfi, yayi t õfin Ãyatul kursiyyu da Falaƙi da Nãsi ya shãfe
jikinsa idan zai kwanta. Mãta za ta iya yiwa mijinta da ƴaƴanta tõfi! Nana Aisha (R.A)
tana yin (tõfin) ruƙiyya a Manzo (SAW). Kuma Annabi (SAW) yana nemawa Hasan
da Husaini (R.A) tsari daga Shai ɗanu kamar ya dda zamu gani a gaba.
Shara ɗin ruƙiyya, dõle ya kasance da harshen lãrafci za a karanta ta, sannan kuma ya
kasance cikinta ãyoyin Alƙur´ãni ne, ko sũnayen Allah (SWA) da siffõfinSa sanannu
da, ƙarshe a ƙudurta Allah (SWA) Shi ne TABBAS Zai bayar da sauƙi.
Ruƙiyya irin wacce in an karanta aljani yake bayãni ta bãkin mara lafiya sananniya ce.
Akwai abubuwan da ya dace a sani da wa ɗanda za a kiyãye kafin a fara gudãnar da
irin wannan ruƙiyar.
28
28
BÃBI NA UKU
BÕKANCI
Bõkanci sana’a ce da mai il imin tsã fi (wani lõ kaci haɗi da bõ ri) kan yi da niyyar shiryar
da mutã ne zuwa ga sãmun r ĩba da tunku ɗe musu cũ ta (Ya kawar musu abũbũ wan da
basa so) sabõda su bashi abin sadaka .
Abin sadaka ya ha ɗa da ku ɗi, kãji, dabbõbi da sutura. Mai sana’ar bõkanci shi ake kira
bõka . Bõkanc i da dũba suna tafiya ne hannu da hannu idan ba’a ce abu ɗaya bane.
Misalin dũba shine wani m ãlami (da sunan istihãra) ya gaya maka cewa tafiyar da za
kayi akwai ha ɗari a cikinta, don haka ka bari sai wani lõkaci.
Bõkanci kuma, bõka zai gaya maka hatsarin da zai sameka sannan ya ce zai maka
maganinsa (ya kawar maka dashi) ta hanyar m ãgani ( asĩri).
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba, Da abin da bã ku iya gani.
Lalle ne, shi (Alƙur´ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Ka ɗan ƙwarai zã ku gaskata.
“Kuma bã maganar bõka ba ne. ”
Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa. Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
(69:38 -43)
Alƙur´ani ba maganar bõka bane (bai yi kama da s ũrutan bõka ba) , kuma ba ’a bõkanci
dashi! Ba’a istihã ra da Alƙur´ ãni a hango abun da zai f ãru gobe ! Allah (SWA) Yace da
Annabi (SAW):
Ka ce: "Bã ni mallaka wa raina wani amfãni, kuma haka ban tunku ɗe wata cũta,
fãce abin da Allah Ya so. Kuma dã na kasance inã sanin gaibi, dã lal le ne, nã
yawaita daga alheri kuma cũta bã zã ta shãfe ni ba, nĩ ban zama ba face mai
garga ɗi, kuma mai bãyar da bishãra ga mutãne wa ɗanda suke yin ĩmãni." (7:188)
Annabi (SAW) bai zama ba face mai garga ɗi da bãyar da bishãra , bai yi bõkanci ba, bai
yi um arni da yin bõkanci ba. Amma yã ce:
Duk wanda yaj e wurin bõka ko mai dũba sai ya gaskata shi, to haƙiƙa ya kãfirta
da abin da Allah (SWA) Ya sauƙar wa Annabi Muhammadu (SAW).
Kuma yã ce: wanda yaje wurin bõka ko mai dũba, sai ya tambayeshi wani abu
kuma ya gaskata (bõkan) , to ba za’a kar ɓi sallarsa ba har (tsawon) dare arba’in.
29
29
FASALI :
3.1 Ilimin bõkanci da dũba.
Ilimin bõkanci da dũba yana da f ãɗin gaske, kuma ya rarrabu kashi -kashi. Ilimin ya
sãmo tũshe ne daga ingantaccen tsarkakenken ilmi, amma sai wassu su ke amfani dashi
ta hanya mummuna wacce aka ha ɗata da ƙarerayi.
A wannan zãmani da muke ciki, ƙarni na ashirin da ɗaya milãdiyya, mutãne (musulmai)
da yawa suna ƙara kar ɓan halascin bõkanci da dũba cikin rashin sani. Wannan yasa na
himmatu da rubu ta wannan ƙaramin litt ãfi domin na fayyace, na fito da bayanin ni’imar
Ubangiji a garemu wacce ake amfani da ita tun farkon duniya. Wannan ni’ima, har yau
itace kan gaba a fasahar duniya, kuma daga cikin iliminta ne wassu bõkaye suka canza
ni’imar Ubangiji z uwa bõkanci. وَمَنْ ي ُبَد ِلْ نِعْمَةَ اّلِلهِ مِنْ ب َعْدِ مَا جَاءَتْهُ فَإِنه اّلِلهَ شَدِيدُ الْعِقَابِ
وَكَذَلِكَ ن ُفَص ِلُ اْلَْيَتِ وَلِتَسْتَبِنيَ سَبِيلُ الْمُجْرِمِنيَ
Ina gõdewa Allah (SWA) da Ya zãbeni Ya bani damar fayyace bayanai uku da bãbu
wani (cikin mutãne n karshe n duniya ) da ya samu damar fayyacesu a rubuce, kamar
yadda na rubuta. Tabbas na fahimci wannan shine fassarar mafarkin rijiyõyin madara
uku da na sha daga garesu.
1. Littafin bayanin sauƙar da Alƙur´ãni mai girma da harrufa bakwai. (Da harshen
Larabci da Turanci )
2. Littafin Yaumul ƙiyama (da harshen Hausa , Turanci da Larabci )
3. Wannan littafi (da harshen Hausa , Turanci , da Larabi ) In sha Allahu.
Allah (SWA) Ya ƙ ãra mana il imi, Ya bamu damar aiki dashi. Allah (SWA) Ya gãfarta
mana kur ãkuren mu (tuntu ɓen alƙalami da sauransu) , Ãmin.
Kamar yadda na bada misãlin aikin bõka da na malamin dũba, a gaskiyar magana (idan
ba bõkanci ta haryar bõri ba) bõka nci baya cika sai da ilimin dũba, haka kuma mai dũba
ba zai iya haƙura a iya dũba ba (duk da cewa itama ba kyau) sai ya faɗa cikin bõkanci.
3.1.1 ilimin d ũba.
Idan malami mai dũba bai shahara sosai ba, mutãne kan ɗauke shi a malamin istih ãra.
A gaskiyar magana , bãbu wani malami da zai iya yi maka istihara ya sanar da kai ãƙibar
abinda kasa gaba (ya sanar da kai alherinsa ko sharrinsa) f ãce ta hanyar dũba!
Istihãrar da bã dũba ba, mutum shi yake wa kansa da kansa. Karanta wa ake kamar yadda
Annabi (SAW) ya k oyar da Sahabbai (Allah Ya yarda da su). Istihara (ta sunnah) ta
kasance kamar haka:
30
30
اللهمه إِّن ِ أَسْتَخِْيُكَ بِعِلمِكَ وَأَسْت َقْدِرُكَ بِقُدْرَتِكَ، وَأَسْأَلُكَ مِنْ فَضْلِكَ العَظِيمِ، فَإِنهكَ
ت َقْدِرُ وََلَ أَقْدِرُ وَت َعْلَمُ وََلَ أَعْلَمُ وَ أَنْتَ عََلهمُ الغُيُوبِ، اللهمه إِنْ كُنْتَ ت َعْلَمُ أَنه هَذَا اْلَمْرَ
خَْيْ ِلِ ِفِ دِيِنِ وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي أَوْ قَالَ عَاجِلِ أَمْرِي وَآجِلِهِ فَاقْدُرْهُ ِل وَيَس ِرْهُ ِل
ُثُه َبَرِكْ ِل فِيهِ، وَإِنْ كُنْتَ ت َعْلَمُ أَنه هَذَا اْلَمْرَ شَرٌّ ِل ِف ديِن وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي أَوْ
قَالَ ِف عَاجِلِ أمري وَآجِلِهِ، فَاصْرِفْهُ عَِن ِ وَاصْرِفِْنِ عَنْهُ، وَاقْدُرْ ِلِ اْلَْيَْ حَيْثُ كَانَ ُثُه
أَرْضِِنِ، وَيُسَم ِي حَاجَتَهُ
Allahumma inni as’ta-khĩ-ruKa bi ilmiKa wa as’taƙ-diruKa bi ƙud -ra-tiKa wa as’alu Ka
min fa ḍ-liKal azĩm . Fa innaKa taƙ -diru walã aƙ ’diru wa Ta ’å-lamu walã a ’ålamu wa
anTa allãmul guyub.
Allahumma in kunta ta’ ålamu a nna hã zal amra khairul liy fĩ dĩniy wa ma’ãshĩ wa
ãƙibatu amriy faƙ-dirhu lĩ wa yas ’sirhu lĩ summa bãrik liy fĩhi . Wa’in kunta ta’ ålamu
anna hazal amra sharrul -liy fĩ dĩniy wa ma’ ãshiy wa ãƙibati amriy fas’rif-hu anniy
was’rif-niy anhu, waƙ-dir liy al -khaira haisu kãna summa ardiy niy.
Sannan sai ya am baci bukatarsa.
Ana yin wannan istihãra n e a bayan an sallaci (sallah) raka’oi biyu na nafila anyi
sallama .
Istihãrar ma su dũba kuma, sukan yi ne ta hanyar bugun ƙ asa da ake ƙira Ramlu . Shi
ramlu yana daga cikin ilimin alƙaluma.
FASALI :
Istihãrar Ramlu (bugun ƙasa) da yadda ake yinta .
Bugun ƙa sa da ake yi da sũnan istihãra don ayi kirdãdon gaibu bai halatta ba . Masu
bũgun ƙasa sukan yi amfani da alƙaluma ne su buge su akan ƙasa, ƙarshe su fitar da
wani alƙalami da zai bayar da bayanin gaibu da ake sa ran fãruwar sa.
Ba irin alƙaluma ne da ka s ani (Biro) ko ice da ake feƙewa asa cikin taddawa (tawada)
ba. Alƙaluman ramlu zã ne ne guda goma sha shida; wato alƙaluman guda goma sha
shida ne, g asu a jere kamar haka:
31
31
No. SIFFAR ALƘALAMI SŨNAN ALƘALAMI
1
Ahyan (Rãhika)
2
Inkis
3
Humrah
4
Bayãra
5
Nasaratul khãrija
6
Nasaratul Dãkila
7
Itbatu Dãkila (Rãyatul Far’hi)
8
Itbatu khãrij a
9
Jaudala (kausaji)
10
Naƙayil kuddi
11
Ƙabrud Dãkila
12
Ƙabrud khãrija
13
Jamã’a
14
Al-Iƙlah (Shiƙaf)
15
Al-Ijma
16
Ɗarĩƙ
Alƙaluman bugun ƙasa .
Waɗannan sune alƙaluman bugun ƙasa. Kamar yadda nayi bayãni, akan bugã su ne da
juna a samu alƙalamin da zai bayar da bayani n lãbã rin gaibu. Shi ma alƙalamin da zai
bayar da lãbãrin gaibu yakan kasance mai siffar ɗaya daga c ikin a lƙaluma na sama da
na rubũ ta.
32
32
Yadda ake bugun ƙasa.
A lõkacin da mai bugun ƙasa ke son ya fitar da alƙaluma, zai samu rairayi (ƙasa mara
duwã tsu) ya gyara kanta yadda za i iya rubutu akai, sai ya fitar da alƙaluma guda hu ɗun
farko (ba hu ɗu na sama da na rub uta ba).
Alƙaluma hu ɗun farko ana fitar da su ne ta hanyar zubi. Kafin mai bugun ƙasa ya zuba
takti, zai yi niyyar Allah (SWA) Ya sa bugunsa ya bada sahihin lãbãri , sannan:
1. Sai ya dangwala yatsansa akan ƙasar, ya ɗaga ya sake dangwalawa a gefen na
farko, yayi ta maimaitawa (da sauri ba tare da ƙidayawa ba) har sai ya samu dogon
layi kamar haka:
2. Zai maimaita irin dangwalawar da yayi ya samu lãyin farko, a kasan lãyi na farko
amma kar yakai lãyin farko tsawo. Ya kuma zãna wani gajeren lãyin a ƙasa, ya
kuma zãna lãyin ƙarshe. Zubin , (daga farko zuwa ƙarshe) zai zama kamar haka:
Wannan zubi ta hanyar dangwalawar lãyuka guda hu ɗu, idan an zubashi shi ake ƙira
takti. Daga taktin da aka zuba ake fitar da alƙalamin farko .
Za a ƙidaya dangwalen l ãyin farko, biyu-biyu, har zuwa abin da ya rage a ƙarshe. Idan
ya rage ɗaya sai a ajiye dangwale ɗaya, idan yã rage biyu sai a ajiye dangwale biyu (ko
lãyi). Haka za’a ƙidaya kowane lãyin a ajiye (dangwalen) abinda ya rage a karshe. Ga
misali:
33
33
A wannan mis ãli na sama, taktinmu ya fitar da alƙalami n Jaudala (kausaji) . Sai a ajiye
shi a gefe, a sake zuba tak ti a fitar da alƙalami na biyu . A sake zuba takti a fitar da
alƙalami na uku, a sake zubawa a fitar da alƙalami na hu ɗu sannan sai a jerasu kamar
haka :
Waɗannan alƙaluma hu ɗun farko da aka samu kowannensu daga takti su ake kira
IYAYE. Daga jikin iyay e za a haifar da ƴaƴa. Za’a ɗauki kãyin alƙalamin farko a ajiye
a gefe, a ɗauki k ãyin alƙalami na biyu a ajiye a kasan wanda aka fara ajiyewa, da haka
za’a fitar da alƙalami na biyar. Kamar haka:
Alƙalami mai s ũna Iƙla ya fita daga k ãyuwan iy ãyen (alƙaluma) guda hu ɗu. Sai muje
zuwa gida na shida.
Daga ƙirjin IYAYE sai a fitar da alƙalami n gida na shida. Daga cikkunan iyaye sai a
fitar da alƙalami na bakwai , sannan na takwas ya samu daga ƙafõfin iyãye . Gidajenmu
guda takwas (a wannann misalin) za su zama suna da alƙaluma kamar haka:
Alƙaluma takwas na farko (Iyãye da ƴaƴayensu) sun samu (a cikin gid ãje takwas) , sai a
kõma ƙasan k õwane alƙaluma biy u a ha ɗe (ha ɗewar ake cewa bugu) su bayar da
alƙalami na gaba. Kamar haka:
Alƙaluma hu ɗu da muka s ãmu a ƙasan takwas, suma za a bugesu biyu -biyu sai su haifar
da alƙaluma biyu a gidan 13 da 14. Gidan sha uku da sha hu ɗu (in an buge) za su haifi
alƙalam in gidan 15. Ƙarshe sai a buga alƙalamin gida na 15 da alƙalamin gida na farko
sai su haifar da alƙalamin ƙarshe. Mis ãlinmu tun daga farkon takti, (idan an gama bugu)
zai zama kamar haka:
34
34
Shike nan an gama! Kowane gida (alƙalamin) da yake wurin shi za a kalla ayi hukunci
(da ky ãwunsa ko m ũninsa) wajen bayar da lãbãri .
➢ Misali:
Gida n a takwas shi ne gida n mutuwa , idan wannan bugu na sama mun bugashi ne da
niyyar sanin bayanin rashin lãfiyar wã ne, sai mu dũba gida na takwas mu gani.
Alƙalamin “Ƙabrul khãrij a” Ya nuna cewa wã ne (marar lafiya) zai mutu tun yana yãro
(ba zai warke ba). Kai kasan wannan ƙarya ne!
Idan (a misali) Alhaji Tarƙĩki ne aka dũba masa (wannan) game da jinyar ɗansa kuma
ya yarda da sakamakon ( result ), to haƙiƙa ya kafirta da wanna n ayar da aka sauƙar ma
Annabi Muhammadu (SAW):
إِنه اّلِلهَ عِنْدَهُ عِلْمُ السهاعَةِ وَي ُن َز ِلُ الْغَيْثَ وَي َعْلَمُ مَا ِفِ اْلَْرْحَامِ وَمَاتَدْرِي ن َفْس مَاذَا
تَكْسِبُ غَدًا وَمَا تَدْرِي ن َفْس ِبَِي ِ أَرْضٍ َتَُوتُ إِنه اّلِلهَ عَلِيم خَبِ ْي
35
35
Lalle, Allah a wurinsa kawai sanin sa´a yake (haka l õkacin mutuwar kowa) , kuma
Yanã saukar da girgije, kuma Yanã s anin abin da yake a cikin mahai fannai kuma
wani rai bai san abin da yake aikatãwa a gõbe ba, kuma wani rai bai san a wace
ƙasã yake mutuwa ba. Lalle Allah Masani ne Mai ƙididdidigewa. (31:34)
Manzon Allah (SWA) yayi gaskiya da yace :
Duk wanda yaje wurin bõka ko mai dũba sai ya gaskata shi, to haƙiƙa ya kãfirta
da abin da Allah (SWA) Ya sauƙar ga Annabi Muhammadu (SAW).
Ka lũra da wassu han yoyi (masu sau ƙi) na fitar da takti !
1. Sukan ba wanda za ayi masa duba carbi sai ya rufe idonsa ya kama kwayar carbi
ɗaya. Sai mai dũba ya ƙidaya (biyu -biyu) daga kwayar carbin da aka riƙe har
zuwa ƙarshe. Ta haka zai fitar da alƙaluma hu ɗun farko.
2. Sukan dat si shãfin Alƙur´ãni mai girma sai su ɗauki harrufa hu ɗun farko, k õwane
harafi akwai kwatankwacin alƙalaminsa (a task ĩnul huruf). kaga daga nan an
samu alƙal uma hu ɗun farko.
Abin l ũra anan:
➢ Akan fitar da taktin alƙa luman bugun ƙasa ta hanyar mai rab õ ka sãmu (tossing ).
Dã mutum zai s ãmu dũtsin lud õ (dice) ya kaɗa, idan ya n ũna marra (1, 3, 5)
mutum ya aje dangwale idan ya nuna tagwaye mutum ya aje l ãyi, dã ta wannan
hanyar mutum zai fitar da alƙaluman bugun ƙasa. Ina fatan ka fahimci yadda
tushen lãbãri n ƙaryar yake !
➢ Shara ɗi ne, kafin a buga ƙasa sai an ƙira sunan Andabu (sau biyu) Dayãdabu
(sau biyu )... kõ sunan su waye? Tabbas wa ɗannan ba sunayen Allah ba ne.
Sunayen aljanu ne. Koma sunayen waye, Allah (SWA) Y ã ce:
Kuma Al lah Yanã da sũnãye mãsu kyau . Sai ku rõƙe shi da su, kuma ku bar
waɗanda suke yin ilhãdi a cikin sũnãyenSa : zã a sãka musu abin da suka
kasance sunã aikatãwa. (7:180)
Allah Shi ne Masani.
➢ Ba a buga ƙasa lõkacin da ruwan sama yake sauƙa. Kõ me yasa? Tsoron Arãdu?
➢ Ba a buga ƙasa lõkac in iska mai (kamar iskan damina)
LUDÕ
(DICE )
36
36
Kamar haka ne mai bugun ƙasa zai ta dũba gidaje yana yin hukunci sannan ya bada
lãbãri n gaibu. Akwai littafi da ya jera bayanai, idan kaga alƙalami kaza a gidan kaza :
1. kaza-kaza kaza ne zai faru,
2. kaza-kaza tafiya (karatu London) ba zai yiyu ba ,
3. kaza-kaza auren sa zai yiwu da ita, amma…
4. kaza-kaza waccar mazin aciya ce, ko tana da ciki?
5. kaza-kaza wane shi zai zama gwamn a, kuma…
6. kaza-kaza EFCC za su kãma ka g õbe da yamma.
7. kaza-kaza za ka samu ƙ ãrin girma .
8. kaza-kaza mijinki za i mutu ki g ãji duk dukiyarsa.
9. kaza-kaza yau mai dũba zai mutu! Banda karya ƙasa .
Haka za ka samu bayanai kala -kala, da ya dda za kayi bugun neman lab ãrai bila adadin,
kai har yadda zaka fitar da s unan wanda zai gãji Sarkin garin wa ɗancan gidãdawan !
Yadda bugun ƙasa ke gãno gaibun sãmun alheri ko rashi.
Annabi (SAW) bai buga ƙasa ya gãno wani gaibu ba, bai san gaibu ba (fãc e abinda Allah
(SWA) Ya bashi lã barin zai fãru). Allah (SWA) Ya tabbatar da rashin sanin gaibun
Annabi (SAW) kuma shi (Manzon) ya yar da da maganar tabbatarwan, bai ɓõye wahayin
ba, da aka yi masa wahayi :
Ka ce: "Bã ni mallaka wa raina wani amfãni, kuma haka ban tunku ɗe wata cũta,
fãce abin da Allah Ya so. Kuma dã na kasance inã sanin gaibi, dã lalle ne, nã
yawaita daga alheri kuma cũta bã zã ta shãfe ni ba, nĩ ban zama ba face mai
garga ɗi, kuma mai bãyar da bishãra ga mutãne wa ɗanda suke yin ĩmãni." (7:188)
Duk da cewa masu bugun ƙasa sun san wannan, sun kã firta dashi . Sun yi ĩmãni cewar
ilimin bugun ƙasa yana iya sa a gãno gaibu. Sabõd a haka (mafi yawan shehunnai) suke
dãgewa akan mutãne su yarda cewar Annabi (SAW) ya san gaibu. Suna ganin cewar
mai da’awar cewa Annabi (SAW) bai san gaibu ba, bashi da il imi sõsai (bai kai ga il imin
taurã ri ba).
Da ilimin taurã ri ne masu bugun ƙasa suk e hukunci wajen gãne kyãwu ko mũ nin abinda
zai fãru a gõbe. Kowane taurãro da Allah (SWA) Ya halitta an bashi alƙaluma dai-dai
da ɗabi’arsa. Sabõda haka (a lissafinsu da lũra da ɗabi’un taurã ri) za su iya ganin duk
abinda zai iya fã ruwa da mutum a lõkaci mai zuwa (gõbe, shekara , ds.)
37
37
Kafin naci gaba, tun daga nan ya kamata ka iya banbancewa tsakanin Bõka da Mai
dũba , duk da cewa ban iso ga bayanin bõkanci ba. Dũba ya taƙaita ga bãda lã barun
gaibu, faƙad (b ã ƙãri). Idan wani Shehin m ãlami ya tsaya a iya dũba y ana nuna kar ãma
da ita, ba za ace masa bõka ba, shi yasa Annabi (SAW) ya banbance yace:
Duk wanda yaje wurin Bõka ko Mai-dũba , sai ya tambayeshi wani abu kuma ya
gaskata (bõkan ko mai -dũban), to ba za’a kar ɓi sallarsa ba har (tsawon) dare
arba’in.
Bõkanci ƙãri ne akan dũba, kuma mai dũba bai cika tsaya wa a wurin dũba kawai ba, sai
yã ƙarasa yanda bõkanci yake. Dalili, idan mai dũba ya bada lãb ãrin (gaibun) ab inda zai
fãru marar dã ɗi, sai wanda aka dũba masa ya bu ƙaci ayi masa wata dabãra a tare masa
wannan mummunan abun da zai f ãru dashi. Ko ya nemi a kashe wannan (da aka bashi
lãbãri ) zai kãwo masa cĩkas a rãyuwa . To duk matakin da za ɗauka kuma sai an ƙarasa
wajen bõkanci!
FASALI :
ILIMIN TAURÃRI
Ilimin taurãri sahihin ilimi ne da Allah (SWA) Ya sauƙar a bayinSa tun farkon dũniya,
amma bõkaye ba sa yin amfani da shi ta hanyar da ya kamata. Shaiɗanun (aljanu) sun
kautar dasu hanya , ta hanyar taimaka musu wajen cutar da mutãne da yin shirka .
Tun k ãfin dũniya ta kammala, da Allah (SWA) Ya gina Sama , sai Ya ha licci Falaki
(hanya ce) wadda rãna da wata suke linƙaya (irin tafiyarsu) a cikint a. A cikin Falaki,
rãna bata karo da wata kuma dukkansu basa gajiya da iyo (linƙãya) .
َلَ الشهمْسُ ي َن ْبَغِي َلََا أَنْ تُدْرِكَ الْقَمَرَ وََلَ اللهيْلُ سَابِقُ الن ههَارِوَكُلٌّ ِفِ ف َلَكٍ يَسْبَحُونَ
Rãnã bã ya kamãta a gare ta, ta riski watã. Kuma dare bã ya kamãta a gare shi ya
zama mai tsere wa yini, kuma dukansu a cikin Falaki suke yin iyo (linƙãya) . (36:40)
A cikin Falaki, Allah (SWA) Yã ƙaddara ma Wata masauƙai wan da yake shiga ta ciki
(tsawon kwana 29 ko 30) sannan ya fice:
( وَالشهمْسُ َتَْرِي لِمُسْت َقَر ٍ َلََا ذَلِكَ ت َقْدِيرُ الْعَزِيزِ الْعَلِيمِ 38 ) وَالْقَمَرَ قَدهرَْنَهُ مَنَازِلَ حَىته
عَادَ كَالْعُرْجُونِ الْقَدِيِ
38
38
Kuma rãnã tanã gudãna zuwa ga wani m atabbaci nãta. Wannan ƙaddarãwar
Mabuwãyi ne, Masani. Kuma da watã Mun ƙaddara masa manzilõli, har ya kõma
kamar tsumagiyar murlin dabĩno wadda ta tsũfa. (36:38-39)
Su wa ɗannan manzil õli (masauƙai na tafiyar wata ), sune Burujai guda goma sha biyu.
وَلَقَدْ جَعَلْنَا ِفِ السهمَاءِ ب ُرُوجًا وَزَي هنهاهَا لِلنهاظِرِينَ ( 16 ) وَحَفِظْنَاهَا مِنْ كُل ِ شَيْطَانٍ رَجِيمٍ
(17 ) إَِله مَنِ اسَْتََقَ السهمْعَ فَأَت ْب َعَهُ شِهَاب مُبِني (سورة اْلجر )
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya wa ɗansu Burujai a cikin sama , kuma Muka
ƙawãta ta ga masu kallo. Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shai ɗani wanda ake
jĩfa. Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi. (15:16 -18)
Burujan, guda goma sha biyu, sune:
Ƙidaya SUNAN BURUJAI
(DA LARABCI) FASSARA (HAUSA) SUNAN BURU JAI A WURIN
TŨRÃ WA (Zodiac Signs )
1. Dalwu Gũga (ta rĩjiya ) Aquarius
2 Hũtu Kĩfi Pisces
3 Himlu Rãgo (namijin tinkiya) Aries
4 Sauru Bijimi (Sa) Taurus
5 Jauza’a Maganã ɗisu (tagwai) Gemini
6 Surɗan ƙãguwã Cancer
7 Asadun Zãki Leo
8. Azra ’a Zã’ra (matar wata) Virgo
9. Al-Mizãn Sikeli (magwajin nauyi) Libra
10 Aƙrabu Kunãma Scorpio
11. ƙausu Kwarĩ da baka Sagittarius
12. Jadyu Barewa Capricorn
39
39
ت َبَارَكَ الهذِي جَعَلَ ِفِ السهمَاءِ ب ُرُوجًا وَجَعَلَ فِيهَا سِرَاجًا وَقَمَرًامُنِْيًا ( 61 ) وَهُوَ الهذِي
جَعَلَ اللهيْلَ وَالن ههَارَ خِلْفَةً لِمَنْ أَرَادَ أَنْ يَذهكهرَ أَوْ أَرَادَ شُكُورًا (سورة الفرقان )
Albarka ta tabbat a ga (Allah) Wanda Ya sanya Burujai (na tafiyar wata) a cikin
sama kuma Ya sanya fitila da watã mai has kakewa a cikinta. (25:61)
Kuma Shĩ ne wanda Ya sanya dare da yini a kan mayewa, ga wanda yake son ya yi
tunãni, kõ kuwa ya yi nufin ya gõde. (25:62)
Bayan Burujai, akwai taurãri guda bakwai waɗanda dare da wuni ke shigansu. Kowace
awa (masali ƙarfe 12:0 0 na rana) akwai taur ãron da ake cikinsa. Wato zai zama kowace
sa’a akwai taurãr on da ake cikinsa, kowace rãnã (daga cikin ranakun wata 29 ko 30)
akwai burujin da ake cikinsa . Taurãrin guda bakwai sune:
1. Zuhal
2. Mushtarĩ
3. Marikh
4. Shamsu
5. Zahra
6. Uɗarid
7. ƙamar
Alhamdulillah! Bisa lurã da bincike akan wa ɗannan Burujai da taurãri, Aljanu suka
shigo cikin harkar suka m aida binciken sararin sam ãniya na Astrology (ilimin taur ãri)
ya koma har kar bõkanci. Shi kansa astrology (ilimin taurãri) na yanzu bõkanci ne!
Mun san i, su wa ɗannan B urujai (12) da taurãri (7) a cikinsu akwai kyãwawa da mũnãnã
(masu nahĩsa) da matsakaita . Ko Ãdãwa da Allah (SWA) Ya halakar da su, Yã halakar
dasu ne a rãnaku masu nahĩsa (masu shu’umci) . Allah (SWA) Ya ce:
فَأَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ رَِيًاصَرْصَرًا ِفِ أََيهمٍ َنَِسَاتٍ لِنُذِيقَهُمْ عَذَابَ اْلِْزْيِ ِفِ اْلَْيَاةِ الدُّن ْيَا
وَلَعَذَابُ اْلْخِرَةِ أَخْزَى وَهُمْ َلَ ي ُنْصَرُونَ (سورة فصلت )
40
40
Sai Muka aika, a kansu, da iska mai tsananin sauti da sanyi, a cikin kwãnuka na
shu´umci (masu nah ĩsa), dõmin Mu ɗanɗana musu azãbar wulãƙanci, a cikin
rãyuwar dũniya, kuma lalle azãbar Lãhira ita ce mafi wulãƙantarwa, kuma sũ bã
zã a taimake su ba. (41:16)
1354 - حَدِيث: ي َوْمُ اْلَرْب َعَاءِي َوْمُ َنَْسٍ مُسْتَمِر ٍ، الطرباّن ِف اْلوسط عن جابر،
ويروى اْلمر َبجتناب اْلجامة يوم اْلربعاء، فإنه اليوم الذي أصيب فيه أيوب َبلبَلء،
وما يبدأ جذام وَل برص إَل يوم اْلربعاء، وليلة اْلربعاء، أخرجه ابن ماجه واْلاكم ِف
املستدرك من حديث ابن عمر بسند ضعيف
Kãfin cikakken bay ãni ya zo, anan inaso ka fahimci cewa, gaski ya ne, akwai rãnaku da
suke masu nahĩsa (shu’umai) faƙad !
Dukkan ƙarerayin bõka ye (na kõwane yã re) da masu dũba , sun rãtaya n e ga amfani da
nahĩsã ko saĩdar rãnaku da lõ kuta. Idan tafiya zaka yi, bõka zai dũba nahĩsã ko saĩdar
rãnar ne ya baka lãbã rin ga ibu. Idan aikin sihiri na ƙ eta za’ a aikata, sai a rã na mai nahĩsã .
Idan sihirin mallakar miji ne, a taurãron mushtari mai saĩda za su aikata… haka dai
aljanu su ke kõyar da su sihiri manya -manya masu yawa.
GARGADI:
Mu ji tsoron Allah! Mu kasance ba ruwanmu da nahĩsã ko sa’ĩdar rãnaku wajen
ayyukanmu. Mu tsaya ga umarnin Allah (SWA) da ManzoSa (SAW), mu hanu da
abũbuwan da suka hanamu.
علم النجوم على العقول وَبل ... وطَِلبُ شيءٍ َل ينال ضَلل
ماذا طَِلبك عِلمَ شيءٍ غُي ِبتْ ... من دونه اْلضراءُ ليس ينال
هيهات ما أحد بغامضِ فطنةٍ ... يدري كمِ اْلرزاق واْلجال
إَل الذي فوق السماء مكانه ... فَلِوَجْهِه اإلكرام واإلجَلل
......................................
الْفَأْلُ وَالزهجْرُ وَالْكُههانُ كُلُّهُمُ ... مُضَل ِلُونَ وَدُونَ الْغَيْبِ أَق ْفَالُ
41
41
FASALI :
3.1.2 ILIMIN BÕKANCI.
Ilimin bõkanci baya cika sai an haɗa da sanin istihãrar ‘bugun ƙasa ’ da ‘ilimin taurãri ’.
Da wa ɗannan ilimi guda biyu ne ake sanin rũhanai da han yoyin ƙiransu da wakiltasu
akan aikata wani aiki na sharri (ko mai kyawu –a wajensu). Ta wan ɗanna n hanyõyi ake
samun dã mar ƙiran ifritu da sarkin aljannu…
Bõri bõkancin ƙiran ke ɓantattun aljannu ne. Mai ( bõkanci n) bõri ya dõgara ne da
bayãnen (lãbarin ƙarya) aljannun da yake har ka das u, kuma mai bõkancin bõri yã ron
aljannu ne sai abinda suka ɗõrashi akai.
Bõka (na gaske) mai ilimin taurãri, alj anu suna jin ts õronsa! Abõkansa, sar ãkunan aljanu
ne da manya -manyansu (irinsu ifritu) , Har ka da manyan aljannu kuwa sai an kauce
hanya!
Sũ (Yahũdawa da bõkaye) suna kafa hujja da abin da shai ɗãnu ke karantawa a kan
mulkin Annabi Sulaimãnu (A.S), sukace: Annabi Sulaimanu ya mallaki aljannu (yana
saka su aiki) ta hanyar bõkanci. Allah (SWA) Yace:
…kuma Sulaimã nu bai yi kãfirci (bõkanci) ba, kuma Shai ɗãnun, sũ ne suka yi
kãfirci, suna karantar da mutãne sihiri. Kuma ba a sauƙ ar da shi ba a kan
malã´iku biyu a Bãbila, Harũta da Mãrũta. Kuma ba su sanar da kõwa ba balle su
ce: "Mũ fitina kawai ne, sabõda haka kada ka kãfirta," balle har su yi ta neman
ilimin abin da suke rarrabewa tsakãnin mutum da mãtarsa da shi daga gare su.
Kuma su (mãsu yin sihirin) ba su zama mãsu cũtar da kõwa da shi (sihiri) ba, fãce
da iznin Allah. Kuma suna neman ilimin abin da yake cũtar da su, kuma bã ya
amfaninsu. Kuma lalle ne, haƙiƙa, sun sani, tabbas, wanda ya saye shi, bã ya da
wani rabo a cikin Lãhira. Kuma tir da abin da suka sayar da rãyukansu da shi, dã
sun kasance suna sani.
Yadda lãbã rin yake:
Lãbãrin mulkin Annabi Sulaimanu (A.S).
Annabi Sulaim ãnu (A.S) ɗan Annabi Dãwuda ne . Annabi Dãw ud (A.S) shine wanda
Allah (SWA) Ya sauƙar mas a da Zabũ ra, Ya sanar da shi sana’ar ƙera tufa mai sulke
(bullet proof ). Allah (SWA) Yace:
Kuma Muka sanar da shi sana´ar wata tufa sabõda ku dõmin ya tsare ku daga
makãminku. To, shin, ku mãsu gõdewa ne? (21:80 )
42
42
Annabi Dã wud (A.S) ya kasance mai ƙ õƙarin g aske –gã tsayuwar (sal lar dare) gã azumi
duk bayan kwã na guda – dãɗin sautin karãtunsa (na Zabũra) sai wanda ya saurãra . Allah
(SWA) Yace:
Kuma Muka bai wa Dãwũda Sulaimãn. Mãdalla da bãwanMu, shi. Lalle shi
(Sulaimãn) mai mayar da al´amari ne ga Allah. (38:30)
Annabi Dãwud (A.S) ya kasance yana tuntu ɓar Annabi Sulaimanu game da wassu
mas’alõli.
وَدَاوُدَ وَسُلَيْمَانَ إِذْ َيَْكُمَانِ ِفِ اْلَْرْثِ إِذْ ن َفَشَتْ فِيهِ غَنَمُ الْقَوْمِ وَكُنها ْلُِكْمِهِمْ شَاهِدِينَ
Ka ambata (Yã kai Manzo), Annabin Allah Dãwũda da ɗansa (Annabi Sulaimanu) a
lõkacin da (sũ biyun) sukayi hukunci akan wani case na masu gõna r lambu . Masu
rigimar, tumãkin ɗayansu ne sukayi ɓarna (cikin dare) a gõnar ɗayan. Sai Annabi
Dãwud (A.S) yayi hukunci cewa za a biya ɓarnar da aka yima m ai gõna da tumãkin da
sukayi ɓarnar (ya daidaita ƙĩmar ta’adi da tumãki ). Kuma Mun kasance Mãsu halarta
ga hukuncinsu . Sai Muka fahimtar da ita (mas´alar) ga (Annabi) Sulaiman. Sai
Annabi Sulaiman yace (ba haka za’ ayi ba) mai gõ na ya kar ɓi tumãkin da sukay i masa
ɓarna (yana amfanuwa dasu) har sai an gyãra masa gõnar lambunsa. Allah (SWA) Yace:
Kuma dukansu (Annabi Dãwud da Sulaiman) Mun bã su hukunci da il imi kuma
Muka hõre duwatsu tãre da (Annabi) Dãwũda, sunã tasbĩhi, da tsuntsãye. Kuma
Mun kasance Mãsu a ikatãwa. (21:78 -)
Annabi Sulaiman (A.S) yã gãji mulkin bãbansa (bayan rasuwar bãbansa) a lõkacin yana
da shekaru goma sha uku (13), Kuma Allah (SWA) Ya ƙãra masa da Annabta.
Kuma sulaimãn ya gãji Dãwũda ya ce: "Yã ku mutãne! An sanar da mu maganar
tsuntsã ye, kuma an bã mu daga kõwane abu. Lalle ne wannan haƙĩƙa shi ne falalar
(Allah) bayyananna."
Kuma aka tattara, dõmin (Annabi) Sulaimãn, rundunõninsa, daga aljannu da
mutãne da tsuntsãye, to, sũ anã kange su (ga tafiya).
Har (wata rãna) a lõkacin da suka j e a kan rãfin turũruwa , wata turũruwa (tayi magana)
ta ce, "Yã kũ jama´ar turũruwa! Ku shiga gidãjenku, kada Sulaimãn da rundunõninsa su
kakkarya ku (idan suka tattaka ku) , alhãli kuwa sũ, ba su sani ba." Sai (Annabi
Sulaiman) ya yi murmushi yanã mai dãri ya daga maganarta, kuma ya ce, "Yã
Ubangijĩna! Ka cũsa mini in gõde wa ni´imarKa wadda Ka ni´imta ta a gare ni da kuma
43
43
ga mahaifãna biyu, kuma in aikata aiki na ƙwarai, wanda Kake yarda da shi, kuma Ka
shigar da ni, sabõda rahamarKa, a cikin bãyinKa sãliha i." (27:16 -19)
Annabi Sul aimanu (A.S) ya kasance gwarzon yãƙi . Idan ya shirya tafiya y ãƙi, yakan sa
a sãƙa ƙãtuwar tabarma (mai fã ɗi). Tãbarmar nan, a kanta ne dukkan sõjõji da kayan
yãƙinsu da dabbõbinsu suke tãruwa, sai Annabi Sulaiman (A.S) ya umarci i ska ta tattagi
wannan tãbarmar (da mayaƙan da suke kãyinta) ta lũla dasu sama, tayi tafiyar watanni
dasu a cikin wuni guda , har sai tã kaisu filin dãgã .
Wata rãna Annabi Sulaiman (A.S) ya samu lãbãrin wani sarki a kan wani tsibirin. Sarkin
ya kasance mai tsananin mulki da gallazawa mutãne . Annabi Sulaiman da rundunar
yãƙinsa suka hau kan iska, ta kaisu wannan tsibirin suka yãƙi wannan sarki suka sãmo
ganima mai yawa. Cikin ganimar da aka sãmo, akwai ɗiyar sarkin mai kyawon da
mutãne basu ta ɓa ganin irinta ba.
Bayan ɗiyar sarki ta musulunta (tana mai ƙarancin son musuluntar), sai Annabi
Sulaiman (A.S) ya aure ta. Annabi Sulaiman yana matuƙar son ɗiyar sarkin da ya aura,
amma ita kullum bata rabuwa da kũkã da baƙin ciki idan ta tuna bãbanta da mulkinsa .
Anna bi Sulaiman yace: Meye abin dãmuwa bayan Allah (SWA) Ya canza miki da mulki
fiye da na bãbanki kuma ya shiryar dake i’zuwa musulunci? Tace haka ne, wãto idan na
tuna dashi ne sai kaga hawaye yana zuwa mini! Da ace zaka umurci shai ɗanu (aljanu)
su zãna mini hõtonsa (a ɗãki na) ina gani safe da maraice , da ina sa ran (hoton) zai sa
baƙin cikina ya tafi.
Annabi Sulaimanu ya sa aka zãnawa amarya hõton babanta ( exactly ), ta girke a ɗãkinta.
Bai sani ba, idan ya fita a gidanta, sai ta risuna tayi sujjada ga wann an hoton da ta ƙãra
saka masa tufãfi (ya zama kamar mutum -mutumĩ). kwana arba’in (ita da masu mata
hidima) suna yin sujjada a wannan gunkin sã fe da maraice, Annabin Allah bai sani ba!
Ãsifu ɗan Barkiyya, wani waliyyi ne da ba ya rabuwa da majalasin A nnabi Sulaimanu
dare da rãna, yã samu lãbãrin bautar gunkin da ake a gidan Annabi Sulaimanu (A.S).
Cikin hikima Ãsifu ya nemi Annabi Sulaimanu ya bashi damar yin wa’azi a mutãne ya
yabi annabawa, Annabi Sulaiman ya yarda kuma ya tara masa mutãne .
Ãsifu ya fara wa’azi yana yabon annabawa da suka gabãta har sai da ya gangaro kan
Annabi Sulaimanu, ya yabi ƙuruciyarsa sannan ya tsaya daga nan. Annabi Sulaimanu
ya fusãta , daga baya ya aika aka ƙira masa Ãsifu ya tambayeshi ko me yasa ya yabi
ƙuruciyarsa bai yabi lõka cin annabtarsa ba? Ãsifu yace: Wanin Allah ne, yau kwana
arba’in, ana bauta masa a gidanka a dalilin sõyayyarka ga Mace.
44
44
Yace: Innã lillãhi wa innã ilaihi rãji’un! Nasan baka fa ɗi kome ba sai abinda ya zo maka,
ya shiga gida ya kakkarya h õton da ake bauta masa, ya hõra amarya da masu mata
hidima sannan ya nemi kaya masu tsarki (wa ɗanda yara -mata da ba su fara Jini ba su ka
sãƙa, kuma wata ma’abociyar jinin al’ãda bata ta ɓa ba), ya sanya.
Da Annabi Sulaiman (A.S) ya sanya kaya masu tsarki sai ya tafi can sah ãra, yayi ta kũka
yana tũba wuni guda, sannan ya dãwo gida.
Daman akwai Uwar ‘yayansa da yake bata ajiyar zõbensa idan zai gewaya (biyan
buƙata). Mulkin Annabi Sulaiman ya kasance (Allah Ya ƙaddara) yana jikin zõbensa,
wata rãna shai ɗani (mai sũna Sakrun) ya riki ɗe siffar Annabi Sulaimanu, yazo ya kar ɓi
zõbe a hannun matar ya tafi kan kujerar mulkin Annabi Sulaiman ya zauna. Fitõwarsa
daga b ãyi, ya tambayi zõbensa, matar tace ƙarya kake, Annabi Sulaimanu ya kar ɓi
zõbensa yana can a majalisa. Annabi Sulaiman u yayi nadama ya fita yana cewa Bani -
isrã’ila nĩ ne Annabi Sulaimanu sai suna watsa masa ƙasa.
Annabi Sulaiman (A.S) ya kõma bakin kõgi yana taya masunta aiki suna b ãshi kifi biyu
a kullum, yaci ɗaya ya saida guda a bãshi alkubus. Mulki ya ku ɓuce wa Annabi
Sulaimanu tsawon kwanaki arba’in (kwatankwacin kwanakin da akayi bautar gunki a
gidansa) .
A lõkacin da kwanaki arba’in suka kusanto , sai shai ɗani Sakru yayi hukuncin da ba’a
gamsu dashi ba. Waliy Ãsifu yace da mutãne : Ya Bani -Isrã’ilã, shin kun tsinkayi
banbancin hukunci (sã ɓanin na Annabi Sulaimanu) kamar yadda na gani? Mutãne suka
amsa: Na’am! Mun gani. Sai Ãsifu yace ku jirãni in shiga wurin iyalensa in tambaya ko
sũma basu yarda da abinda muka ƙiy ã ba.
Da waliy Ãsifu ya shiga gidan Annabi Sulaimanu, s ai ya samu lãbãri n fiye da katõ ɓarar
da suka gani. Yace: Innãlillãhi wa innã ilaihi rãji’un! Lalle wannan, tabbas, Jarrabawa
ce bayyananniya. Ya fito majalĩsa yayi bayani a Banĩ -Isrãila.
Da Shai ɗani ya saurãri bayanin waliy Ãsifu, ya tabbata asĩrinsa ya tõ nu, sai yai fiffike
daga wurin (ya tashi sama), ya gifta ta saman kõgi ya jefa zõben silar mulki (na Annabi
Sulaimanu) a cikin kõgin. Allah da ikonSa, kifi ya ha ɗiye zõben kuma masunta suka
kãma (a kõmarsu) tare da wannan kĩfin.
Ranar da kwanaki arba’in su ke cik a, aka sallami Annabi Sulaimãnu da kĩfaye biyu ladan
aikinsa (a wata ruwaya an bashi kyautar kifayen ne bayan an dũkashi da yace shine
Sulaimanu) . A lõkacin da ya tsãga kifin da zai ci, kwatsam! Sai ga zõbensa. Ya sanya a
hannunsa ya fã ɗi ƙasa yayi s ujjada (gõdiya ga Allah (SWA) ) wanda Ya dã wo masa da
mulkinsa. Ya kõma majalĩ sa, mutãne da aljanu da tsuntsã ye sai murnar dawowarsa ake.
45
45
Annabi Sulaimanu ya bayyana tũ barsa kan kuskurensa, aljanu suka bazama neman
(Shai ɗani) Sakru (wannan da ya ɗãna mulkin kwãnaki 40). Da aka kãmo Sakru, aka
fãfuke dutse (ya zama kamar kabari) aka jefa shi ciki, aka tõshe bãkin dũtsen da baƙin
ƙarfe aka lĩƙe da dalma sannan aka jefa dũtsen cikin teku.
Dukkan wannan lãbãri (cikin litt ãfin “Kãmil fit Tãrikh ”), ƙarƙashin fa ɗinSa Ma ɗaukakin
Sarki:
وَلَقَدْ ف َت َنها سُلَيْمَانَ وَأَلْقَي ْنَا عَلَى كُرْسِي ِهِ جَسَدًا ُثُه أََنَبَ
Kuma lalle haƙĩƙa, Mun fitini Sulaiman kuma Muka jefa wani jikin mutum a kan
karagarsa (ta mulki) . Sa´an nan ya mayar da al´amari zuwa gare Mu. (38:34)
Daga nan sai Annabi Sulaimanu ya rõƙi Allah (SWA) mulki da karfin iko akan mutãne ,
aljannu, dabb õbi da tsuntsaye.
Ya ce: "Ya Ubangijĩ na! Ka gãfarta mini, kuma Ka bã ni mulki wanda bã ya kamãta
da kõwa daga bãyãna. Lalle Kai, Kai ne Mai yawan kyauta. (38:35)
Sai Allah (SWA) Ya bã shi ikon mulkan mutãne, Aljanu, dabbobi da tsuntsaye , kuma
Ya hõre masa iska –tanã gudu da umurninsa, tãna tãshi da sauƙi, inda ya nufa. Da
shaiɗãnu du kkan mai gin i, da mai nutsa (a cikin kõguna ). Waɗansu (mũgwãyen
shaiɗãnu kuma ), ɗaɗɗaure a cikin marũruwa. (38:36 -38)
Wannan addu’a (kamar yanda aka rawaito) Allah ne Ya kimsa masa ya rõƙa kamar haka.
Kuma iska takan ɗauko masa ra hõtannin maganganu, kuma yana s ã iska ayyuka :
Wata r ãna Annabi Sulaimanu yana h ĩra tare da wani mutum, sai Malã’ikan mutuwa ya
kawo masa ziy ãra. A lõkacin da Mal ã’ikan mutuwa ya ga mutumin da yake wajen
Annabi Sulaimanu (A.S) sai yayi murmushi. Bayan ya tafi, sai wannan mutumin yace:
Ya annabin Allah! Ko waye ne wannan (da ya tafi)? Annabi Sulaiman yace Mala’i kan
mutuwa ne. M utumin yace naga yayi murmushi a lõkacin da ya kalle ni, ka umarci iska
man ta kaini ƙasar Indiya. Annabi Sulaimanu (A.S) ya umarci iska ta kai wannan mutum
ƙasar Indiya t a jefar dashi.
Jim ka ɗan, sai Mala’ikan mutuwa ya dawo wurin Annabi Sulaimanu yace: A n umarce
ni na ɗauki r ãyin mutumin da naga (ɗãzu) a wurinka a can ƙasar Indiya, kuma sai na
ganshi a nan!
46
46
Lãbãrin A nnabi Sulaimanu da Sarauniya Ba lkĩsu mai gadon zĩnãri.
A can ƙasar Yam an, anyi wata sarauniya da ake k ira Bilkĩsu. Sarauniya, Balkĩsu j ĩkar
sarkin aljanu (Sarki Amru ɗan Umair) , tana da gadõ na mulki wanda aka ƙerashi da
zĩnãre (gwal).
Wata rãna Annabi Sulaiman (A.S) y ã fita tã re da tawagarsa ana tafiya , sun iso wurin da
ake son aikin Hud -huda (na geophysicist ) na bincika gurbin da za a tõna rĩjiya marar
zurfi, sai Annabi Sulaimanu ya tsinkayi wurin da (tsuntsu) Hud -huda ke tare rãna yaga
Hud-huda bayanan.
Kuma ya binciki tsuntsãye (ya leƙa duka bai ganeshi ba) , sai ya ce: "Me ya kãre
ni bã ni ganin hud -hudu , kõ ya kasance daga mãsu fakuwa ne (ya ɓũya)?"
Annabi Sulaimanu yace:
"Lalle ne zã ni azabta shi azãba mai tsanani kõ kuwa lalle in yanka shi, kõ kuwa
lalle ya zo mini da dalĩli bayyananne."
A lõkacin da aka nemi tsuntsu Hud -huda bã ya nan , bai dãwo ba , Sai ya zauna bã nesa
ba (bai da ɗe ba a can wajen shãwãgi) , sa´an nan (ya dãwo wurin Annabi
Sulaimanu ) ya ce: "Nã sa n abin da ba ka sani ba, kuma na zo maka daga (birnin)
Saba ’i, da wani lãbã ri tabbatacce." Ganin ido:
"Lalle ni nã sãmi wata mace wadda tanã mulkinsu kuma an bã ta daga dukkan
kõme (na mulkin dũniya) , kuma tanã da gadon sarauta mai girma.
Gadon sarauta da take zama , a cikin wani katã ɓãren gini, an ƙerashi da gwal, an
rarrãt aya masa kayan ƙyali masu tsãda –na Yãƙutu da dũtsin zabardaji da Lu’u -lu’u.
Hud-huda yace: "Na sãme ta ita da mutãnenta, sunã yin su jjada ga rãnã, baicin
Allah, kuma Shai ɗan ya ƙawãce musu ayyukansu, sabõda haka ya karkatar da su
daga hanya, sa´an nan sũ, ba su shiryuwa." …
Annabi Sulaimanu Ya ce: "Za mu dũba (muga) shin kã yi gaskiya ne, kõ kuwa kã
kasance daga maƙaryata?" Zan aike ka "Ka tafi da takardata wannan, sa´an nan
ka jefa ta zuwa gare su, sa´an nan kuma ka jũya daga barinsu, sa´an nan ka ga
mene ne suke mayarwa (me zasu shawarta )."
A lõkacin da tsuntsu Hud -huda ya k õma Yaman –garin Saba’a, ya jefa taka rdar
(wasiƙar) Annabi Sulaimanu (A.S) a kan Sarauniya Bilkisu, taga tsuntsu ya koma gefe
yana jira sai Ta ce: "Yã kũ mashawarta! Lalle ne, an jefo, zuwa gareni, wata
takarda mai girma." Ta karanta lãyin farko tace: "Lalle ita (wannan takarda) daga
47
47
Sulaiman take, kuma lalle ita (an fara rubũ tawa a samanta) da sũnan Allah, Mai
rahama, Mai jin ƙ ai."
Sãƙon da takardar ke ɗauke dashi shine: "Kada ku yi girman kai a gare ni, kuma ku
zo mini kunã mãsu sallamãwa."
Sarauniya Bilkisu (mai gadon zĩnã re) Ta ce: "Yã ku mashawarta ! Ku yi Mini fatawa
ga al´amarĩna, ban kasance mai yanke wani al´amari ba, sai kun halarta."
Suka ce: "Mũ ma´abũta ƙ arfi ne, kuma ma´a bũta yãƙi mai tsanani ne, kuma al´amari yã
kõma zuwa gare ki, sabõda haka ki dũba mene ne zã ki yi umurn i (da s hi)?"
Sarauniya ta ji tsõron kar ta fa ɗi ba daidai ba, rundunar yaƙin Annab i Sulaiman ta shigo
mata gari ta yi fata -fata da garin , sai
Ta ce: "Lalle sarã kuna idan sun shiga wata alƙarya (da mayaƙansu) , sai su ɓãta ta (suyi
mata kaca -kaca), kuma su sanya mã su darajar mutãnenta ƙasƙanta ttu. Kuma kamar
wancan ne suke a ikatãwa (gãlibi) ." Sarauniya tace gara mu nemi sulhu da zaman lafiya !
"Kuma lalle nĩ mai aikãwa ce zuwa gare su da kyauta, sa´an nan mai dũbawa ce (na ga):
Da me manzannin (da zan aika) zã su kõm o."
To, a lõkacin da (kyauta r sarauniya ) ya je wa Sulaiman ya ce: "Shin, za ku ƙãra ni da
dũkiya ne? To, abin da Allah Ya bã ni, shi ne mafi alheri daga abin da Ya bã ku. A´a,
kũ ne kuke yin farin ciki da kyautarku." Kai ɗan aike! "Ka kõma zuwa gare su. Sa ´an
nan (idan ba su zo sun musulunta ba) lalle munã je musu da rundunõni, bãbu wata
tãɓukawa r (gwabza yãƙi) da za su iya game da su (rundunõnin da za mu zo da su), kuma
lalle (idan suka yarda muka zo) munã fitar da su daga gare ta, sunã mafi wulãkantuwa,
kuma sunã ƙasƙantattu."
To a lõ kacin da Annabi Sulaiman (A.S) ya gama gamsuwa cewar sarauniya za ta zo
wurinsa ta musulunta (da jama’arta), sai yayi farin ciki ya tãra mutãne da aljanu da suke
ƙarƙashinsa. Ya ce: "Yã ku mashãwarta! Wannenku zai zo (ya ɗauko) mini da
gadonta (na mulki) , a gabãnin (kãfin) su zo sunã mãsu sallamãwa?" Sabõda su
yarda da annab cina idan sun zo.
Wani mai ƙarfi (If-Rĩtu) daga aljannu ya ce: "Nĩ inã (iya) zo maka da shi a gabãnin ka
tãshi daga matsayinka (majal ĩsa). Kuma lalle nĩ a ga re shi, haƙĩƙa, mai ƙarfi ne
amintacce (ina da ƙarfin ɗauko shi , kuma ba zan ciri kome a jikinsa ba )."
Annabi Sulaiman (A.S) yace: ina son wanda zai iya ɗauko gadon da sauri fiye da
wannan! Sai Wanda yake a wurinsa akwai wani il imi (na Ismul -lãhi al -a’azam )
daga Littafi ya ce: "Ni inã (iya) zõ maka da shi a gabãnin ƙy aftãwar ganinka ta
kõma gare ka " (kafin kyaftawar ido) .
48
48
Wasu suka ce ana nufin kamar kãfin ka waiga ka dãwo da kãyinka , ake nufi da kyaftawa.
Da Ãsifu (marubucin Annabi Sulaiman) ya ce zai iya kãwo gadon sarauniya Bilkisu
kafin Annabi Sulaiman ya jũya ya dawo da ganinsa, sai Annabi Sulaiman (A.S) ya
yarda. Ãsifu yayi alwala yace da Annabi sulaiman ya kalli wajen ƙasar Yaman. Kafin
Annabi Sulaiman ya jũyo, Ãsifu yã rõƙi Allah (SWA) akan Ya ƙadda ra (kun, fa yakun)
gadon Sarauniya Bilkisu ya kasance a gaban Annabi Sulaiman (A.S).
Allah Maji r õƙon bawa, Ya ƙaddara gadon Sarauniya Bilkisu da yake ƙasar Yaman ya
nutse cikin ƙasã ya ɓullo a gaban Annabi Sulaiman (A.S) da ke Baitul -Muƙaddas, sai
kawai Annabi Sulaiman yaga gado a gabansa.
To, a lõkacin da ya gan shi matabbaci a wurinsa, (sai) ya ce: "Wannan daga falalar
Ubangijĩna yake, dõmin Ya jarraba ni: Shin, zan gõde ne, kõ kuwa zan butulce!
Kuma wanda ya gõde, to, yanã gõdewa ne dõmin kansa, kuma w anda ya kãfirta,
to, lalle Ubangijina Wadãtacce ne, Karĩmi."
Annabi Sulaiman Ya ce: "Ku canza kamar gadonta gare ta, mu gani, shin zã ta
shiryu, kõ kuwa tanã kasancewa daga wa ɗanda bã su shiryuwa."
Sai aka cire bezar gadon da gwuiwar hannayensa, aka canza shimfi ɗu (irinsu) –wurin
shifiɗa Ja aka mayar da shimfi ɗa rãwaya (yellow) da sunkuyen haka, wurin shimfi ɗa
launin tsanwa ( Green ) aka mayar shimfi ɗa Ja, da sunkuyen haka – gado ya can za siffar
launi kuma tufãfinsa suka dena jan ƙasa , ya zama kana iya ganin ƙ afãfunsa na zĩnaren
gwal.
To a lõkacin da (Sarauniya Bilkisu) ta je (gaban fadar Annabi Sulaiman) aka ce
(mata) "Shin, kamar wannan gadon sarautarki yake?" Ta ce: "Kamar dai shĩne
(wannan, kamarsu ɗaya).
(Annabi Sulaiman yana b ãda lãbãri yace) : Kuma an bã mu il imi (tauhidi da ƙudura)
daga gabãninta kuma mun kasance mãsu sallamãwar (al´amari ga Allah)." Kuma
abin da ta kasance tanã bautãwa, baicin Allah, (shi) ya kange ta (tun farko ta
fahimci gaskiya duk da kasancewarta mai kaifin hankali da basĩra ). Lalle ita, tã
kasance (ta tãshi ne) daga mutãne kãfirai.
To daman Annabi Sulaimanu ya samu lãbãrin Bilkĩsu tana da gãshi mai yawa a
ƙwabrinta (wanda ya wuce misãli). Sabõda haka yasa aka shirya wata hanya zuwa cikin
fãda (misalin Jan carpet da ake sanyawa sh ũgaban ƙasa) . Hanyar wata dõguwar rumfa
ce da akan iya ɗauke ta, cikin rumfar aka sanya dandamalin gilãshi ( Marbles ) guda biyu
ninke –kana ganin na cikin kamar ruwan teku da kĩ faye a cikinsa . Annabi Sulaiman
49
49
(A.S) yana cikin fãda (ƙarshen hanyar shig õwa) yana kan kujera, yana kallon yadda
Sarauniya Bilkisu zata tãka ta shigõ, sai
Aka ce mata, "Ki shiga a gidan sarauta." To, a lõkacin da ta gan shi (dandamalin
gilãshin) , tã yi zaton sa wa ni gul bi ne, kuma ta kuranye daga ƙwaurinta (zata
shiga) . Sai Annabi Sulaim an ya kawar da kã yinsa , Ya ce: "Lalle ne shi, (ba ruwa ba
ne) sõro ne mai santsi daga madũbai (na marbles )."
Tãke Sarauniya Bilkisu ta raina kanta , ta tabbatar da risãlar Annabi Sulaimanu, tayi
nadãmar bautar wanin Allah da sukayi Ta ce: "Yã Ubangijĩna! " Lalle nĩ, na zãlunci
kaina, kuma nã sallama al´amari tãre da Sulaiman ga Allah, Ubangijin halittu."
Annabi Sulaiman (A.S) yasa aka ƙera masa abin aski ( clipper ), aka ba Bilkĩsu ta aske
gãshin ƙwabrinta, Daga baya ya aureta (yana sonta kwarai), ya mayar da ita mulkinta
na garin Saba’a. Kowane wata yakan je wurinta (sau ɗaya) ya kwana uku sannan ya
dãwo.
Wassu suka ce: Ba Annabi Sulaimanu ne ya auri Sarauniya Bilkĩsu ba, a lõkacin da ya
nuna mata cewar baya dãcewa a musulunci ta zauna haka bã miji, sai tace ya aurar da
ita ga Sarki Hamdãna (na ƙabilar Tubba’i). Sai ya ɗaura musu aure , ya mayar da ita
ƙasarta (Yaman), ya wakilta mata mijinta a sarautar sa nnan ya t ãra aljanun ƙasar Yaman
ya umarcesu da yin biyayya a wakilin Sarauniya Bilkisu. Bayan rasuwar anna bi
Sulaim ãnu, aljanu suka yi tãwãye a sarki Hamdãna, mulkinsa da na Sarauniya Bilkĩsu
ya ƙãre (ta hanyar jũyin mulki) .
Wafãtin Annabi Sulaimanu (A.S)
Har a lõkacin da ajalin Annabi Sulaimanu ya gab ãto, alhali ya ka sance sau tãri idan yayi
Sallah, bishiya takan tõfo (ta tsiro) a gabansa, sai ya tambayeta sũnanta da amfaninta.
Idan ta kasance ta nõmawa ce sai a noma ta, idan ta kasance ta mãgani ce sai ya rubuta
sunanta da mãganinta.
Wata rãna bayan Annabi Sulaimanu (A.S) yayi Sallah, wata bishiya ta tsiro a gabansa.
Ya tambayi sunan bishiya r, tace: sũnanta “Kurnũbah” , Ya tambaya: ga me kika fito?
Tace: Ga rũsa wannan gida (Baitul Muƙaddis). Sai Annabi Sulaiman yace: Allah (SWA)
ba zai rũsa wannan birni ina cikinsa ba, ke ce dai akan idonki zan halaka sannan wannan
birni ya rũshe. Sai ya cire ta, sannan yace:
اللههُمه عَم ِ عَلَى اْلِْن ِ مَوِْتِ حَىته ي َعْلَمَ النهاسُ أَنه اْلِْنه َلَ ي َعْلَمُونَ الْغَيْبَ
Ya Ubangiji! Ka ɓõye ma aljannu mutuwa ta har mutãne su gãne (su sani) cewar
Aljannu (maƙaryata ne) basu san gaibu ba.
50
50
To a wani lõ kaci da Annabi Sulaimanu (A.S) ya dõgara a jikin sandarsa (yana tsaye) ya
tada kabbarar sallah, aljanu suna ta famar aikin wahala da ya saka su, sai Allah (SWA)
Ya ƙaddara masa mutuwa. Allah (SWA) Yace:
Sa´an nan a lõkacin d a Muka hukunta mutuwa a kansa (ta ɗauke ransa) , bãbu
abin da ya ja hankalinsu (ya nũna musu) , a kan mutuwarsa, fãce dabbar ƙ asa
(garã ) wadda tak e cin sandarsa. To a lõkacin da (Annabi Sulaiman) ya fã ɗi (ƙasa),
sai aljannu (suka gãne mutuwarsa) suka bayyana (ga mutãne) cewa dã sun kasance
sun san (sanin) gaibu , dã ba su zauna (sun dukufa da aiki) a cikin azãba mai
wulãkantarwa ba. (34:14)
Annabi Sulaimanu (A.S) y ãyi wafã ti yana da shekaru 53, y ãyi mulki tsawon shekaru 40.
Bayan rasuwarsa, Bani -Isrã’ila suka s o su san tsawon lõkacin rasuwarsa (aljanu n ã aiki),
sai suka sãmo sanda suka ba wa garã (termite s) taci. Da garã ta cinye sandan a kwana
guda da dare ɗaya, sai suka lissafa ( carbon dating ) suka sã mu ya rasu kimãnin shekara
ɗaya. Daga nan suka san cewa aljanu (shai ɗãnu) maƙaryata ne basu san gaibu ba (sanin
gaibu sai Allah) . Dã sheɗãnu sun san gaibu da basu shekara guda , cur, suna aiki a Annabi
Sulaimanu bayan rasuwarsa ba.
(Ance) Da shai ɗãnu suka so su sãkawa garã sai suka ce: d ã kina cin abinci dã mun k ãwo
miki mafi dã ɗi, kuma b ãkya sha balle mu kãwo miki abin sha mafi dã ɗi, Amma (munyi
alƙawari) zamu na cir õ (mu samar) miki ruwa da lãka a duk yanda ki ke. Wannan shine
dalilin da yasa kake g anin lãka a cikin tsakiyar itacen da garã ta kama, shine dalilin da
yasa kake ganin shũ ri gininsa da lãka kuma siffar gininsa na shai ɗãnu (gõdiyar aljanu
ne ga garã) .1
1. Tafsirin Ibn Kathir (ya danganta labarin da Malaman Ahlul Kitab).
SHŨRI KO GIDAN GARÃ (ANT HILL )
51
51
Tõ sai Yahũdawa da bõkaye suk a yarda da jita -jitar shaiɗãnu kan mulkin Annabi
Sulaimãnu (A.S), suka ce: Annabi Sulaimanu ya mall aki aljannu ta hanyar sihiri, su kayi
maki rci suka tõ no abubuwan da suka binne a ƙasan karagarsa, suka ce wannan shine
asirin da sarki Sulaimanu ya yi amfani dashi ya mallaki talak ãwa. Allah (SWA) Yã
barranta r da shi, Yace:
…kuma Sulaimãnu bai yi kãfirci ba, kuma Shai ɗãnun, sũ ne suka yi kãfirci, suna
karantar da mutãne sihiri …
Kuma shai ɗanu suka fitar da wata ƙarya wai shi asiri (sihiri) an sauƙar dashi ne (tun
farkon dũniya) akan wa ɗansu mal ã’iku a Bãbĩla n ƙasar iraƙi (sunansu Hãrũta da
Mãrũta). Wai suka ce wa ɗannan malã’ ikun, idan zã su kõyar da asĩ ri (tsãfi) sai sunyi wa
mutum kashedi cewa: Asĩrin da z ã mu kõya maka yanada ha ɗari! Yana iya haifar da
fitina ya kai mutum ga kãfirci don haka ka kiyaye! Sannan (Wai) sai su kõ yar da asirai
harda wanda z ã ayi a raba (auren) miji da mata…
Allah (SWA) Yace:
Kuma ba a sauƙar da shi (ilimin tsãfi) ba a kan malã´iku biyu a Bãbila, Harũta da
Mãrũta. Kuma (Harũta da Mãrũta ) ba su sanar da kõwa ba balle su ce: "Mũ
(zamu b aka asĩri) fitina kawai ne (ka kiyaye) , sabõda haka kada ka kãfirta," balle
har su yi ta neman ilimin (asiri) abin da suke rarrabewa tsakãnin mutum da
mãtarsa da shi daga gare su. Kuma su (mãsu yin sihirin) ba su zama mãsu cũtar
da kõwa da shi (sihiri) ba, fãce da iznin Allah. Kuma suna neman ilimin abin da
yake cũtar da su, kuma bã ya amfaninsu. Kuma lalle ne, haƙiƙa, sun sani, tabbas,
wanda ya saye shi (ya bada abin sadaka (na gõro)) , bã ya da wani rabo a cikin
Lãhira. Kuma tir da abin da suka sayar da rã yukansu da shi, dã sun kasance suna
sani. (2:102)
الْفَأْلُ وَالزهجْرُ وَالْكُههانُ كُلُّهُمُ ... مُضَل ِلُونَ وَدُونَ الْغَيْبِ أَق ْفَالُ
Cĩgaba da bay ãnin ilimin bõkanci:
1. Daga cikin ilimin bõkanci, akwai masu amfani da sihirin Kaldãnin. Su
kaldãnĩna, mutãne ne da suka yi ĩmani da taurã rin nan guda bakwai (Zuhal,
Mushtariy, Zahra , Uɗarid, Marikh, Shamsu, da ƙamar ) suna bauta musu, da cewa
sune suke zãg ãwa (tsawon shekara) sai su zo da alheri, wani lõkaci su zo da bã
yanda kasõ ba! Su ne (Kaldã nĩna) wa ɗanda aka aika musu Annabi Ibr ãhim (A.S)
yayi musu wa’azi cikin hikima kamar haka :
52
52
To, a lõkacin da dare ya rufe a kansa (shi Annabi Ibr ãhim) , ya ga wani taurãro
(Mush’tarĩ) , ya ce: "Wannan ne, ubangijina?" Sa´an nan a lõkacin da (taurã ron)
ya fa ɗi, ya ce: " Ba ni son mãsu fã ɗuwa."
Sa´an nan a lõkacin da ya ga watã (taurãron ƙ amar) yanã mai bayyana, ya ce:
"Wannan ne Ubangijina?" Sa´an nan a lõkacin da ya fã ɗi, ya ce: "Lalle ne idan
Ubangijina bai shiryar da ni ba, haƙĩƙa, inã kasancewa daga mutãne ɓatattu."
Sa´an nan a lõkacin da ya ga rãnã (taurã ron Shamsu) tanã bayyana, ya ce:
"Wannan shĩ ne Ubangijina, wannan ne mafi girma?" Sa´an nan a lõkacin da ta
fãɗi, ya ce: "Ya mutãnena! Lalle ne ni barrantacce nake daga abin da kuke yi na
shirki."
"Lalle ne nĩ, na f uskantar da fuskata ga wanda, Ya ƙãga halittar sammai da ƙasa,
inã mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bã ni cikin mãsu shirki."
Kuma mutãnensa suka yi musu da shi (suka bayyana masa shãci -faɗi (illusion )
game da alherin da taurãri kan zo dashi) . Ya ce: "Shi n kunã musu da ni a cikin
sha´an in Allah, alhãli kuwa Yã shiryar da ni? Kuma bã ni tsõron abin da kuke yin
shirki da shi (na nahĩsa da sa’ida ), fãce idan Ubangijina Yã so wani abu (sai ya
same ni) . Ubangijina Ya yalwaci dukkan kõme da ilmi. Shin, ba zã ku yi tunãni
ba?" "Kuma yãyã zan jin tsõron abinda kuka yi shirki da shi, kuma (kũ) bã ku jin
tsõron cewa lalle ne kũ, kun yi shirki da Allah, abin da (Allah) bai saukar da wata
hujja ba game da shi? To, wane ɓangare daga sãshen biyu (nĩ ko kũ) ne mafi
cancan ta da aminci, idan kun kasance kunã sani?" (6:76 -81)
Nayi bayanin yadda bõkaye suke amfani da istih ãrar bugun ƙasa su fitar da taurãro
sannan suyi hukunci da ky ãwu ko muninsa wajen bayar da lãbarin sanin gaibu.
عَنْ زَيْدِ بْنِ خَالِدِ اْلُْهَِنِ ِ رَضِيَاّلِلهُ عَنْهُ، أَنههُ قَالَ: صَلهى بِنَا رَسُولُ هللاِ صَلهى اّلِلهُ عَلَيْهِ
وَسَلهمَ صََلةَ الصُّبْحِ ِفِ اْلُْدَيْبِيَةِ ِفِ أَثَرِ َسََاءٍ كَانَتْ مِنَ اللهيْلِ ، ف َلَمها انْصَرَفَ أَق ْبَلَ عَلَى
النهاسِ ف َقَالَ : هَلْ تَ دْرُونَ مَاذَا قَالَ رَبُّ كُمْ؟ قَالُوا: اّلِلهُ وَرَسُولُهُ أَعْلَمُ ، قَالَ صَ لهى اّلِلهُ عَلَيْهِ
وَسَلهمَ: قَالَ : أَصْ بَحَ مِنْ عِبَادِي مُؤْمِن بِ ، وَكَافِر ، فَأَمها مَنْ قَالَ : مُطِرَْنَ بِفَضْلِ هللاِ وَرَحَْ تِهِ ،
فَذَلِكَ مُؤْ مِن بِ كَافِر َبِلْكَوَاكِبِ، وَأَمها مَنْ قَالَ : مُطِرَْنَ بِن َوْءِ كَذَا وَكَذَا، فَذَلِكَ كَافِر بِ
مُؤْمِن َبِلْكَوَاكِبِ. رَوَاهُ الْبُخَارِيُّ ِفِ "الصهحِيحِ" عَنِ الْقَعْنَبِ ِ.
53
53
Manzo (SAW) yace: Shin kun san me (Allah) Ubangijinku yace? Sahabbai suka
ce: Allah da ManzonSa sune ma fi sani! Mai tsira da aminci yace: (Allah) Ya ce:
Daga cikin bãyi Na wassu suna wayen gari suna mũminai, wasu k ãfirai. Tõ amma
wanda yace an mana ruwa cikin ikon Allah –rahamarSa da FalalarSa, tõ
wancaninka shine yayi ĩmãni daNi ya k ãfirta da taurãri. Kuma amma wanda yace
an mana ruwa sabõda (anyi zãfi, ko taurãro) nau’in kaza da kaza, to wancaninka
ya K ãfirce miNi yayi ĩmãni da taurãri.
Sabõda haka, duk malamin da ya yi bugun Jumu’a ya sanar da lõkacin k ãmun Dãmina
(lõkacin ruwan sama) ko fitar dãmina ya ka firce wa Allah (SWA) kuma ya yi bõkanci .
Har ila yau, bõkaye kanyi amfani da lõkutan hũdowar wa ɗannan taurãri (guda bakwai)
wajen aikata sihiri . Misali, sihirin mallake budurwa (sõyayya) ana aika tãwa a lõ kacin
da taurãro n Mushtari ya fito, a wannan lõ kacin ne ake samun shai ɗanu (ruhãnai) da suka
kwarai wajen kar ɓan kwantirãgi n haɗa sõyayya (ta hanyar shiga jikin mace) .
2. Daga cikin ilimin bõkanci, akwai sanin hanyõyin kiran shai ɗãnu (da ake musu
laƙabi da rõhãnai) da b ãsu kwantirãgi. Rõhãnai da ake basu aiki na alheri2 (kamar
haɗa sõyayya) su ake kira uluwwiy (rõhãnai m ũminai), dukkan sunayensu yana
ƙãrewa da ĩlu (misali: Mĩkã’ ĩlu da Jibrã -ĩlu). Rõh ãnai wa ɗanda ake b ãsu aiki na
ƙeta (kamar haukatar da wani ko kisa ) su ake kira sufuliy (rõhãnai kãfirai),
sunaye nsu yana ƙãrewa da -ɗiyshu (misali: Mĩkã -ɗĩshu da “Jibrã -ɗĩshu”).
➢ Sama da shekaru goma sha biyar, nã saurãri wani mai mãganin gargajiya
yana bayani a gidan rediyo (yana ambatar rõhãnai). Nayi tatt aki zuwa
shagonsa dake kwanar ɗan-marke (Kano). Da shike t ambaya na je, ban
yanki kati ba, na tambayeshi game da rõhãne. Ya ce (sũ rõhanai) rũhi ne
na sãlihan bãyi (waliyyai) da suke t ãshi daga ƙaburbura suna taimakon
mutãne n dũniya !
Yã danganta da tã ɓewar bõka, rõhãnai suna fit õwa ƙiri -ƙiri a ga ban bõka idan y a
kirãyesu. Hanyõ yin ƙiran rõh ãnai da basu kwantirãgi suna da yawa, amma
kowace hanya ɗaya ne daga cikin wa ɗannan:
Hanyar rantsuwa: Hanyar rantsuwa itace wacce bõka zai zauna ya yi ta kiran
sunayen rõhãnai (kamar sau dubu), yana kiransu yana ƙ õna turãre, y ana cewa: Na
rantse da sunanka (……...), ya kai sarkin Aljanu! Ku amsa mini sabõda
“Salamun ƙaulan min rabbir rahĩm ”, kuyi tawakkali yã kũ masu hidima a
2. Aikin alheri a wurinsu saboda za su samu rĩba daga gareshi (zasu amfana du k da cewa wanda aka
yi wa asirin zai cũtu). Amma aikin da ba na alheri ba, ba su da wata rĩba daga gareshi sai dai su cutar
da wanda akayi wa asirin saboda wata hassada kawai.
54
54
waɗannan sũnaye da wannan ãya mai tsarki, ku sanya soyayyar wãne a cikin
zũciyar wance har ya kasance ba ta iya barci sai ta ganshi… kaza, kaza, kaza!
Hanyar kar ãtun addu’ar kiransu: Hanyar kar ãtun addu’ar kiran rõhãnai ƙ ãri
ne akan hanyar rantsuwa. Bõka zai nemo turãre irin na rõhãnan da yake son ƙira
(uluwwiy ko sufuliy). Turãren ƙiran rõhãne sun ha ɗa da M asɗaki, libãnuz zakari,
Jãwiy, kasbara, duwãwul jinni da sauransu.
Misãlin addu’ar (kiran) rõhãne masu hidima a sũratul Jinni, ana karanta suratul
Jinni ne, duk bayan ãya ɗaya sai a kira s ũnayen rõhãne ayi rantsuwa dasu, ana c ĩ
gaba da ƙ õna turãre har sai anga cinyar mutum t ã fãɗo daga saman ɗãki! Idan
mutum ya tsõrata ya haukace! Idan yaci gaba (da addu’a) sai wata cinyar ta fã ɗo,
da haka sai sassan mutum sun gama kammala sai ya tãshi ya tambayi mai addu’ar
buƙatarsa…
Mai sauƙinta shine aga ɗãkin ya game da haske, a lõkacin da rõhãnen suka iso,
daga nan sai bõka ya rõƙi (taimakon) abinda yake so rõhãnen suyi masa .
Irin wannan hanyar bõkanci, sai wanda ya k ãfirta kwarai. Irin wa ɗannan bõkaye
sũ ke bugan ƙirji suce yanzu -yanzu za su kai mutum lãhira!
➢ (Ance) Wani bõka, idan anje wurinsa, sai ya yi gõri a mutãne yace: Allan
nãku Y ã kãsa kenan kun z õ wurinmu… (Na’ ũzu billãh , wa nastagfiruh! )
Duk wanda yaje wurin bõka ko mai d ũba sai ya
gaskata shi, to ha ƙiƙa ya k ãfirta da abin da Allah
(SWA) Ya sau ƙar ga Annabi Muhammadu (SAW).
Hanyar ajiye ƙulle -ƙulle: hanya ce da ake rub ũtawa rõhãne (da rub ũtunsu)
kwantirãgin da ake so su aikata. Wani lõkaci akan zãna hoton saurayi da budurwa
sun ha ɗa hannu sabõda rũhãne su gãne kwantirãgin sõyayyane. Bayan an rubuta
bayanen kwantirãgi, sai a ha ɗa da wassu ƙulle -ƙulle a ƙulle aje wurin zaman
aljanu a ajiye.
55
55
➢ Wata r ãna mun t ãru a lãyin ɗiban ruwa (a makarantar GSS Azare) , rigimar
wassu ɗãlibai ta kai ga tõno wassu ƙõy ãyen kãza (far ãre guda biyu) a cikin
wani shũri (gidan garã) . A jikin ƙ õyãyen, an rub ũta ãyõyin Alƙur´ãni, an
buɗa kõwace minjãye an rubuta sunan wani da wata.
Tun students suna ts õro ana guduwa, ƙarshe, har aka fasa wa ɗannan
ƙõyãyen. Allah (SWA) Y ã ƙaddara warwarewar wannan sihirin kenan .
Alha mdu lillãhi.
Hanyar rubutun ɗalsami da Hãtimi : Ɗalsami wani rubutu ne marar ma’ana da ban
san me alj anu suke nufi da shi ba. Akan sã mu ɗalsami ne daga wurin bõka zuwa bõka
(passing ɗinsa ake) . Cikin kundin mã luman zaure da yawa akan sãmu asirai waɗanda
rubũtunsu ɗalsami ne bayan hã timai.
Rubũtun ɗalsami a tafin hannu kawai (suka ce) yana iya sauƙar wa mace jini idan ta
gane shi! Ba mãmãki n tãsirinsa idan an tũra mata ta wayar GSM. Innãlillãhi wa innã
ilaihi rãji’un ! Allah Ya kiyaye mu da tsãfi da masu yins a.
ɗalsami
RUBŨTUN RÕHÃNE
(Da wannan rubũtu ake rubũta musu su shiga jikin mutum)
Sihirin ha ɗa sõyayya a jikin kwan kãza.
56
56
➢ Kĩmãnin shekaru ashirin da ɗõriya da suka wuce, wani abõkina malamin zaure
ya fito daga gidan uwar ɗãkinsa. Yana bã ni lãbari, ɗiyarta keson a mata wani
taimako na farin jini da mallake samãri…, kuma tã bãshi lãbãrin wani malami a
garin Zãriya wanda yake musu rub ũtu a jikinsu sabõda…
➢ Na ta ɓa sãmun lãbãrin wani m ãlami da wata m ãta taje neman asiri wurinsa akan
mijinta ya saya mata mõta . Matar kyakkyawa ce kwarai, malamin yace sai an
rubuta ( ɗalsami) an sãdu da ita! Innã lillãhi wa innã i laihi rãji’un. Bayan mijinta
ya saya mata mõta sai ta kãwo masa abõkiyarta akan itama ya tãra da ita sabõda
mijinta ya saya mata mõta.
Hãtimi:
Ban sani ba ko da hanyar da ake kõyon rub ũtun isar da sãƙo ta hanyar ɗalsami, amma
shi Hãtimi ana r ubuta shi ne ta hanyar bugu ( calculations ). Hãtimi yana farawa ne daga
mai gidan dara uku -uku (uku sau uku).
Idan ana so a sanya rub ũtun Bismillah (ko wata sũra guda ta Alƙur´ãni mai girma) a
cikin hãtimi , sai a dũba daga adadin harrufa, a tara harrufa nta (misãli harrufa biyun farko
na bismillah: Ba’un = 2, Sĩnun = 60, 2+60 = 62).
Rubũtun ɗalsami a ji kin wata mata
57
57
Bayan an tãra adadin harrufa an ƙarasa lõgõgin lissafi, kowace darar hãtimi (each box )
za ta samu adadi /alƙalami (number ).
Idan aka gama zuba hãtumi, kowane (l ãyin) gid aje uku (daga sama zuwa ƙasa
(columns )), idan ka tãra za ka samu 15. Haka kowane gidaje daga gefen hagu ko dama
zuwa ɗaya gefen ( Rows ), Jimillar alƙalumans u zai kasance 15. Daga kusurwa zuwa
kusurwa (dungu zuwa dungu ( along diagonals )) idan ka tãr a zaka sa mu goma sha biyar
(15), haka daga ɗaya dungun zuwa ɗayan!
Iya wannan kawai, ana rubuta shi a jikin zõbe a gayawa mutum sũrũtun da zai yi (idan
ya shiga wani hali) don ya samu taimakon aljanu (rõhãne).
Dã za ka sãmu hãtimi mai zubin gidãje hu ɗu-huɗu, sũma adadin lãyi zuwa lã yi
(independent rows and columns ), kusurwa zuwa kusurwa (independent diagonals ) dõle
su baka jimillar alƙaluma dai -dai. Yi amfani da wannan hãtimi na ƙasa ka gani , jimillar
da za ka samu a kowane lãyi shine 34.
خاتم روحان ي
Zõben azurfa an rubuta masa hãtumi
58
58
Bayan an gama fitar da hãtimi, sai a kawo sunã yen rõhane da ake son ba kwantirãge,
(ko ake son su taimaka lõkacin da abu ya ɓãci) a rubuta sunãyensu ta kowane gefe (gefe
huɗu da dungu hu ɗu). Ga misalin wani hã ɗaɗɗen hãtimi da na ɗauko online :
Ka ƙãre mas a kallo! A wannan ha ɗaɗɗen hãtumi na sama, za mu ga mai gidan dar ã uku
sau uku ne. irin alƙaluma (numbers ) da muka zuba (a misalin da ya gabata) sũne a cikin
wannan h ãtumin , kawai an fassara alƙaluman ne (a gefensu) da rubutun aljanu (ƙalamur
rõhãniy), an kuma rubuta sunayen r õhãnen da ake so su taimaka (a ƙ asan alƙaluman).
Kõwane gefe da dungu (kusurwa ko angle )) za ka ga sunan aljani (rõhãni uluwwiy ).
Lãyukan dara -darar kuma, a wannan hatimin, rubutun “Bismilla” ne -(lãyukan baya n
hatumin , daga sama sai ka zãga anticlockwise ). Sai “ ƙauluhu wa lahul mulkul haƙƙu ”.
Idan dã hãtimin asirin sharri ne (na ƙeta), za a rub ũta sunãyen rõh ãne sufuliy ne kuma a
kewaya da Bismillar wãnin hanun agõgõ ( clockwise ).
Bayan hãtimi ya ha ɗu, sai a ha ɗãshi da abin da za’a ha ɗa (sau tãri najasa) sannan a rufa
da fãtar wata dabba (har Jãba ko bõdari ana rufawa da fatarsu) ya zama lãya ko gũru.
Ko akai hãtimin wani wuri a binne (ko a jefa cikin shadda ( masai -toilet ) ko a binne a
cikin kabari) ko magud ãnar ruwa da dai sauransu.
Irin wannan lãya (da sauransu) ita ake ƙira tamĩmatan . Annabi (SAW) ya ce:
من تعلق َتيمة فقد أشرك
Duk wanda ya rataya tamĩmatan (lãya) to yã yi shirka ( Shĩ Mushirikĩ ne)
Haɗaɗɗiyar Lãya
59
59
Wannan bayanai (na ɗalsami da hãtimi) ba ƙaramin ilimi ne da bõka yake himmatuwa
da saninsa ba.
Bayan irin wannan hãtimi, akwai hãtimi irin na shai ɗãnun Yahudãwa ( Jews ) mai
tãrin sirri. Shĩ ma wannan hãtimin buga lissafinsa ake a fitar da tsãfi mai girman gaske.
Shĩ ma irin wannan hãtimi ana rubuta shi a jikin zõbe da kãyan ad on mãtã ( jewellar y),
agõgo, carbi da sauransu, duk don sabõda shai ɗan ya kasance yana t ãre da mutum yana
taimaka masa.
Shi irin wannan h ãtimi na Yahũdãwa, da sirrinsa suke ganin ake iya mallakan dũniya
gaba ɗayanta. Sabõda haka suka sanya shi a jikin tũtarsu da ku ɗinsu da sauran abũbuwan
da bamu sani ba. Ka dũba:
Hãtimin Yahũdawa da yadda suke fitar dashi
Kwã ɗon Sarƙar wuya
Tũtar Isrã’ila (Yahũdãwa)
Dalar Amurka
60
60
To kõ Amurkawa suna tsammãnin wannan tsãfin (na jikin ku ɗinsu) ya
sanya ku ɗinsu yake jãgõrantar ku ɗaɗen dũniya?
61
61
Bermuda Triangle (Dãlar Bãmuda da ke cik in ruwa) matattarar Shai ɗanun dũniya ne da
bã su barin ko tsuntsu ya gifta ta samansu. Nan ne Hedikwatar majal ĩsar ɗinkin d ũniya
ta shaiɗãnu (MASON United Nation Headquaters ).
MASON yana nufin Mystic Ancient Shrine Order Nobles wai Tsangayar Rõhãnai na
ainihi (na dã) masu tanƙwasa kõwa (yabi dõka). Allah ( SWA ) Shi ne Masani.
Kuma kamar wannan ne Muke bayyana ãyõyi, daki -daki, kuma dõmin hanyar
mãsu laifi ta bayyana. (6:55)
Waɗannan hãtumai na Yahũdawa sun maida shi stamp (kan-sarki) da suke sanyawa
akan k ãyansu. Idan ka kwatanta kan -sarki ( stamp ) biyu na sama, ka mayar dasu 3-
dimensi onal (3D Pictures ) zã ka ga sunyi kama da wannan ɗan-itaciya na gefe.
Kan-sarki ko kan shai ɗan?
طَلْعُهَا كَأَنههُ رُءُوسُ الشهيَاطِنيِ
(itãciyar zaƙƙũm) G undarta, kamar dai shi kãnun Shai ɗan ne.
Lalle itãciyar zaƙƙũm, Ita ce abincin mai laifi. (idan an ci) Kamar narkakken
kwalta yanã tafasa a cikin cikunna. Kamar tafasar ruwan zãfi. (44:43 -46)
Allah (SWA) Shi ne Masani .
Who owns the Federal Reserve
Kãnun Shai ɗãnu
رُءُوسُ الشهيَاطِنيِ
62
62
ƙulle-ƙulle
شَر ِ الن هفهاَثَتِ ِفِ الْعُقَدِ Hanyar ƙulle -ƙulle tafi yawa a dukk an ayyukan sihirin cutar da mutãne . Sihirin da
tsĩnanne n Bayahũde Labĩdu ɗan A’asami ya yi wa Manzon Allah (SWA) ya kasance
ƙulle -ƙulle ne. Gãlibi ana ha ɗa sihirin ƙulle -ƙulle da wani abinda ya ta ɓa jikin mutum
(kamar tsumman rigarsa ) wani lõkaci ma ƙasar da mutum ya tãka ake ɗebowa. Sabõda
haka ne ake son mãta suna tãnada gãshinsu da tsummansu na gõge -gõge su ƙõna kãfin
a kai bõla.
3. Yana daga il imin bõkanci, sanin kimiyyar tãsirin yanayi a jikin ɗan-adam l õkacin
haihuwarsa (ilimin Astrology ). Kamar yadda suka ce, wa ɗannan Burujai 12
(masauƙan rãna da wata), ɗabi’arsu tana sh ãfar mutum idan an haifeshi lõkacin da
rãna ke ciki. Mis ãli, idan an haifi J ãriri a lõkacin da rãna take cikin Burujin kunãma
to jariri zai tashi da ɗabi’ar Burujin kun ãma! Shaiɗan zai yãfici jãriri ya masa shaida.
Sũ ko ɗabi’un Burujai guda hu ɗu ne (kõwane burujai uku suna da ɗabi’a guda).
ɗabi’un sune :
a. Nãriy ( ɗabi’ar wut ã)
b. Mã’iy (ɗabĩ’ar Ruwa)
c. Haw ã’iy (ɗabi’ar Iska)
d. Turãbiy (ɗabi’ar Tur ɓãyã)
63
63
Bõkãye da Astrologers suka ce:
• Mutãne masu ɗabĩ’ar wuta (mace ko namiji) sun kasance masu saurin tafasa (saurin
fushi), masu kĩshi, marasa alƙibla amma basu da riƙo (na laifin da aka musu) da
sauransu .
• Mutãne masu ɗabĩ’ar Ruwa (mace ko namiji) , yadda kaga teku haka suke –gã haƙuri
amma in ransu ya ɓaci sai sunci mutum! Suna da nũna sõ yayya, suna da taimako,
kuma b ã’a sanin cikinsu. Da sauransu.
• Mutãne masu ɗabĩ’ar Iska (mace ko namiji) , suna kasancewa kamar masu iska (iska -
iska), sun a da zumũ ɗi da son shiga siyãsa , suna da rãkã ɗi wani lõkaci da suna da
hãlin shirga ƙarya.
• Mutãne masu ɗabĩ’ar tur ɓãya (mace ko namiji) , idan ka samu ɗayansu ka s ãmu
sakwatõtõ , marar kuzãri, mai sauƙin jũyawa sabõda ƙaranci tunã ni.
Ta hanyar sanin wa ɗannan ɗabĩ’u, bõka yana kãfircinsa yadda yake so! Da zarar bõka
yana so ya san ɗabi’ar mutum (wanda ake so a cutar da shi), zai tambayi sunansa da
sunan mahaifinsa da mahaifiyarsa , shikenan an gama! Tuni liss ãfin alƙaluma zai fitar
da ɗabĩ’arsa (Nãri, Ma’iy, Ha wã’iy ko turãbiy).
A wannan z ãmani da muke ciki (21st century ), Yah ũdawa suna da bõkaye ( Astrologers )
a yawancin ma’aikatu. Duk form da za ka cike sai an buƙaci sunan mahaifiyarka
(mothers name , maiden name ) da sauransu. Ta haka ne su ke sãmun sauƙin binci ken
ɗabi’ar mutum (da yi ma sa tsãfi in t a kãma).
Har ila yau, masu binciken ɗabĩ’un ɗan-adam sun ã nan da yawa a filin sãda zumunta
(Mũsa mman facebook) . Da zãrar ka yarda , sai su ɗebi bayanenka (sũna, shekarar
haihuwa ds.) su buga liss ãfin alƙaluma su fitar maka da bay ãne (misali) cewa za ka
zauna da mace ɗaya ne a r ãyuwarka , Za ka rãyu tsawon shekar ũ kaza, gasunan dai muna
ganin irinsu ko da yaushe .
Kalandar tsa yuwar Burujan shekarar 2016
64
64
Dalilin irin wannan hanyar binciken ɗabĩ’a masu sana’a ( Mũsa mman masu ɗõrin
karaya) kan tambayi sunan wanda ya karye da sunan iy ãyensa, sai su tũra aljanu suje su
ɗõrashi (alhãli yana wani garin) !
Ta irin wannan (sanin ɗabĩ’ũ) bõka ke sanin yanda zai binne sihiri n da ya yi wa mutum.
Mutum mai ɗabĩ’ar ruw ã akan kai tsãfin da aka yi masa magudanar ruwa. Manzon Allah
(SAW) yãfi kõwa haƙuri, sai aka jefa ƙulle -ƙullen da aka yi masa cikin rĩjiya,
Hasbunallãhu wa ni’imal Wakĩl!
Kuma kamar wannan ne Muke bayyana ãyõyi, daki -daki, kuma dõmin hanyar
mãsu laifi ta bayyana. (6:55)
Wani lõkaci mutum Nãriy (ga ɗabĩ’a) akan ƙ õna sihiri da aka yi masa bayan an rub ũta
akan allon ƙarfe. Innãlillãhi wa innã ilaihi rãji’un!
4. Yana daga cikin ilimin bõkanci, sanin yaudara da annamĩmanci. Bõkaye suna
yaudarar masu zuwa wurinsu da cewa sun san “ Ismul lãhil -A’azam”, Shai ɗanu suna
jin ts õronsu, kuma da shi suke rõƙon Allah.
Yãwo da annamĩmanci yana daga cikin sihiri! Bõkaye sukan kware wajen
annamimanci , suna da mataimaka da ake ƙira ƴan -kõro masu taimaka musu wajen
yãwo da annamimanci da haifar da gãba a tsakanin al’umma.
➢ (Ance) Wani bõka ya zo wajen wani mutum (da ya sani) yace: matarka t ã
zo ayi mata aiki ka mutu. Sabõda amãnarmu da kai, nã dai b ã ta ƙasa ta
zuba maka ka ɗan a cikin abinci, amma kar ka fa ɗa mata. Ƙarshe n lãbãrin,
ashe Allah (SWA) Ya hukunta ƙ ãrewar ajalin mijin kwana ka ɗan bayan
annam ĩmancin bõka a tsakaninsa da matarsa.
Kaɗan daga cikin (ilimin) abubuwa da bõka ke amfani da su kenan wajen tafiyar da
sanã’arsa. Ina ganin wa ɗannan ka ɗai yã isa yasa mai karãtu ya fahimci nau’i kan sihiri
kamar haka :
ALLON ƙARFE
65
65
FASALI:
3.2 NAU’IKAN SIHIRI N DA BÕKA KAN YI :
1. Sihiru Tafriƙ : Sihirin shiga tsak ãnin mutãne (a raba su) a haifar musu da
ƙiyayya . Misali: Raba mata da miji.
2. Sihiru Muhibba: Sihirin s õyayya, sanya wani (ko wata) sõyayyar d õle.
3. Sihiru Takyil: Sihirin rufa’ido –mutum yana ganin abu a sã ɓãnin haƙiƙanin
yanda ya sanshi. Misali: Sanya kwallin tsãfi (na idonki idõna) wanda zai sa aga
wanda ya sa nya ya zama kyaykyawa.
4. Sihiru Junun: Sihirin haukatarwa. A fitar da mutum a hankalinsa na wani lõkaci
ko na din -din-din. Kõ ayi ma sa kurciya ya shiga dãji ko ya bar garin cikin hauka.
5. Sihiru Khumul: Sihirin ɗaure mutum ya kasa zuwa kõ’ina, ya kõma baya iya
magana da kõwa kamar ta ɓaɓɓe, kullum yana cikin cĩwon ga ɓɓai. Ana yin irin
wannan sihirin a mahaukaci mai dũka wai don a ɗaure ma sa hannaye ya dena
dũka. Ko misãlin kafe matar aure mayãwaciya. Da sauransu.
6. Sihiru Hawãtif : Sihirin da za a shagaltar d a mutum , a sã shi rashin nutsuwa da
tsõro, ya ri nƙa jin kamar wani yana kir ansa, ya rinƙa mafarkan dõdanni da
sauransu. Wani lõkaci har mai wannan rashin lãfiyar kanga abin tsoro ido da ido.
7. Sihiru Marad : Likitanci da Sihiri, mai amfani da sihiri wajen yin maganin wata
cũta (a kansa ko a mutãne ). Misãli: kãciyar sã wando, ɗõrin nesa, da sauransu.
وإنك َلتباِل بعد َنول ... أسحر كان طب ك أمجنوَن
8. Sihiru Nazif kõ istihãda : Sihirin da zai sa mace tanã wuce al’adarta.
9. Sihiru Ta’a ɗil: Sihirin sanya mace son namiji ɗaya tak, sauran maza (har)
mahaifinta su zama b ã ta ƙaunarsu. Ko mallake miji da sanya shi jin haushin
mãtan dũniya gaba ɗaya (har m ahaifiyarsa).
10. Sihiru Raba ɗ: Sihirin sauƙar wa mace jini (a lõkacin da rãnakun al’ada basu zo
ba) don kar mijinta ya s ãmu d ãmar sãduwa da ita.
Bã sai bõka ba! Duk wanda ya aikata ɗayan wa ɗannan ko yasa aka
aikata masa to ya yi tsãfi kenan kuma ya zama mush iriki sannan idan
ya mutu bai tuba ba za ya shiga wuta. Allah (SWA) Ya shirya r da mu i
zuwa hanyar ts ĩrã.
""من ت َعَل ق َتَِيمَة فَل أمت هللا له، ومن ت َعَلهق وَدَعَة؛ فَل وَدَعَ هللا له
Duk wanda ya rãtaya lãya , Allah ba Zai cika masa (bũrinsa) ba. Duk wan da ya
rãtaya konso ( shell ), Allah ba Zai dũbe shi ba. (Hadisi rawaitowar Ahmad da Hãkim)
66
66
3.2.1 Hanyar gãne wanda aka yi masa sihiri da nau’insa.
Akwai ab ũbuwan da za’a lũra da su a g ãne cewa mutum yana ɗauke da sihiri. Wani
lõkaci shi kansa mutum kan iya gãnewa yana ɗauke da sihiri.
1. Hanya mafi sauƙi da za’a iya fahimtar mai ɗauke da sihiri sai in ya kasance mai
ƙõƙarin addini kuma sai aka lũra yana yawan wasi -wasi a cikin sha’anin ibadar
tasa (ba kamar yanda aka san shi ba), ya zama kamar mai ta ɓin hankali . Duk da
haka ba za a tabbatar da cewa sihiri bane, sai a gwada ruƙiyya. Fahimtar sihiri a
tare da mai shan ƙwãya ba abu ne mai sauƙi ba.
2. Malamai sunce mutum na iya fahimtar m ãtarsa tayi masa sihiri a lõkacin da ya
ga baya iya tsallaka karã idan t ã ajiye, kuma ya fahimci tana cika bãki (da alfahari)
a game da ĩkonta a kansa.
3. Yawan mafarkai m ãsu ban tsõ ro, da jin ƙiran suna ba tare da sanin ta ina ne ba ,
yana sa mutum ya fahimci cewa yana tare da wani aljani da aka tũrõ masa.
4. Tabbas jini n Istihãdha kam, i dan b ã a dalilin tsinkewar wata jijiya ba , akwai
tãsirin shai ɗan a tattare da zuwansa. Mun samu wannan bayani daga Manzon
Allah (SWA), yã ce:
فَإَِّنهَا هُوَ دَاء عَرَضَ أَوْ رَكْضَة مِنَ الشهيْطَانِ أَوْ عِرْق ان ْقَطَعَ
Sabõda haka daga mace t ã ga jin in istihãdha , yana da kyau ta fãra neman tsari
daga shai ɗãnu bayan ta karanta Innãlillãhi wa innã ilaihi rãji’un.
Bayãnin warware sihiri ta hanyõyin ruƙiyya (tõfi) a rũwan magarya da sauransu
ya gabãta a bãbi na biyu. Allah (SWA) Ya taimaka.
... قُلْ أَف َرَأَي ْتُمْ مَا تَدْعُونَ مِنْ دُونِ اّلِلهِ إِنْ أَرَادَّنَِ اّلِلهُ بِضُر ٍ هَلْ هُنه كَاشِفَاتُ ضُر ِهِ أَوْ
أَرَادَّنِ بِرَحَْةٍ هَلْ هُنه ِمُْسِكَاتُ رَحَْتِهِ قُلْ حَسْبَِ اّلِلهُ عَلَيْهِ ي َت َوَكهلُ الْمُت َوَك ِلُونَ
"Ashe, to, kun gani abin da kuke kira, wa ɗanda suke wanin Allah ne,
idan Allah Ya nufe ni da wata c ũta, shin s ũ abũbuwan nan m ãsu
kuranye, cutarsa ne? K õ kuma Ya nufe ni da wata rahama, shin, su
abũbuwan nan m ãsu kãme rahamarSa ne?" Ka ce: "Mai is ãta Allah ne,
gare Shi m ãsu tawakk ali ke dõgara."
67
67
BÃBI NA HUƊU
MAITA.
Malamai suna cewa ba bu wani abu da aka sani maita a musulunci, fãce kambun baka
(makamancin maita ). Idan munyi la’akari da abubuwan da ake dangantã su da maita, z ã
mu iya kasa Maita gida uku:
1. Maitar cin wani abu da bã ’a cinsa (ko sha) : A wurin bahaushe , ainihin mã ye
shi ne mai kãma kurwar mutum (ta hanyar tsãfi) ya cinye sai mutum ya mutu.
Wann an bãbu tabbacin hakan na iya fã ruwa , amma sananne ne ana kisan mutã ne
ta hanyar tsãfi (idan an dãce da ƙaddara) .
Ba sãbo n abu bane a wannan zãmani, ana sãmun mutãne masu cin naman mutãne .
Masu shan jinin mutãne ko cin namansu ɗanye ko gas asse (a zãhiri ba ta hanyar
tsãfi ba) s ũ bahaushe yake nufi da mã yu (na asali). Hakan yana f ãruwa (gãlibi) a
garũrũwan arnan da ke cikin d uwãtsu da birãne masu yawan ƙungiyõ yin asĩri.
Ko a zãmanin mãguzancin hausãwa, ance, mutã nen fãda kanyi ferfesun kutãre su
cinye sabõda su zamõ masu taurin rãyi. Ka mã ajiye bayanin fatalwun Vampires ,
“A yawancin manyan bir ãnen dũniya akwai wasu mutãne da suka
kunshi ma'aikata a kusan kowane fanni k ãmã daga asibiti da
kamfan õni da otal -otal, wa ɗanda suke shan jinin mutãne akai
akai. Me ya sa suke sha? ”
BBC ta bincika, ta wallafa ran 29 Junairu 2016 . Zaka iya dũbã wa idan ka lãtsa
wannan akalar (hyperlink ).
A al’ãdar bahaushe, wanda ke iya cin k õwane irin nãma ɗanyensa, ko wani abu
da hausawa basa ci, ana misalt ãshi da mãye (a ce “ sai ka ce mã ye!”)
68
68
2. Maitar Jãruntaka: Maitar jã runtaka ana danganta ta ne ga duk wanda ya yi fice
ko yake da ƙw ãzo akan wani al’amari. Ko wajen ilimi bahaushe kance wãne mãye
ne. Da yawan mutãne sukan yi t sãfi a kansu don su kasance h atsabib ai (mãyu)
anã jin ts õronsu .
Tsana nin sõyayya ma, bahaushe kan danganta ta da maita, sai kaji yã ce: wãne
mãyen m ãtã ne! (wato yana buƙ ãtar aure ko ana son danga nta shi da neman mãta).
Wãne mãyen sh an kunu ne yana nuna yawan shansa ga kunu (ko rashin sake
fuska) .
3. Maitar Idõ ko Bãki : Irin wa nnan maita ita ake kira “ Ainun ” ma’ana: Id ãnu. Irin
wannan maita ba luggar (nahawun) bahaushe ba ce, ba kuma ta hanyar tsãfi ake
sãmunta ba. Mai tar idã nu baiwa ce (ta ƙaddara) da wassu ke ɗauke da ita. Idan
mai maitar i do yaga wani abu da ya (b ãshi sha’awa ) sai ya yaba kyawun wannan
abun, to (da ikon Allah) sai wannan abun ya lãlãce. Idan kyawun mutum ya yaba
to (da ikon Allah) sai wannan mutumin ya k amu da rashin lãfiya. Sabõda yabawan
bãkinsa ne ke haifar da cũ tarwa (in Allah Ya so), hausawa kan ce masa m ai
kambun baka.
Dukkan masu cũtarw a da kambun baka m ahassada ne, sũne marasa taya (mutum)
murna da kalamai irin “Kai! Allah Yayi albarka, Bãrakallãhu fih!” da sauransu.
Amma ba dukkan mahassada ne mãyũ (masu maitar ido) ba.
Maita irin ta mahassada gaskiya ce (akwai ta), Manzon Allah (S AW) Ya tabbatar
da kwai, yace: Maitar ido gakiya ce! Shai ɗan da hassadar ɗan-Adam suke bijirõ
da ita. kuma ya c e: Dã akwai wani abu da zai gabã ci ƙaddara, dã maita ta gabãta.
وأخرج مسلم وأحد والَتمذي وصححه عن ابن عباس رضي هللا عنهما عن النب صلي هللا
عليه وسلم قال: العني حق ولو كان ش يء سابق القدر لسبقته العني، واذا استغسلتم فاغسلوا
Dã maita na iya kashe mutum kafi n kwanansa ya ƙãre dã tã kashe! Manzon Allah (S AW)
ya ce: Mafi yawan mutãne n al’ummata da suke mutuwa –idan All ah Ya ƙaddara
ƙarar kwanansu – (suna mutuwa ne) da (jinyar) kurwa –sanadiyyar mãyu .
Shi mai hassada wanda yake da maita, maitarsa kamar wassu kibiyõyi ne da suke fita
daga zũcciyarsa (a lõkacin da hassadarsa ta mõtsa), sai su nufi wajen wan da ake ma sa
hassada . Idan Allah Ya ƙaddara kibiyõyin (maitar) mai hassada ba su kai ga mutum ba,
to ya yi sa’ a. Idan ko suka kai gareshi, wannan sai yanda Ubangiji (Allah (SWA)) Ya
hukunta.
69
69
➢ Tafsirin ƙur ɗabĩ ya kawo (a tafsirin 68:51) , an ce cikin Banũ Asad akwai masu
maitar idanu. Ya kasance mãyun Banũ Asad suna ji da maita, har idan suka ga
wata ƙosassar S ãniya ko Rãƙuma ta gifta ta gabansu sukan ƙ ura mata ido sannan
su ƙira baiwarsu (macen bãwa) suce: ga dirhami ki ɗauko masaki ki bibiyi
wannan sãniyar (k o rãƙumar), idan tã fã ɗi (an yanka) sai ki siyõ mana nãmanta!
Da ikon Allah sai aga wannan saniyar tã tuntsire (ta fã ɗi) tana neman mutuwa
har sai an yanka ta.
Kalbiyyu ya ce: akwai wani mutum daga cikin lãrabawa da yake kãmewa daga
cin abinci tsawon kwana biyu ko uku, sai maitar bãkinsa ta cika da guba. Idan
rãƙumi ko tunkiya az õ giftawa sai yace: Kai! Yau kam ban gani ba a kyãwu
kamar irin wannan rãƙumi (ko tunkiya) , sai kaga dabb õbi ka ɗan ne (da ikon
Allah ) suke tsĩra.
Sai kafiran Makka suka nemi wannan mutumi akan ya yi amfani da maitar
bãkinsa ya kashe Manzon Allah (SAW )! A lõkacin da Annabi (SAW) ya zo
wucew a, sai wannan mutumin ya rera wã ƙa kamar haka:
قَدْ كَانَ ق َوْمُكَ َيَْسِبُونَكَ سَي ِدًا ... وَإِخَالُ أَنهكَ سَي ِد مَعْيُونُ
Haƙiƙa ya kasanc e mutãne nka nã tsammaninka S hũgaba,
Dĩbã (a yau) S hũgaba kake kamamme (da mãitar idaniya) .
Sai Allah (SWA), da kiyayewarSa, ya kãre ManzonSa (SAW), kuma Ya sauƙar da
lãbãrin:
وَإِنْ يَكَادُ الهذِينَ كَفَرُوا لَي ُزْلِقُونَكَ ِبَِبْصَارِهِمْ لَمها َسَِعُوا الذ ِكْرَ وَي َقُولُونَ إِنههُ لَمَجْنُون
Kuma lalle, ne wa ɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da
kallonsu (na maitar id ãnu), a lõkacin da suke jin karãtun Alƙur´ãni, kuma sunã
cewa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!" (68:51)
➢ Sahalu bn Hanif (R.A) kyakkyawan balãrabe ne –fari mai kyan fasali! Wata
rãna sun fita zuwa miƙãtin Juh’fa, sai ya shiga wanka. Yana cikin wanka sai
Ãmir ɗan Rabĩ’ah ya hango jikinsa (Jãjur), sai yace: (kai!) ban gani ba kamar
wannan rãna… jiki irin wannan? Shi kenan sai Sahalu yai farf ãɗiya ya fã ɗi.
Sai (sahabbai) suka zo ga Manzon Allah (S AW) suka ce: Yã Ras ũlullãh! Shin
kana da wani abu ga Sahal, wallãhi ko kãyinsa ba ya iya ɗagawa (sabõda jinya).
Manzon Allah (S AW) yace: Shin akwai wani da kuke zargi (da ha nnu) a kans a?
Sahabbai suka ce: Ãmir ɗan Rabĩ’atu ya gane shi (a lõkacin yana wanka)! Sai
Manzon Allah (SWA) ya ƙira Ãmir, ya nuna masa rashin jin d ãɗinsa, yace :
70
70
Akan me ɗayanku zai kashe ɗan’uwansa? Idan kaga abinda ya b ãka
mãmãki ka (kasa) yi masa san -barka ?
Sannan sai Manzon Allah (S AW) yace masa: Wanke masa (sabõ da ya samu
mãgani). Sai (Ãmir) ya wanke:
1. fuskarsa , da
2. Hannãyensa , da
3. Gwuiwar hannunsa (guda biyu), da
4. Gwuiwar ƙafarsa (biyu), da
5. Gefen (tãfin) ƙafõfinsa, da
6. Yankin tufarsa ta wurin da t ake shafar jikin sa.
Dukkansu ya wanke a cikin wata ƙwarya ( container ), sannan sai aka kwãra
wannan ruwan a kã yin Sahalu –wani mutum yana kwara masa a k ãyinsa da
gadon bayansa – sannan aka j ũya ta gabansa, … sai gã Sahal, a cikin mutãne ,
yana fara’a b ãbu wata sauran cũta a tare da shi.
➢ Sa’adu bn Abiy Waƙƙas (R.A) ya fita a cikin sutura biyu, a lõkacin yana
gwamnan Irãƙi, sai wata mãta ta ƙura masa idãnu tace: Lalle wannan gwamna
nãku … kaza kaza , ta yabeshi.
A lõkacin da ya kõma masauƙinsa sai ya fã ɗi (ba lãfiya). Sai maganar wannan
matar ya fã ɗõ masa a zũciya . Nan da nan ya aika, matar tazo ta wanke masa
gaɓɓan da ake wankewa yayi wanka da ruwan, sai Allah (SWA) Ya bashi
lafiya.
sabõda haka malamai suka ce i dan an san cewar mutum y ã kãmu da cũta ta dalilin mai
maitar ido kuma an san mutumin (ko ana zarginsa) to, sai a nemi mutumin (mai maitar
idon) ya taimaka ya wanke ma marar lafiyan. A kãwo masa ruwa a masaki (likidi ri), ya
tsõma hannayensa, ya kurkure bã kinsa ya zuba a cikin ƙwaryar, sanna n ya wanke
fuskarsa. Ya sanya tã finsa na hagu ya kamfato ruwa ya wanke gwuiwar hannunsa na
dama , ya maimaita haka da ɗaya hannun ya wanke gwuiwar hannun hagu, sannan ya
wanke tufarsa duka da ruwan masakin, ƙarshe sai a yi amfani da ruwan a kwara wa
marar lafiyan a kãyinsa da bãyansa sau ɗaya, zai samu sauƙi da iznin Ubangiji.
Wassu suka ce an ã karanta masa ayar da ta gabata (ayar 68:51) a matsayin ruƙiyya .
4.1 R igãkafi don ku ɓuta daga kãmun mãyu.
Anan, rigakafi yana nufin hanyoyin da za’a bi, ba ta hanyar shan wani magani ba , a
nemi tsarin Allah (SWA) daga sharrin Mãyu (mahassada). Hanyoyin sun rabu zuwa
gida uku; Hanyar kiyayewar ma’ãmala da kuma hanyar karãtun addu’oi da lũra da yara .
71
71
1. Kiyayewar m u’ãmala domin neman tsari da ga mãyu.
Mai karatu zai yi mãmãki n kasancewar yayi mu’amala da mã yu, amma hakan ba
zai b ãshi mãmãki ba idan ya yarda cewa yana mu’ ãmala da mahassada .
A cikin mahassada ne ake samun mãyu amma ba dukkan mai
hassada ne mãye ba!
Tabbas cikin wa ɗanda muke mu’ ãmala dasu a kasuwa, siyasa, aikin gwamnati,
makarantu da sauransu akwai mahassada da bã za mu iya saninsu ba. Ya kamata
mu kiyaye mu’ ãmalarmu dasu sabõda Allah Ya kiyayemu daga hassadarsu da
mãitar wassun su. Za mu kiyaye kamar haka:
a. Sanya tufãfi na mutunci tãre da shigar musulunci: Ya kamata mu kiyaye
irin kayan da za muke shiga cikin jama’a dasu. Kayan su kasance wa ɗanda za
su rufe mana jiki Mũsa mman daga cibiya zuwa gwuiw õyi. Jikin mutum ta ciki
(daga ƙirji zuwa gwuiw õyi) yãfi launin fãta mai kyau da kyãwun gani
(Mũsa mman jikin mace)! Mun dai ji lãbãrin Sahabin nan Sa halu (R.A) .
A ɗaya hanun, kõda gãwa ce ba’a son aga wani aibi a jikinta a bayyana
lãbãrinsa , to menene tsammaninka idan mai hassada (mãye wanda baya sonka)
ya hangi wani aibi daga jikinka? Ai dole sai yayi magana!
Sabõda haka, mãt a ku kiyã ye! Ko gidan bik i, ko makarantu, ko kasuwanni,
kai harma cikin samã ri ana iya s ãmun mai maitar ido (ba lalle a gãne tãsirin
maitarsa ba) .
Kuma ka ce wa mũminai mãta su runtse daga gannansu, kuma su tsare
farjõjinsu kuma kada su bayyana ƙawarsu (kwalliyarsu) fãce abin da y a
bayyana daga gare ta, kuma su dõka da mayãfansu a kan wuyan
rigunansu, kuma kada su nũna ƙawarsu (kwalliyarsu) fãce ga mazansu
ko ubanninsu ko ubannin mazansu, ko ɗiyansu, ko ɗiyan mazansu, ko
´yan´uwansu, ko ɗiyan ´yan´uwansu mãtã, kõ mãtan ƙungiyarsu, ko abin
da hannãyensu na dãma suka mallaka, ko mabiya wasun mãsu bukãtar
mãta daga maza, kõ jãrirai wa ɗanda bã su tsinkãya a kan al´aurar mãtã.
Kuma kada su yi dũka da ƙafãfunsu dõmin a san abin da suke ɓõyewa
daga ƙawarsu. Kuma ku tũba zuwa ga Allah gabã ɗaya, yã ku mũminai!
Tsammãninku, ku sãmi babban rabo . (24:31)
Dukkan wa ɗannan idan an kiyayesu, za a ku ɓuta daga barazanar mãyu in
Allah (SWA) Ya yarda.
➢ Daga Anas bn Malik (R.A): Annabi Yãƙũbu (A.S) ya yi tun ãnin sharrin
kallo irin na mahassada (mãyu) ida n ya kasance ƴaƴan sa za su shiga garin
Misra ta ƙõ fa guda (t ãre) sai yace musu:
72
72
… "Yã ɗiyana! Kada ku shiga ta ƙõfa guda, ku shiga ta ƙõfõfi dabam -
dabam, kuma bã na wadãtar muku kõme daga Allah. Bãbu hukunci
fãce daga Allah, a gareShi na dõgara, kuma a ga reShi mãsu dõgara sai
su dõgara." (suratu Yusuf)
b. Taƙaita wãsanni masu jiyar da mutum girman kai. Ta hanyar wasanni ,
mutãne suna samun d ãmar yabawa mutum da zugashi yadda suke so. Idan
wanda ake kambamã wa da yaba kwalliyarsa bai dace ba, kibiyõyin hassada
(maita) dake fitõwa daga bãkin masõyin nasa (da ikon Allah) sai su kaishi ga
wahala.
c. Kiyãyewa a lõkacin cin abinci: Yana da kyã wu mutum ya kiyaye a lõkacin
da yake cin abinci, idan yaga wani ya ƙura masa ido (kõ da almã jiri ne) tõ
yasan cewa wassu maganganu kan iya biyo baya.
Bai kamata mutum ya riƙa yãgan naman kãza yana ci a gaban almãjiran da
suka kwãna uku da yunwa ba. Yana da kyau mutum ya shiga daga ciki idan
zai ci abinci.
2. Addu’oin neman tsari da ga maitar Mãyu (Mahassada) .
Duk wanda ya nemi tsari da mahassada to ya nemi tsari da mãyu gaba ɗayansu!
Cikin addu’ar da Mala’ika Jibrĩlu ke yiwa Annabi (SAW), idan ya s ãmu rashin
kuzã ri, har da nema masa tsari da mahassada da mãyu. Yakan ce:
بسم هللا ابريك من كل داء يشفيك من شر كل ذي عني ومن شر كل حاسد إ ذا حسد
Da sũnan Allah ina barrantar da kai daga dukkan cũta . (Allah) Yana kiyayeka
(Ya warkar da kai ) daga sharrin dukkan mai maitar ido, kuma daga sh arrin
dukkan mai hassada idan yã yi hassada.
3. Lũra da y ãra: Lũra da yara shi ne yi musu rigãkafi daga sharri n mahassada da
mãyu. Annabi (SAW) ya kasance yana yima Hassan da Hussaini (R.A) addu’ar
rigãkafin masu cutarwa.
عَنِ ابْنِ عَبهاسٍ رَضِيَ اّلِلهُ عَن ْهُمَا، قَالَ : كَانَ النهبُِّ صَلهى اّلِلهُ عَلَيْهِ وَسَلهمَ ي ُعَو ِذُ اْلَْسَنَ
وَاْلُْ سَنيَْ رَضِيَ اّلِلهُ عَن ْهُمَا: أ عِيذُكُمَ ا بِكَلِمَاتِ هللاِ التهامهةِ ، مِنْ كُل ِ شَيْطَانٍ وَهَامهةٍ ، وَمَنْ
كُل ِ عَنيٍْ َلمهةٍ ُثُه ي َقُولُ صَ لهى اّلِلهُ عَلَيْهِ وَسَلهمَ : كَانَ أَبُوكُمْ ي ُعَو ِذُ ِبِِمَا إَِسَْاعِيلَ وَإِسْحَاقَ
عَلَيْهِمَا السهَلمُ .
73
73
Da cikakkun kalmõmin Allah, Ina nema muku tsari daga dukkan shai ɗani da
mũgu kuma daga dukkan maitar ido –mũgun gani.
A lõkacin da yãro zai tafi makaranta, yana da kyau a karanta masa irin wannan addu’a:
أعِيذُك بِكَلِمَاتِ هللاِ التهامهةِ ، مِنْ كُل ِ شَيْطَانٍ وَهَامهةٍ ، وَمَنْ كُل ِ عَنيٍْ َلمهةٍ
Ko a karanta masa wata addu’a da ta sauwaƙa, kõ dã da hausa ne: Allah (SWA) Ya
dawõ da kai lãfiya ya rabaka da sharrin mahassada da ƴan sã ido (sã’id ãwa). Kar kiyi
mãmãki , yaron da zai tafi makaranta yãfi buƙatar addu’a fiye da mijin da zai tafi
kasuwa! Ance sabõda:
a. Rashin wãyon yãro da sanin yanda zai kiyaye kansa ta hanyar addu’a.
b. Kũtsawarsu cikin kowane irin mutãne ba tare da jin ts õro ko addu’a ba.
c. Ana musu fa ɗa da munãnan kalãmai kamar ace: shaƙiyyi, d õlo, mai ƙiriniya, mai
ƙãton kai, Jãki, wãwã, da sauransu .
d. Malamai kan yabesu; Akwai ƙõƙari, Good boy , gentle , fine boy da sauransu.
e. Tsãwa da malamai kanyi wa yãra har su fita a cikin ha yyacinsu.
Dukkan wa ɗannan, idan ƙaddara ta riga fãtã, suna sa yãro ya kamu da sharrin mai maitar
ido (mai kambun baka) kasancewar ba lalle mutum ya sani yana da maitar ido ba. Za a
iya fahimtar yãro ya samu matsala (an cũtar dashi da maita) idan an lura:
a. Dã yana da ƙõƙari kuma daga baya ya zama jãki (marar ƙõƙari) !
b. Yãro yana tsõron zuwa makaran ta ainun da gaske, alhãli dã yana zumũ ɗin tafiya.
c. Wani laulayi da yãro kan dawo dashi daga makaranta, da sauransu.
4.2 Kuɓuta daga sharrin mãyu.
Idan Allah (SWA) Ya sa wani tsãfin mãyu (ƴan ƙungiyar asiri ( cultism )) bai yi tãsiri
akan mutum ba, zai iya ku ɓuta daga sharrinsu (in sha Allahu) :
1. Ta hanyar karatun addu’oin neman tsari (safe da maraice).
2. Kuma mutum ya kasance y a nesanta kansa da shiga wani kã suwanci na sirri da
ake tsammanin samun arziƙi cikin gaggawa.
3. Idan har (yã kasance) an sãmu wani mãye (ma tsãfi) yã mayar da wani mutum
dõya ko an sãmeshi yana farfa ɗiya, ruƙiyya ce abin da ya dace.
4. Mutumin da aka tabbatar rashin lafiyarsa ta dalilin kamun mai kambun baka ce
(maitar ido) , za a wanke masa ga ɓɓan mãyen sabõda ya samu m ãgani.
5. Idan mutum yaji dugu -dugu, kamar wani abu yana yãwo a cikin jikinsa, sai ya
maida h ankali wajen yima kansa ruƙiyya.
74
74
6. Idan yãro ya k amu da cutarwan mai maitar ido (gãlibi kõ magana baya iya yi) ,
kuma ba a san mãyen ba, Annabi (SAW) ya ce sai a sãmu (dag a ƴan gidansu)
wanda yafi son yãron ya wanke masa ga ɓɓai a wankeshi. (ha ka nan babba ma
idan ba’a san mayen ba!).
7. Sai a karanta Suratul Fãtiha, Ã yatul kursiyyu, Falaƙi da Nãsi, dukkansu ƙafa
bakwai -bakwai, ana karant awa ana tõ fa masa a jikinsa har sai Alla h (SWA) Ya
bãshi lafiya. Idan jikinsa akwai zazza ɓi mai zãfi a yawaita wankansa da ruwan
sanyi (wanda idan an zuba masa ba zai zãbura ba). Wanka sau uku, biyar, bakwai!
Allah (SWA) Ya sauwaƙa.
8. Ana yima mutum in da ya kãmu da cũtarwar mai maitar ido addu’a d a ɗayan :
١ اللهم وِل الكلمات والدعات الستجبات عافه أعني اإلنس وأنفس اْلن
٢ أعيذك بكلمات هللا التما مة من كل شيطان ومهة وكل عني َل مة
٣ أعيذك بكلمات هللا التما ت اليت َل جياوز هن بر وَل فاجر من شر ما خلق وبر أو ذر ومن
شر ما ينزل من السماء ومن شر ما يعرج فيها ومن شر ما خيرج من اْلرض ومن شر ما
يكمن فيها ومن شر فنت الليل والنهار ومن شر كل طارق إَل طارق يطرق خبْي َي رحان
٤. بسم هللا أر قيك من كل شر يؤذيك ومن ك ل نفس وعني كل حاسد هللا يشفي ك
٥ اللهم رب الناس البأس واشف أنت الشاِف َلشفاء إَلشفاؤك َليغادر سقما
٦ اللهم اذهب حر العني وبردها ووصبها
Kowacce aka z ãɓa zã a karanta sau bakwai ( 7). Yãro ana karantawa a tofa a tãfukan
hannu sai a shãfe masa jiki.
9. Mutumin da ya kãmu da cũtarwar mai maitar ido, ana iy a shã fe jikinsa da “man -
zaitun” wanda aka tõfa a cikinsa addu’oin (ɗaya daga waɗannan na sama) ruƙiyya
da Fã tiha, Kursiyyu, Falaƙi da Nãsi.
75
75
BÃBI NA BIYAR .
HALASTACCEN SIHIRI, BÕKANCI DA MAITA.
5.1 Halastacciyar mait a.
A wannan karon bari mu fãra da maita. Duk irin nau’ikan maitar da mukayi bayani,
guda ɗaya ta halasta a ta ɓa, amma sai a lõkacin da aka shiga wani hali na ƙaƙa -nikayi .
Allah (SWA) Yace:
Kawai abin da Ya haramta a kanku, mũshe da Jini da nãman alade da a bin da aka
kurũrũta game da shi ga wanin Allah. To, wanda aka matsã, wanin ɗan tãwãye,
kuma banda mai zãlunci, to bãbu laifi a kansa. Lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai
jin ƙai. (2:173)
Kã ga anan mũshe da shan jini da naman alade harãmun ne. Amma idan mutu m ya
kasance yã shiga wani mawuyacin hãli…
Allah (SWA) Yace:
…To, wanda aka sanya wa lar ũra a cikin yunwa mai tsanani, bã yana mai karkata
zuwa ga wani zunubi ba, to, lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
Kã ga anan maitar cin mũshe da shan jini y a halasta, matuƙar an shiga la rũra mai
tsananin gaske. Amma shan jini ( Mũsa mman na mutum) sabõda neman mã gani b a ya
daga cikin larũra sabõda bai halasta ayi m ãgani da najasa ba.
Sannan cin mũshe biyu da cin daskararren jini guda biyu ba laifi bane ko da ba w ata
larũra! Annabi (SAW) yace: An halasta mana Matattu biyu da Jinnai biyu. Amma
matattu biyu sune Fãrã ( grasshopper ) da kĩfi. Kuma amma jinnai biyu sune Hanta
(liver) da Saifa ( spleen ). (Hadisi Da’ĩfi)
➢ A lõkacin da muke yãra, idan ance ana cin fãri a gari n Haɗeja sai muce musu mãyu!
Ban san yaya akai ba cikin ƴan shekarunnan sai gãshi, a garin Azare, ana yãwo da
fãri na sayarwa bãro -bãro. Fãrin daga Maiduguri ne , ko daga Ha ɗeja? Allah Shi ne
Masani! Ni dai ba zanci fãra ba!
Amma kã ga taran jinin rãgon da aka yanka, ko cin nãman ɓera da gafiya da duk wani
mai fĩƙa, da tsuntsaye masu kõfato irin su mikiya da angulu…, cinsu sai mãyen asali
(na kwarai).
5.2 Halastaccen sihiri .
Halastaccen sihiri ba ana yinsa don a cutar da wani bane. An ambace shi da sunan sihir i
ne sabõda ya dda yake karkato da mutum (ko mutãne ), ya mantar dasu baƙin ciki, ya
sanya musu farin ciki har su aikata wani abu ba tare da ainihin suna sani ba.
Annabi (SAW) yace:
76
76
إِنه مِنَ الْب َيَانِ لَسِحْرًا، أَوْ إِنه ب َعْضَ الْب َيَانِ لَسِحْر
Lalle cikin iya magana akwai sihiri! Ko lalle sãshen bayãni tabbas nã da sihiri (na
ɗaukar hankali).
Bayã ni anan shi ne fasãhar zance da isar da shi. Wannan ko yana daga ni’imomin
Ubangiji akan mutãne: (Allah) Mai rahama …, Yã halitta mutum. Yã sanar da shi
bayã ni (magana).
Bayãni , da shi ne ake jãwowa (mutum ya yarda) kuma da shi ne ake kõrewa. Sa sata ɗan
Sauhan yace : Annabin Allah yayi gaskiya (SAW), Lalle mutum ya kan kasance yana da
gaskiya –da tarin hujjõji – yana daga cikin masu gaskiya sai kaga wasu mutãne sun
sihirce bayãninsa (sabõda iya maganarsu) su tafi da gaskiyarsa (sai a ganshi maƙaryaci).
Kuma Umar ɗan Abdul -Aziz yace da wani mutum da ya tambayeshi game da wata
buƙatarsa, sai ya kyautata lafazin tambayar har ya ba Umar mãmãki: (Umar yace)
Wannan (m agana taka) wallãhi, tabbas tana daga halastaccen sihiri .
Mace tã sãmu (halal ne) ta rinƙa yin amfani da sihirin magana wajen farantawa mijinta
rãyi da bashi shãwarwari , sãɓanin wajen janye hankalinsa da karkatar dashi ya zuwa
saɓon Allah (SWA) –kamar mace tayi amfani da sihirin bayãni har mijinta ya yarda ya
bar ɗiyarsa ta shirya Party na gwangwajewa a ranar bikinta (harãmun ne).
Namiji, yã sãmu ya sihirce matarsa da kalãmai da zã su kãwo musu zam an lãfiya, harma
zai iya ha ɗawa da ƙarya ƴar ka ɗan, duk don a zauna lãfiya!
A bãbin da ya gabãta, mun gani , yana daga cikin ilimin bõkanci sanin yaudara da
annamimanci. Wannan sihiri na annamimanci yana halasta w ajen sulhunta mutãne n da
suka sã mu sã ɓãni, sai ya zama bã annamimanci ba kenan! Manzon Allah (SAW) yayi
rukusa cikin ƙarerayi guda uku:
a. Ƙarya a fagen yãƙi.
b. Ƙarya a cikin zantukan mutum ga m ãtarsa (Iyãlinsa) ,
c. Ƙarya a cikin sulhu tsakanin mutãne.
Anas ( R.A) yace: Duk wanda ya sulhuntã a tsakãnin mutum biyu, Allah Zai bãshi lãda
–ga kõwace kalma da yayi amfani d a ita, lãdan ƴanta baiwa.
Sulhu bashi da iyaka, Manzon Allah (SAW) ya ce: Sulhu jã’izi ne (ya halasta) a
tsakãnin musulmai, fãce sulhun (daidaituwa akan) haramta halal ko halasta
haram. Kuma Musulmi suna kan sharru ɗansu, fãce shara ɗin da zai haramta halãl i
ko ya halasta harãmun.
77
77
Allah (SWA) Ya ce:
Bãbu wani alheri a cikin mãsu yawa daga gãnawarsu fãce wanda ya yi umurni da
wata sadaka kõ kuwa wani alheri kõ kuwa gyãra (sulhu) a tsakãnin mutãne.
Wanda ya aikata haka dõmin neman yardõdin Allah to zã Mu bã s hi lãda mai
girma. (4:114)
Kwalliya tana daga cikin halastaccen sihiri da mãta kan iya yi su jãwo hankullan
mazãjensu har su daina tunãnin ta waje . Ita kõ kwalliya ta ha ɗa da ƙyali da gyaran jiki
(taushinsa da ƙãrin ni’ima da kula da gãshi da ƙirjĩ), amma banda canza halitta
(Bleaching , ƙãrin gãshi da sauran laifuka )
Shi kõ halastaccen ilimin dũba da bõkanci, bayaninsa yana da matuƙar yawa kuma a
cikinsa akwai bu ƙatar tantancewa. Yana da kyãwu bayaninsa ya kasance a sabon bãbi.
78
78
BÃBI NA SHIDA.
ILIMIN ALƘALUMA A FARKON DŨNIYA DA ƘARSHENTA .
Ilimin alƙaluma yana daga cikin ni’imõmi manya da Allah (SWA) Ya sanar da ɗan-
Adam a dõron ƙasã. Ilimi ne da yake dũniya (ake amfã ni dashi) tun lõkacin da Annabi
Ãdamu (A .S) yake rãye har ya zuwa wannan lõkaci.
Annabi Idris yãyi zãmani da Annabi Ãdamu –kãkan tãlikai –(A.S) sun rãyu tãre tsawon
shekaru ɗari uku da takwas (308). Shĩ ne Annabĩ ( ɗiyan Ãdamu) na farko bayan
annabcin Ãdamu da Shĩsu (Alaihimu s Salam).
A lõkacin Annabi Idris ne A llah (SWA) Ya sauƙar da il imin alƙaluma! Kuma an fãra
yin lissafin (hisã bi) ne a kan ƙas ã.
Amfani da il imin alƙaluma (ainihinsa) mu’ujiza ne ta Annabi I dris (A.S). Tun daga
lõkacinsa ake amfani da wannan ilimin (wanda ya k õyar) har ya zuwa wannan lõkaci.
Kõyarwansa ilimin alƙaluma kamar misãlin ɗibbun nabawiy ne da muka samu daga
Annabi Muhammadu (SAW).
Yã zo a cikin sahihin hadisi a littafai da yawa , har da Sahihul Muslim:
عن مُعاوِيَةَ بنِ اْلَكَمِ- رضي هللا عنه - قال: قلتُ: َي رسُولَ هللاِ إّن ِ حديثُ عَهْدٍ
َبْلاهِليهةِ، وَقَدْ جَاءَ هللاُ ت َعَاَلَ َبإلسَْلَمِ، وإنه مِنه ا رِجَاَلً َيَتُونَ الكُههانَ قال: « فََلَ أتِتِِمْ »
:ق ُلْتُ: وَمِنها رِجَال ي َتَطَْيهُونَ؟ قَالَ « ذَلِكَ شَيْء جيَِدُونَهُ ِفِ صُدُورِهِمْ، فََلَيَصُدهَّنهُمْ »
ق ُلْتُ: وَمِنها رِجَال خيَُطُّونَ ؟ قَالَ: « كَانَ نَبٌِّ مِنَ اْلنْبِيَاءِ خيَُطُّ، فَمَنْ وَافَقَ خَطههُ، فَذَاكَ. »
.رواه مسلم
79
79
Mu’awiya bn Hakam (R.A) yace: Ya Rasulullah ! Ina magana (game da) zãmanin
jãhiliyya, G ãshi yanzu Allah Ta’ala Ya kãwo musulunci: (A lõkacin) daga cikinmu
akwai mutãne da suke zuwa wajen bõka. (Annabi SAW) ya ce: (yanzu) kada kuje
wajensu.
Mu’awiya bn Hakam yace: (a lõkacin) daga cikinmu akwai mutãne masu yin
Istihãrar jefa tsuntsu sama (Ta ɗayyar), Annabi (SAW) yace: Wannan wani abu
ne suke sãm unsa a cikin zukãtansu (zuciya kan raya musu) , kada su tareku (daga
gaskiya).
Mu’awiya bn Hakam yace: (kuma a lõkacin) daga cikinmu akwai mutãne suna
buga (lissafin) alƙaluma, Annabi (SAW) yace: Ya kasance Annabin Allah daga
cikin Annabãwa (a lõkacinsa) ya na bug ãwa (lissafin), duk wanda ya dãce da
bugunsa to wancan (yã sãmu yayi ta bugãwa).
Malamai da yawa sunyi bayã ni game da fa ɗinsa (SAW): duk wanda ya dãce da
bugunsa to wancan (yã sãmu yayi ta bugãwa). Wasu malamai sukace a yanzu babu
yanda mutum zai gan e cewa bugunsa ya dãce da irin wanda Annabi Idris (A.S) ya koyar
sabõda haka babu wani sauran halastaccen bugu! Wassu ko , ce sukayi ai irin maganar
nan ne ta hikima wanda take nufin: idan mutum zai iya gãnowa halastaccen bugun
Annabi Idrĩsa bã sai yayi ba!
Kĩmãni n shekaru biyar ina binciken neman ƙ ãrin haske game da wannan hadisi, kafin
na samu bayanen malamai da na rubata a sama . A cikin shekarar 2006/2007 na fãra
fahimtar yanda wannan hadisi ya dõsa a zãhiri (da ikon Allah (SWA), a lõkacin ina
Level 500 (Electrical Engineering )). Cikin ƴan shekarun nan, Allah da ikonSa, Y ã bani
dãmar fayyace bayãnai uku da mutãnen ƙarni (aƙalla) gõma ke neman sani n haƙiƙanin
bayãnansu . Alhamdulillah! Ba tare da nã kasance mai wani zurfin ilimi ba, Allah (SWA)
Ya karramani da fayyace war:
1. Ahrufus Sab’a –logar karatun Alƙur’ani bakwai
2. Ayyamullah –Rãnakun Yaumul ƙyama , da
3. ILmul ƙalam –Ilimin hisãbi (Lissãfi) da aka sauƙar wa Annabi Idris (A.S) .
Shi ilimin hisãbi babu wata hanyar lissafi da takai shi sauri. Ana amfani dashi ta hanyõyi
da yawa, Mũsa mman a wannan ƙarni , duk da cewa mutãne basu fahimci ilimin ne suke
amfani d ashi ba .
A cikin wannan litt ãfin, lõkacin da nake bayani game da Istiharar Ramlu ( bugun ƙasa )
na kãwo alƙaluma (tare da siffarsu) guda g õma sha shida, kamar haka:
80
80
SIFFAR ALƘALAMI SŨNAN ALƘALAMI
Ɗarĩƙ
Itbatu Dãkila (Rãyatul Far’hi) ,
Naƙayil kuddi ,
Nasaratul Dãkila ,
Jaudala (kausaji) ,
Ƙabrud Dãkila
Al-Iƙlah (Shiƙaf)
Inkis
Itbatu khãrija
Al-Ijma
Ƙabrud khãrija
Bayãra
Nasaratul khãrija
Humrah
Ahyan (Rãhika)
Jamã’a
81
81
Idan kã lũra da siffar wa ɗanna n alƙaluma , bari mu jũya kowane alƙalami samansa ya
kalli gefen dã ma. Su zama kamar haka:
SIFFAR ALƘALAMI SŨNAN ALƘALAMI
Ɗarĩƙ
Itbatu Dãkila (Rãyatul Far’hi) ,
Naƙayil kuddi ,
Nasaratul Dãkila,
Jaudala (kausaji) ,
Ƙabrud Dãkila
Al-Iƙlah (Shiƙa f)
Inkis
Itbatu khãrija
Al-Ijma
Ƙabrud khãrija
Bayãra
Nasaratul khãrija
Humrah
Ahyan (Rãhika)
Jamã’a
Yanzu bari mu sake kwafan ( copy ) waɗannan alƙaluma (wa ɗanda muka jũya) , amma
wajen lã yi mu rubuta ɗaya, wajen ɗugõ (dot) mu rubuta sufuli ( zero).
Idan mun kwafa (tare da maye gurbin lãyi da ɗaya, ɗugõ da sufuli), alƙalumanmu zasu
kasance kamar haka:
82
82
SIFFAR ALƘALAMI SŨNAN ALƘALAMI
0000 Ɗarĩƙ
0001 Itbatu Dãkila (Rãyatul Far’hi) ,
0010 Naƙayil kuddi ,
0011 Nasaratul Dãki la,
0100 Jaudala (kausaji) ,
0101 Ƙabrud Dãkila
0110 Al-Iƙlah (Shiƙaf)
0111 Inkis
1000 Itbatu khãrija
1001 Al-Ijma
1010 Ƙabrud khãrija
1011 Bayãra
1100 Nasaratul khãrija
1101 Humrah
1110 Ahyan (Rãhika)
1111 Jamã’a
Wai ko ka fahimci me alƙal uman suka koma? Allahu Akbar! Waɗanna n alƙaluma sun
kõma “ Binary numbers ” –magana ( yãre) da computer ta ke fahimta! Da wa ɗannan
alƙaluma ne dukkan fasãhar zãmani ta digital take aiki. Kãma daga calculator, ag õgo,
wayar hannu ( GSM ), HD satelliate reciever , Radio, TV, da sauran dukka n abubuwa da
suke amfãni da “alluna masu ɗauke da kãyan bugun alƙaluma ” (electronics circuits
boards ).
Wani abun mãmãki , kayan cikin computer na IC -IC (integrated circuit ) duka an ƙerasu
ne da t ãcacciyar ƙasa ( silicon ). Akan wanna n ƙasar ne , mai amfani da nã’ũrar computer
ko wayar hannu ( GSM ) yake bugun alƙaluma.
83
83
6.1 ALƘ ALUMAN DÃ, DA NA YANZU.
Allah (SWA) Shi ne Mafi sani k õ dã can anyi amfani da alƙaluma sabbi irin na
Amurkãwa. Am urka ta cinma matsaya akan alƙaluman da kamfanõni masu ƙera digital
abubuwa za su riƙa amfani da su wajen bugu wa ɗanda ake ce dasu: American Standard
Code for Information Interchange (ASCII). Sun sanya alƙalami biyu ga kowane
harafin keybord .
Amma irin jerin alƙaluman dã taskin -taskin ne: taskĩnul huruf , Taskĩnul kawãkib,
taskĩnul dã'irati da sauransu, Wa ɗanda a yanzu sune Weighted and un-weighted codes :
8421 codes, 7421 codes, 5421 codes, 6311 codes, 5311 codes, 3321 codes, gasunan da
yawa. Ka bincika Binary Coded Decimal (BCD).
84
84
1
0
0
1
0
1
1
0
6.2 YAD DA COMPUTER DA DANGINTA SUKE SARRAFA ALƘALUMA.
Ba wani abu ne a cikin computer da wayõyin sa lũla ba wanda da ya wuce killacecciyar
ƙasa –Semiconductors . Ƙasa ce aka sarrafa aka dunƙule gurbi -gurbi (IC -IC), kowane
dunƙulen ( IC) yana irin bugun alƙalami da aka ajiyeshi d õminsa. Misali:
IC na cikin computer da suka shahara da sa rrafa alƙaluma ana ce musu LOGIC GATES .
Mafi ƙarantar IC mai juya kan alƙalami (bit) shi ne NOT GATE . Sai an sãmu NOT
GATE guda hu ɗu su juya alƙalami ɗaya (ya zama kishiyar wanda aka juya) , ga misalin
su.
IC ɗaya (mai lamba 7404 ) zai iya maka wannan bugun!
Task ĩnin Alƙaluma (Binary Coded Decimal)
85
85
A fasalin da nay i bayanin Ramlu (bugun ƙasa), nã fitar da alƙaluma daga kãyin iyã ye,
ƙirjin su da sau ransu, sai muka buga sauran gidã je kõwane gida biyu (alƙaluma biyu)
suka fitar da wani alƙalamin daban . Wannan bugun zã mu ga OR GATE ne yake yi n sa!
Shĩ OR Gate, IC ne mai ƙafa uku ( ƙafa biyu mashiga , ɗaya mafita) hotonsa kamar haka:
OR Gate yana ha ɗa kan alƙala mi da alƙalami ne ya fitar da kã yin wani alƙalamin. Ko
ƙirji da ƙirji ya fitar da wani ƙirjin alƙalamin, … haka nan dai! Lõgar da OR gate yake
bi (ya buga kãyi da kãyi) ya fitar kãyi na uku shine: idan kã yuwan alƙaluma biyu suka
shiga OR Gate, to abin da zai fitar shi ne (1 = true) idan ɗayan alƙaluman da suka shiga
ya kasance (1) ne!
Wannan lõgõ gin bugu na LOGIC GATES ana rubũ tãsu a teburi da ake kira TRUTH
TABLE . Truth table na OR Gate ya kasance kamar haka:
OR GATE guda hu ɗu ne za su iya buga alƙaluma biyu su fitar da na ukunsa! Gã mis ãlin
yadda bugun zai kasance:
OUTputs
INputs
86
86
Kã ga a wannan mis ãlin OR G ates guda hu ɗu sun buga alƙal uman Bayãra da Humra
sun fitar da alƙalami mai sũna Jam ã’a. A bõkonce:
(Kar ka manta 0 OR 0 = 0 )! IC guda ɗaya mai lamba 7432 yana ɗauke da OR Gates
guda hu ɗu, yana dai -dai da ya buga alƙaluma.
Sauran LOGIC GATES da suka ha ɗu sukayi ƙwaƙwalwar computer sun ha ɗa da: NOR,
NAND, AND, XOR, X NOR. Da wa ɗannan IC kana iya gina komputar kanka da kanka !
Full-adder (kwakwalwar liss ãfin tara Ku ɗi ko wani abu)
87
87
6.3 Yadda Computer da danginta suke ajiye alƙaluma a rumbu .
Kamar ya dda nayi ba yãni a bãya, alƙalami yana da kãyi, ƙirji, cikĩ da ƙafa. Tunda mun
jũya alƙaluman mu (sun kõma dãma zuwa hagu), sai mu kira kõ wane ɗaya (kãyi ko ƙirji
ko ciki ko ƙa fa) BIT. Cikekken alƙalami yana da BIT guda hu ɗu, BIT guda takwas
(alƙaluma biyu jere) ana ce musu BYTE .
Idan alƙaluma biyu-biyu jere ( byte) suka kai dubu sai ace musu KILO -BYTE . Alƙaluma
byte miliyan ɗaya sune MEGA -BYTE . Alƙaluma byte miliyan dubu su ake cewa
GIGA -BYTE . Na ƙarshensu TERA -BYTE .
Memory (rumbu) da zai iya ajiye alƙaluma byte miliyan dubu, idan kaje sayensa a
kasuwa sai kace a baka memory gigabyte ɗaya (1 Gigabyte), yanzu naka n ji mutãne suna
cewa 1 -Gig, 2 -Gig, 4-Gig, da sauransu. Ba’a ƙera 3 -Gig! 5, 6, 7 Gigs!
Ana ƙera memory ne bayan an lissafa 2 power n . (2n) kaga idan ka lissafa da n = 10,
11, 12…
210 = 1024 byte = 1 kilobyte
211 = 2048 byte = 2 Kilobyte
212 = 4096 byte = 4 kilobyte
213 = 8192 byte = 8 kilobyte.
Idan da Gigabyte m uke lissãfi kã ga zaka samu 1 Gigabyte, 2 Gigabyte, 4 Gigabyte sai
8 Gigabyte, 16, 32 da sauransu. Haka dai lissafin tãron alƙaluma yake kasancewa a duk
fãɗin dũniya .
Kowane harafi na keybord da ka sani , alƙalami guda ne . Idan ka lãtsa harafin A,
computer zata maida shi alƙalami ( binary ) sannan ta ajiye shi a memory. Dubban
memory a cikin computer sune REGISTER S. Bangaren da computer ke yin bugu kuwa
shi ake kira ARITHMETIC & LOGIC UNIT (A.L.U). Dukkan nã’ũra masu tuna abu
(masu kwakwalwa) suna da wannan tsãr i na memory, A .L.U da sauransu , wato suna da
CPU ( Central Processing Unit ). Bayanen ne… computer engineers zã sufi g ãnewa.
Computer da danginta, suna sarrafa alƙaluma n da suka ajiye ne ta hanyõyi kamar haka:
88
88
1. Hanyar bugu da jujjuya alƙaluma: Duk abin da ka sani –hoto, sautin MP3,
Video– sai computer ta mayar dashi alƙaluma kafin ta ajiye shi. Duk editing (na
sarrafa hõ to ko Video) da ka sani computer tana yinsu ne ta hanyar bugun
alƙaluma da jujjuyasu ( logic gates conversion ). Tsãfin computer na cire kan
mutum da ɗõra shi akan wani hõton duk sarraf ãwar alƙaluma ne. A video edi ting,
akwai wani tsãfin computer na ɓoye duk abinda aka rufe shi da kõren kyalle
(kyalle tsanwa) ko shũ ɗi. Misali : idan aka ɗauki hotonka da video camera kana
sanye da shu ɗɗan kã ya, a wa jen editing idan akayi CROMA KEY ING na hotonka
sai computer tayi tsãfin rufa -ido a shu ɗɗan kayanka, sai aga kã yinka shi ka ɗai
yana tafiya yana magana. Ta iri n wannan hanyõyi ne masu shirya fina-finai suke
irin dabon da suka ga dãma ! Allah (SWA) Yana cewa:
Kuma akwai daga cikin mutãn e wanda ke sayen tãtsuniyõyi (fina -finai) dõmin ya
ɓatar da mutãne daga hanyar Allah, bã da wani ilmi ba, kuma ya riƙe ta abin
izgili! Wa ɗancan sunã da wata azãba mai wulãkantãwa.
Kuma idan an karanta ãyõyinMu a gare shi, (a kace masa kallon fina -finai ba
kyau) sai ya jũya bãya, yanã mai girman kai, kamar dai bai saurãre su ba kamar
dai akwai wanĩ danni a kan kunnuwansa! To, ka yi masa bushãra da azãba mai
raɗaɗi (da zai shiga a rãnar Lãhira) . (31:6 -7)
An sauƙar da wannan aya ne a dalilin Nadri ɗan H ãris, Yã sayi wata baiwa maw ãƙiya
(kamar yar film). Ya kasance daga y ã ji wani yana niyyar zuwa kar ɓan musulunci sai
ya kirashi zuwa wurin wannan mawaƙiyar ya ce da ita: (ga baƙ õna) ki ciyar dashi, ki
shãyar dashi, ki rera masa wãƙa . Wa nnan yafi (masa) alheri daga abinda Muhammadu
yake kira zuwa gareshi ( na musulunci).
Wannan dai -dai yake da (hãlin) mutumin da zai hana mutãne saurã ron karatun Alƙur´ãni
ya saka musu wãƙõ ƙin drama…
2. Hanyar bin umarni (programming): Wancan bayani na bugu da computer take
yi da sarrafa alƙaluma duka bayani ne da ya shafi computer hardware .
Tãrin u marni da suke gayama computer irin bugun da akeso tayi shi ake kira
software . Software na farko da ake saka ma computer ita ce ta rũhin ta (ana ƙiranta
system softwa re), misã linsu Windows 7 na kamfanin Microsoft da Ubuntu .
Da system software ne computer take gãne keybord , mouse da sauran jikkunanta.
Software na biyu da ake sakawa computer ita ce Application software . Application
software tãrin umarni ne dake sa compu ter tayi duk irin abinda ake so.
Application software guda ɗaya ana kiransa program . Zaka fi saurin ganewa idan
89
89
nace maka Apps! WhatsApp s, Facebook Apps, Twitter Apps, gã sunan tuli a
google play duk application sof tware ne na waya r Android .
Rubuta wa comp uter application (tãrin ũmarni –idan an taɓa can ki bũde shafi…)
shi ake kira programming . Kowane program da aka saka a cikin computer, yana
shiga ne da tãfinta ( Interpreter ko compiler ) wanda zai na fassara wa computer
yaren program zuwa nata yaren na alƙa luma. Misali idan ka danna kar ɓan
N10,000 a ATM, tã fintar dake cikin computer zai mayar mata da yaren alƙaluma.
Da ilimin alƙaluma ne computer zata ƙidaya ku ɗin da ka buƙ ata (bayan ta dũba
yawansu a asũsu nka) sannan ta miƙo maka dai -dai yawan ku ɗin da ka t ambaya.
Hanyar programming y ã bunƙasa hany õyin amfanuwa da computer kwarai,
halastattun hanyõyi da haramtattu. Kãmã daga program na rubũtu, program na
saurãron karatun Alƙur´ãni (Quran player), program na karta (card), da sauransu.
Robot (mutum -mutumi), n ã’ura ne mai siffar mutum da ake sanya mata programs
(tãrin umarni), sai kawai kaga gunki yana aikata aikin da aka bashi umarni!
6.4 YADDA AKE RUBUTA COMPUTER PROGRAMMING:
Ba sai mutum ya iya bugun alƙaluma zai iya rubuta computer program ba. Akwai
mutãn e da suka ƙirƙiri yãrai da yawa ( programming languages ) da mutum kan iya
kõya ya rubuta wa computer tarin umarni. Misalin programing languages sun ha ɗa
da JAVA, FORTRAN, C++, Visual Basic, Android Programing da wanda yake
tãshe yanzu –python programming .
Kafin ka yanke shawarar yãren da za kayi amfani das hi wajen rubuta program, akan
zãna wani abu da akece masa flowchar t. A takaice misali nsa kamar haka:
90
90
A wannan ƙaramin misalin (na ATM machine), idan program ya fãra, computer zata
rubũto maka: “M alam saka katinka”. Idan ka saka kãti an umarceta da ta fãra dũba
shekarar da katin zai ƙare sai ta tambayi kanta da kanta: ATM yayi expire ? Kuma sai ta
bãyar wa kanta amsa.
Idan amsar Yes ne (yayi expire ), sai tabi umarnin hannun dãma ta tũro maka da kãt inka
ka ƙãra gaba. Sannan ta tsaya haka nan (kar ta shiga abinda ba’a sata ba) .
Idan amsar No ne (katin baiyi expire ba) sai ta bi umarni (na ƙasa) ta dũba sunan jikin
katin ta rubuto “Welcome wane” ta ambaci sunan jikin katin. Daga nan sai ta wuce
umarni na gaba (a misalinmu shine ta tsaya haka nan), idan kuwa ta tsaya hakanan ba
yadda za ayi katinka ya fito! S abõda ba a bãta umarnin fita r maka da k ãti ba. Sabõda
haka programming yana buƙatar tun ãni (sãke -sãƙe) mai yawa.
Idan zã muyi amfani da wannan flowchart (na sama) mu rubuta program
kwatankwacinsa wanda za’ayi installing a computer yayi aiki, sai mu rubuta codes
kamar haka:
dim ATM_name = n, ATM_expiry = x, todays_date = y
Duk wa ɗannan bincike n, computer tana yinsu ne ta hanyar bugun alƙalu ma a cikin
ARITHMETIC AND LOGIC UNIT (ALU) –cikin tãrin LOGIC GATES .
Tun kafin a haif e wacce tũrawa suke ganin ita af farkon programmer a dũniya ( Ada
Lovelace ), Imam Shãɗibiy (Rahimahullah) ya rubuta program –waƙar sanin ƙirã’oin
Alƙur´ãni mai girma da ruwãyõyinsa.
Littafin na Imam Shã ɗibiy, mai sũna “Hirzul amãniy… ” (mai laƙabin Shã ɗibiyya) , ya
samu kar ɓuwa kwarai da gaske. Duk wanda ya saurã ri sha ɗibiyya zai yi mãmãki n
fasãhar wannan bãwan Allah. Farkon wãƙar ma ce yayi:
Na fãra coding (wannan program) da sunan Allah,
Tabãraka, Rahmãnan, Rahĩman wa Mau’ilã (Mai kiyãyewa).
91
91
Bayan ya bũ ɗe (wãƙe) da Basmalah, yã yi salãti da yabõ ga fiyayyen hali tta (SAW), ya
gõdewa Allah (SWA) sannan ya zayyana falalar Alƙur´ãni da makarancinsa sai ya zarce
da ambatõ sunayen Imãmai mãsu ƙirã’ oi da ruwãyõyinsu, Ya ce:
فأما الكري السر ِف الطيب َنفع ... فذاك الذي اختار املدينة منزَل
Amma (kãga) mai girman sirri na ƙamshin (jiki) Nãfiu…,
To, wannan shi ne ya zã ɓi (garin) Madina Wurin zama.
Ya zayyana Imãmai (ƙirã’oinsu) bakwai da ruwãyõyinsu sannan ya fara coding !
وها أَن ذا أسعى لعل حروفهم ... يطوع ِبا نظم القواِف مسهَل
جعلت أَب جاد على كل قارئ ... دليَل على املن ظوم أول أوَل
Tõ yanzu zan jarraba, la’alla harrufansu (da zan bãsu wajen coding ),
Suyi dacewar (bibiyan) zubin ƙãfiya sake ba ƙaidi.
Na sanya (lissãfin) A-ba-ja-din akan kõwane (Imam) Mai ƙirã’a,
(Ya zamto) Dalili (da za’a gãne shi) akan kõwane lãyi na code ɗaya bayan ɗaya.
A taƙaice Imam Shã ɗibiy yãyi declaration na Imãmai da harrufa (A, B, J, D…) kamar
haka:
Dimens ion (Dim) :
Nafi’u = A, Ƙalun = B, Warshu = J,
Ibn Kasir = D, Bazzi = H, Ƙumbul = Z
Abu Amr = h, Duuriy = T, Sũsiy = Y
Ibn Ãmir = K, Hisham = L, Ibn Zak’wan = M
Ãsim = N, Shu’uba = S, Hafsu = AIN
Hamza = F, Kalaf = Dh, Kallad = Q
Kisã’iy = R, Abul Hãris = S, Duuriy = T
Akwai wassu declaratio ns da ya ƙã ra sannan ya fãra rubũta codes lãyi-lãyi a kowane
fasali. Ka ɗau misã lin baitin farko na fa salin Sũratu ummul ƙur’an :
92
92
ومالك يوم الدين راويه َنصر ... وعند سراط و السراط ل قنبَل
(Karatun) Mãliki yaumid diyni wa ɗanda suka rawaito (karantashi da alif) sune Nãsirun,
Kuma amma wurin (karãtun Sira ɗal…) sirã ɗa ne da sirã ɗi a (karatun ruwayar) ƙumbul .
Bayani:
Gaɓar wãƙar ta farko, tana umurnin computer cewa karãtun “ Mãliki yaumid diyn ” ta
sanya shi ga Imam da a ka yi declaring ɗinsa da N (N = Ãsim (ruwayat Hafs da Shu’uba) )
sabõda shi ka ɗai ne cikin masu ƙira’a bakw ai yake karantawa hakanan . Sauran Im ãmai
kuma suna karantawa “ Maliki Yaumid din ” ba tare da alif akan mĩ mun ba.
Gaɓar wãƙa ta biyu kuma yana nuna cewar karãtun:
اهْدَِنَ الص ِرَاطَ الْمُسْتَقِيمَ (٦ ) صِرَاطَ الهذِينَ أَن ْعَمْتَ عَلَيْهِمْ
Imam ƙumbul yana karantãwa ne da harafin Sĩnun a maimak on harafin Şodun kamar
yadda kaga kalmomin a ga ɓar baitin. Yanayin wãƙa yasa ya fãra ambatar Sira ɗa ta biyu
kafin ta farko.
Haka Imam Shã ɗibi yayi ta jera lãyukan programming codes har lãyuka dub u da ɗari
da saba’in da uku (1173). Allah (SWA) Ya kai haske cikin kabari n waliy na kwarai .
Ibn Jazari shi ne yabi sahun Imamu Shã ɗibĩ, ya cika bayanin ƙirã’oin sauran Imãmai
uku da ruwãyõyinsu ta hanyar coding . Littafinsa mai sũna Ad-Durra ya shahara kwarai
a fannin kimiyar Alƙur´ãni mai girma.
Kada na jã ka da nis a, in taƙaita maka bayani, hanyar computer programing (in sha
Allahu) itace da Annabi (SAW) yace: Ya kasance Annabin Allah daga cikin
Annabãwa (a lõkacinsa) yana bugawa, duk wanda ya dãce da bugunsa to wancan
(yã sãmu yayi ta bugãwa). Mutum ya sãmu ya rubu ta codes sannan yayi running !
Duk da cewa programming ya halasta, akw ai hanyõ yin da basu halasta ba. M un ga
wassu kafin wannan bayã nin. Programing (mutum ya ƙirƙiri program ) na wasanni
(games ) na karta ko wãsannin bãtsa ko wa ɗanda zã su shagaltar da mutum daga addinin
musulunci duka harãmun ne kuma suna kõmawa ne ga irin bugun ƙasa na ramlu (na
kirdãdon gaibu).
Sabõda kasancewar rubuta program yana tattare da tsammani (sãƙe -sãƙe na zãto), ya
kamata mu san wane zãto ne yake halal a musulunci. Yanzu ga bayan ai a kan ilimin
zato:
93
93
6.5 PROBABILITY :
Probab ility lissafin fãruwar wani abu ne ta hanyar alƙaluma ( numbers ). Lissafi iya gãya
(matuƙa ) da wani marar tauhidi kan iya cewa tabbas abin zai faru !
Za mu iya cewa akwai probability na rashin tabbas da tsamm ani, da probability na
mũgun zato da probability na ka ɗin ludo.
1. Probability na rashin tabbas da tsammani n ƙaddarar Ubangiji : Irin wannan
probability, masu lissãfã shi aikin banza ne. Ko ba’a lissãfã shi ba, mutum bashi
da tabbacin faruwar abun , Amma d ole yana tãre da tsammanin fãruwar wani abu
a zũciyarsa.
Misãlin probability akan marar lafiya rabi da rabi ne! Rabin tsammani warkewa,
ɗaya rabin kuma mutuwa. Sabõda haka ne probability in an tãrashi duka sai ya
zama ɗaya (ko 50% + 50% = 100%) .
To amma id an aka sãmu marar lafiyar wani ne ya fasa masa ciki (har hanjinsa ya
fito), tsammanin mutuwa sai yafi na rayuwa, misã li tsammanin mutuwa ya
kasance kashi saba’in (70%) na rãyuwa ya kasance sauran kashi talatin (30%).
Dukkan rãyuwar ɗan-Adam tana cike da t sammani ne, abubuwan da zã su
sãmeshi. Wani lõkaci alheri yayi ta bijir õwa fiye da tsammanin mutum kãfin
jarraba wa ɗaya ta zo, wani lõkaci kuma jarrabawar takan fi yawa. Alhamdulilãhi
a kõwane hãli.
Ɗan Mas’ud (R.A) yace: Annabi (SAW) ya yi mana wani zãne mai gefe
huɗu, sannan ya j a wani dogon layi daga tsakiya har sai da ya fita waje.
Kuma ya zana wassu ƙananan layuka daga layin tsakiya …,
kamar haka:
94
94
Iyakar Ajalin (rayuwar) ɗan-Adam
(Dogon) Bũri na ɗan-Adam :
Yaso wannan yaso wancan!
Siffa r ɗabĩ’ar ɗan-Adam : Bũrinsa ya fice ajalinsa!
Sai Annabi (SAW) yace: Wannan , (kamar) shi ne (mis ãlin) mutum! Wannan (zãne
mai gefe hu ɗun) ajalins a ne da ya kewayeshi. Wannan ( dõgon lãyi) da ya fita,
bũrinsa ne. waɗannan ƙanãnan zãnen kuma (ƙaddara) masu bijirõwa ne. Idan
wannan (alherin) ya ku ɓuce masa sai wannan ya cimmasa , idan wannan
(jarrabawa r cũta) ta ku ɓuce masa sai wannan ta cimmasa. (Bukha ri ya rawaito)
Zanen (ginin blocks) na jikin ɗãkin Ka’aba zai tuna maka da wannan hadisin a kowane
lõkaci, In shã Allahu!
Rãyuwa tsammanin 50-50 ne, idan ka wayi gari kar kayi tsammanin jiran yammaci.
Idan ka kai yamma (a rãye) kar kayi tsamm anin jiran zaka wayi gari. Kayi imãni
da ƙaddara:
قُلْ إِنه صََلَِتِ وَنُسُكِي وََمَْيَايَ وَِمََاِتِ ّلِلِهِ رَب ِ الْعَالَمِنيَ( 162 ) َلَ شَرِيكَ لَهُ...
Ka ce: "Lalle ne sallãta, da baikõna, da rãyuwãta, da mutuwãta, na Allah ne
Ubangijin tãlikai." "Bã bu abõkin tãrayya a gare Shi. (6:162)
Shĩ probability na rashin tabbas da tsammani n ƙaddara , muminai suna mayar da
al’amarinsu ne ga Allah –Ubangijin halittu. (ba sa lissãfãshi ko su sa a lissãfa musu ta
hanyar bugun ƙasa da sauransu).
95
95
Irin wannan tsammãni na maida al’amari ga Allah (SWA) shi ne wanda Annabi Yusuf
(A.S) ya yi game d a abõkan zãmansa na kurkuku bisã lũra da la’aka ri da mafarkin da
yayi. Mafarkin Annabawa kuma tabbaci ne! Amma dai Ya maida al’amari zuwa ga
Allah (SWA).
وَقَالَ لِلهذِي ظَنه أَنههُ َنَجٍ مِن ْهُمَا اذْكُرّْنِ عِنْدَ رَب ِكَ فَأَنْسَاهُ الشهيْطَانُ ذِكْرَ رَب ِهِ ف َلَبِثَ ِفِ
الس ِجْنِ بِضْعَ سِنِنيَ
Kuma ya ce da wanda ya tabbatar da (tsamm ãnin) cewa shi mai ku ɓuta ne daga
gare su, "Ka ambace ni a wurin uban gidanka." Sai Shai ɗan ya mantar da shi
tunãwar Ubangijinsa, sabõda haka (Annabi Yusuf) ya zauna a cikin kurkuku ´yan
shekaru. (12:42 )
Irin wannan probability na t sammani halal ne, kai wajibi ne kõwane mũmini ya yishi da
tabbaci:
إِّن ِ ظَن َنْتُ أَّن ِ مَُلَقٍ حِسَابِيَهْ
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai ha ɗuwa da hisãbina ne." (69:20)
Kamfanunnuwa da yawa suna amfani da probability na tsammãni ta hanyar computer
(division of sales figures ) wajen kirdãdon cinikin da akan iya sãmu a kõwane watan
shekara, Program na Microso ft Excel ya shahara da irin wannan aikin! Sai dai su
kamfanunnuwa suna forecasting sales ne sabõda su tãnadi kayan ayyukan da zai ishe su
aikin shekara. Allah Shi ne Masani.
2. Probability na tsammani game da ɗan-uwa: Ɗan-uwa anan, musulmi namiji ko
mace, sa bõda Annabi (SAW) yace : Musulmi ɗan-uwan musulmi ne!
Addinin musulunci addini ne da yake kira zuwa ga kyautata zato (na tsammani) ga
mutãne , sabõda Allah (SWA) Ka ɗai ya san abubuwan da suke ga zuciyar mutãne .
Aliyu bn Abiy ɗãlib (R.A) y a ce: Wanda ya zacek a da alheri ka gaskata zatonsa .
Kada kayi (mummunan) zato (game) da wata kalma (mummuna)
wacce ta fita daga (bãkin) wani, alhãli kai zaka iya fassara
mummunar kalmar (da ya fa ɗa) da kyakkyawa.
A lõkacin da aka yi ƙiren ƙarya (yarfe) ga Nana Aisha (Matar M anzon Allah (SAW)
Allah Ya yarda da ita ) mutãne da yawa ba suyi zatõ na kyautata tsammã ni game da
96
96
ɗan-uwa ba, sai suka kũtsa cikin gari suna yã ɗa zance irin na propaganda . Allah
(SWA) Ya ce:
لَوَْلَ إِذْ َسَِعْتُمُوهُ ظَنه الْمُؤْمِنُونَ وَالْمُؤْمِنَاتُ ِبَِن ْفُسِهِمْ خَْيًْا وَقَالُوا هَذَا إِفْك مُبِني
Don me a lõkacin da kuka ji shi (lãbarin) mũminai maza da mũminai mãta ba su
yi zaton alheri (na kyautata tsammani) game da kansu ba (su canza maganar da
suka ji da mai kyau kamar yadda Abu Ayuba da m atarsa sukayi ) kuma su ce:
"Wannan ƙiren ƙarya ne bayyananne?" (24:12) `
Lalle ne wa ɗanda suka zo da ƙiren ƙarya (game da lãbãrin Nana Aisha) waɗansu
jama´a ne daga gare ku, kada (mũminai) ku yi zatonsa sharri ne a gare ku. ôa,
alheri ne gare ku. Kõwane m utum daga gare su na da sakamakon abin da ya
sanã´anta na zunubi, kuma wanda ya ji ɓinci girmansa, daga gare su, yanã da
azãba mai girma. (24:11)
3. Probability na mummunan zatõ: Amma kã ga probability (zatõ) na hassada da
mugunta ya kasance wanda yake hãlaye n kãfirai da munafukai ne kuma irinsa ne
bahaushe kan ce: “Zatõ zunubi ne kõda y ã zama gaskiya” :
ôa kun yi zaton Annabi da mũminai, bã za su kõmo zuwa ga iyãlansu ba, har
abada (a lõkacin da suka tafi yãƙi) . Kuma an ƙawãta wannan (tunãni) a cikin
zukãtank u, kuma kun yi zato, zaton mugunta, kuma kun kasance mutãne
halakakku . (48:12)
وَي ُعَذ ِبَ الْمُنَافِقِنيَ وَالْمُنَافِقَاتِ وَالْمُشْرِكِنيَ وَالْمُشْرِكَاتِ الظهان ِنيَ َبِّلِلهِ ظَنه السهوْءِ
Kuma Ya yi azãba ga munãfikai maza da munãfikai mãtã da mu shirikai maza
da mus hirikai mãtã, mãsu zato mugun zato game da Allah, ... (48:6)
Ƙolõluwar mũgun zatõ game da Allah shi ne mutum ya ɗõra zaton Allah ba zãYa tãshi
matattu ba –domin rãnar sakamakõ.
إِنههُ ظَنه أَنْ لَنْ َيَُورَ
(Dõmin shi) Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba (zuwa ga Allah) . (84:14)
Kã ga irin wannan zaton ai na kafirai ne –marasa addini ( pagans ). Tun dã ma, sũ da
shaiɗanu suna yin mũnãnan zato:
97
97
وَأََّنهُمْ ظَنُّوا كَمَا ظَن َن ْتُمْ أَنْ لَنْ ي َب ْعَثَ اّلِلهُ أَحَدًا
"Kuma lalle ne mũ, mun yi zaton mutum da aljani bã zã su iya fa ɗar ƙarya ba ga
Allah." "Kuma lalle ne shi wasu maza daga cikin mutãne, sun kasance sunã neman
tsari da wasu maza daga cikin aljannu, sabõda haka suka ƙãra musu girman kai."
"Kuma lalle ne sũ, sun yi zato , kamar yad da kuka yi zato, cewa Allah bã zai aiko
kowa (da manzanci) ba." (72:5 -7)
Kamar yadda ya gabãta, masu bugun ƙasa suna amfani da ilimin probability ta hanyar
dũba allon rãyuwa ko mutuwa su bãda lãbarin (zaton) aƙibar marar lafiya. Kamar haka
ne ake amfani d a ilimin (a zãmanance) a bãyar da lãbã rin yiwuwar sãmuwa r rũwan sama
da makamancin su (weather forecast ). Ĩmãni da gaskat a probability wajen samun ruwan
sama kamar ĩmã ni da sãmunsa don tsayuwar wan i taurãro ne, hakan kuwa kãfirce wa
addinin da Manzon Allah (SAW) yazo dashi ne!
4. Probability na ka ɗin ludo ( dice): Lissãfi irin wanda da shine ake fitar da rabon
gãdo da zakka shekaru aru -aru da suka gabãta, lissãfinsa ya taƙaita ne ga tãrawa,
ɗebewa da sarayarwa ( basic arithmetic s).
Hanyar ka ɗin ludõ ( sampling of data) yanki ne na ilimin probability na zãmani !
Masana statistics sun shahara wajen amfani da ilimin kaɗa ludõ wajen ƙididdigewar
lissafi. Akwai computer programs masu yawa da ake amfani dasu wajen data
analysis .
Ta hanyar ka ɗin ludo (mean , median , mode ), bayan lissãfin ƙera matsakaicin kujerun
zama na ƙabĩlõli da sauransu, akan lissafa zaton shekaru (life span ) da ɗan wata ƙasa
(kamar china) zai rãyu a duniya!
Bayani yã gab ata, yadda masu bugun ƙasa kan aikata (tun dã can) su fitar da lãbãrin
gaibu ta hanyar ka ɗin ludõ .
To sai dai Agõgo mai nũ na lambõbi ( digital clock ), na cikin applications programs , ana
yinsa ne da bada umarnin random . Umarnin random (na wã -taganganõ) yanki ne d aga
kaɗĩn ludõ, kuma da shi ne ake sanya player ta riƙa zã ɓen wãƙõƙi a birkice (idan an
lãtsa shuffle ko Random ).
LUDÕ
(DICE )
98
98
َيَأَي ُّهَا الهذِينَ آمَنُوا اجْتَنِبُوا كَثِْيًا مِنَ الظهن ِ إِنه ب َعْضَ الظهن ِ إُِثْ...
Yã kũ wa ɗanda suka yi ĩmãni! Ku nĩsanci abu mai yãwa na zato. Lalle sãshen
(wani yankin ) zato laifi ne. .. (49:12)
6.6 ALƘALUMA UKU NA CIKIN ALƘUR´ÃNI MAI GIRMA.
Allah (SWA) Ya yi magana game da alƙaluma nau’i uku a cikin Alƙur´ãni mai girma.
1. Alƙalami na farko: Yana daga cikin Alƙaluman da A llah (SWA) Ya ambata a
cikin Alƙur´ãni mai girma, alƙalamin da aka fara halitta kãfin komai. Allah
(SWA) Yace:
ن وَالْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَ ( 1 ) مَا أَنْتَ بِنِعْمَةِ رَب ِكَ ِبَِجْنُونٍ
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa. Kai (Annabi
Muhammadu) , sabõda ni´imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba. [68.2]
وَجَاءَ ِفِ اْلَدِيثِ الشهرِيفِ: " إِنه أَوهلَ مَا خَلَقَ هللاُ القَلَمَ ف َقَالَ لَهُ اكْت بْ . ف َقَالَ: َيَ رَب ِ وَمَا
أَكْتُبُ.قَالَ : اكْتُبِ القَدَرَ وَمَا هُوَ كَائِن إَِلَ اْلَبَدِ". ( رَ وَاهُ الَت ِْمَذيُّ وَأَحَْدُ )
2. Alƙalami na biyu: Alƙalami da Allah (SWA) Ya sanar mutãne game da su ta
hanyar mu’ujizar Annabi Idris (A.S), wa ɗanda ake bugu dasu kuma suka gangaro
zuwa ga wannan al’umma ake amfanuwa da ilimin su ta hanyar computer da sauran
digital devices suna daga cikin manya -manyan ni’imõmin Ubangiji da Ya ambata
a cikin Alƙur´ãni mai girma. Allah (SWA) Yace:
( اق ْرَأْ وَرَبُّكَ اْلَْكْرَمُ 3 ( ) الهذِي عَلهمَ َبِلْقَلَمِ 4 ) عَلهمَ اإلِْنْسَانَ مَا َلَْ ي َعْلَمْ
Ka yi ka ratu, kuma Ubangij inka shi ne Mafi karimci. Wanda Ya sanar (da
mutum) game da alƙalami. Ya sanar da mutum abin da bai sani ba. (96:3-5)
99
99
3. Alƙalami na uku: Allah (SWA) Ya ambata, a cikin Alƙur´ãni, alƙalami da muke
sanyawa a cikin tawada muyi rubutu dashi. A yanzu, duk da cewa akwai
alƙalamin rubutun allo na almãjiranci, alƙalamin zãmani shi ne biro. Allah
(SWA) Yace:
وَلَوْ أََّنهَا ِفِ اْلَْرْضِ مِنْ شَجَرَةٍ أَقَْلَم وَالْبَحْرُ َيَُدُّهُ مِنْ ب َعْدِهِ سَب ْعَةُ أَْبُْرٍ مَا نَفِدَتْ كَلِمَاتُ
اّلِلهِ إِنه اّلِلهَ عَزِيز حَكِيم
Kuma dã dai abin da ke a cikin ƙasa duka, na itãce, ya zama alƙalumma, kuma
teku tanã yi masa tawada, a bayansa (tekun, a zõ) da wa ɗansu tekuna bakwai (ayi
ta rubũta kalmõmin Allah ), kalmõmin Allah ba zã su ƙ ãre ba. Lalle, Allah
Mabuwãyi ne, Mai hikima. (31:27)
4. Alƙa lami na hu ɗu: Alƙalami na hu ɗu da Allah (SWA) Ya ambat a mana a cikin
Alƙur´ãni mai girma alƙalami ne (ƙuri’a) da aka kã ɗa zãɓe da shi. Wannan
alƙalami ɗayan biyu ne da muke amfani da shi a wanna n dũniyar; ko dai irin
alƙalami mai amfani da tawada, ko alƙalamin bugun lissafi, Allah (SWA) Shi ne
Masani.
Wannan yana daga lãbarun gaibi, Munã yin wahayinsa zuwa gare ka (Ya
Muhammadu (SAW) ). Ba ka kasance ba a wurinsu a lõkacin da suke jefa
alƙalumansu (domin ƙuri´a) wãne ne z ai yi renon Maryam. Kuma ba ka
kasance a wurinsu ba a lõkacin da suke ta yin husũma . (3:44)
A Lõkacin da mahaifiyar Nana Maryamu ta tafi da ita zuwa ga m asu kula da
(masallacin) Baitul Muƙaddas don a s ãmu mai renonta, husũma tã ɓarke a
tsakanin wa ɗanda su ka cancanci renonta, kõwa yana so ya samu ladan renonta!
Alƙaluma
TEKU
TAWADA ( INK)
100
100
Annabi Zakariyya (A.S) yace nafi cancanta da renonta sabõda Auntyn ta (Ashya’u
wacce suke uba ɗaya da Hannatu –umman Maryam) tana wur ĩna, sai Banĩ Isrã’ĩla suka
ce mũ ma mun dãce mu reni ɗiyar mãlaminm u. Da aka kãsa cimma matsaya, ƙarshe sai
aka yanke shawarar kã ɗa ƙuri’a sabõda aga wanda Allah (SWA) Zai bãshi nasarar zama
mai renonta.
Gudanar da zã ɓen shi ne kowa ya zõ da alƙalaminsa a jefa a cikin kõgi (ruwa) mai
gudãna, wanda ruwa bai tafi da alƙala minsa ba shi ne ya lãshe za ɓe! Annabi Zakariyya
(A.S) shi ne Allah (SWA) Ya zã ɓa ya reni Nana Maryamu (A.S).
Shi irin wannan zã ɓe (na ƙuri’a) da aka gudanar, shekaru masu yawa kafin Annabi
Zakariyya, an gudãnar da irinsa:
Kuma lalle (Annabi) Yũnu sa, haƙĩƙ a, yanã daga Manzanni. A lõkacin da ya gudu
zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi. Sã´an nan ya yi ƙuri´a , sai ya kasance
a cikin wa ɗanda aka rinjaya. (37:141 -)
A lõkacin da Annabi Yunus (A.S) ya kira mutãne nsa (da wa’azi) suka ƙi amsawa har
azãba tayi kusan sauƙa a garin sai ya fita (ya ƙaura). Yana cikin tafiya, har a a lõkacin
da ya shiga jirgin ruwa tare da wassu mutãne domin ya ƙetara teku, sai jirgi ya samu
matsala a tsakiyar teku.
Ya zama dõle a rage lõdi (nauyi) ko a fitar da mai laifin kuskure (tsaka ninsa da Allah)
kafin jirgi da mutãne n cikinsa su tsira, sabõda haka kowa ya amince da yin ƙuri’a. Da
aka kã ɗa ƙuri’a sai ta f ãɗa kan Annabi Yunus (A.S), aka je zãgaye na biyu, uku duk tana
faɗuwa akan Annabi Yunus (A.S). Shi ke nan, dole aka haƙura aka je fa Annabi Yunus a
cikin teku, a wani zancen ya jefa kansa. Yana fã ɗawa cikin teku, Sai kĩfi ya yi lõma da
shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
Allah (SWA) Ya hana kifi karya ƙashin Annabi Y ũnusa da cin naman jikinsa. Haka
Annabi Yunusa (A.S) ya zauna a cikin duffai uku (dufun dare, teku, da cikin kĩfi) har
tsawon kwana arba’in. Sai ya yi kira a cikin duffai , cewa (yayi) : "Lã ilãha illã anta
subhãnaka inni kuntu minaz zãlimin” (21:87).
SHARK
101
101
Allah (SWA) Ya ce:
Sai Muka kar ɓa masa (addu’arsa) kuma Muka tse rar da shi daga baƙ in ciki.
Kamar haka ne Muke tse rar da masu ĩmãni. (21:88).
Allah (SWA) Ya ce:
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba, Lalle dã ya zauna a cikin
cikinsa (ya zama kabarinsa) har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su (a lãhira) .
Tõ a lõkacin da ya ci ka kwana arba’in (wasu suka ce ba biyu), Allah (SWA) Yace:
Sai Muka jefa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya. –Duk
jikinsa yã dafu. (sai) Kuma Muka ts irar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
(Surat us Saffat : 141-148)
A zãmanin yanzu Allah (SWA) Ya sanar da ɗan-Adam hanyõyi masu yawa na kã ɗa
ƙuri’u da lissãfã su ta hanyar amf ãni da digital devices irinsu Card reader da sauransu.
Alhamdulillãhi Rabbil Ãlamin!
102
102
BÃBI NA BAKWAI .
BINCIKEN SARAR IN SAMÃNIYA.
Ba ko ina bane sararin samãniya illa sama mai ɗauke da burujai ! Allah (SWA) Yace:
Inã rantsuwa da sama mai ɗauke da Burujai (guda goma sha biyu) . (85:1)
Ita ce dai sama , wacce Allah (SWA) Ya ƙãwata da fitulũ da tartatsin wutar lantarki
(Yũla). Allah (SWA) Yace:
Kuma lalle Mun ƙawãta saman dũniya da fitillu, kuma Muka sanya su (masu fitar
da tartatsi) abin jifa ga shai ɗãnu, kuma Muka yi musu tattalin azãbar Sa´ĩr (a sũ
shaiɗãnun) . (67:5)
Tun tun tuni ma shai ɗanun aljanu suna zuwa sararin samãniya satar saurãren
maganganun ma lã’iku. Idan shai ɗanu suka sãto maganar M alãiku sai suje wurin bõkaye
su gaya musu abubuwan gaibu da zasu faru (bayan sun ƙara ƙarerayi) . Allah (SWA) Yã
sanya fitulun sama suna jefo tartatsin wuta a she ɗanu idan sun je sama satar saurãre.
Wannan tartatsin wutar muna kiransa “taurãruwa mai wutsiya” a lõkacin da muna yara!
Tũrawa suna kiransa da “ shooting star ” ko “meteor ”, amma a larabce “Shihãbun” Allah
Ya kira ta.
Allah (SWA) Yace:
Lalle Mũ, Mun ƙ ãwatãr da saman dũniya da wata ƙawa (kwalliya) , watau taurãri.
Kuma sunã tsari daga dukan Shai ɗan mai tsaurin kai. Bã zã su iya saurãre zuwa
ga jama´a (Malã´iku) mafi ɗaukaka ba, kuma an ã jĩfar su (da shihãbun) daga
kõwane gefe dõmin tunku ɗewa, kuma sunã da wata azãba tabbatacciya. Fãce
wanda ya fizgi wata kalma (daga zance n malã’iku) , sai yũla (shooting star ) mai
haske ta bĩ shi (ta ƙõna shi) . (37:6 -10)
وَلَقَدْ جَعَلْنَاِفِ السهمَاءِ ب ُرُوجًا وَزَي هنهاهَا لِلنهاظِرِينَ ( 16 ) وَحَفِظْنَاهَا مِنْ كُل ِ شَيْطَانٍ رَجِيمٍ
(17 ) إَِله مَنِ اسَْتََقَ السهمْعَ فَأَت ْب َعَهُشِهَاب مُبِني (سورة اْلجر )
103
103
Bayan da Allah (SWA) Ya sanya taurã rin jifan shai ɗãnu ( masu satar saurãren maganar
Malã ’iku) shaiɗanu sun cika da mãmã ki! Suna hirã sukace: A!
( وَأََنه لَمَسْنَا السهمَاءَ ف َوَجَدَْنَهَا مُلِئَتْ حَرَسًا شَدِيدًا وَشُهُبًا 8 ) وَأََنه كُنها ن َقْعُدُ مِن ْهَا مَقَاعِدَ
لِلسهمْعِ فَمَنْ يَسْتَمِعِ اْلْنَ جيَِدْ لَهُ شِهَاَبً رَصَدًا ( 9 ) وَأََنه َلَ نَدْرِي أَشَرٌّ أُرِيدَ ِبَِنْ ِفِ
اْلَْرْضِ أَمْ أَرَادَ ِبِِمْ رَِبُُّمْ رَشَدًا
"Kuma lalle ne mũ mun nemi (hawan) sama, sai muka, sãme ta an cika ta da tsaro
mai tsanani da kuma yũlãye (taurãrin shooting stars )." "Kuma lalle ne mũ, (a baya )
mun kasance muna zama daga gareta, a wurãren zama dõmin saurare (na
maganar Malã’iku) . To wanda ya yi saurãre a yanzu, zai sãmi yũla (shooting sta r)
mai dãko dõminsa." "Kuma lalle ne mũ (munyi mãmãki ), ba mu sani ba, shin
sharri ne aka yi nufi ga wa ɗanda k e cikin ƙasa (bõkãye da masu neman sanin
gaibu) , ko Ubangijinsu Yã yi nufin shiriya (ne) a gare su ne?" (72:8 -10)
Wallãhi Ubangijinsu Yayi nufin shiriya ne a garesu. Wannan littafin ma nufin shiriya
ne da Ubangiji Ya yi a gare su da mutane bã ki ɗaya. Allah (SWA) Yasa su fahim ta!
FASALI :
7.1 Dũniyar wata da ƴan sama jannati (astro nauts ).
A gaskiyar ma gana, babu wata dũniya ta daban da Allah (SWA) Ya halitta a wani wuri
na daban. Burujai ne kawai (Masauƙai) na wata da magũdãnar rãna da Allah (SWA) Ya
halitta.
وَالشهمْسُ َتَْرِي لِمُسْت َقَر ٍ َلََا ذَلِكَ ت َقْدِيرُ الْعَزِيزِ الْعَلِيمِ ( 38 ) وَالْقَمَرَ قَدهرَْنَهُ مَنَازِلَ حَىته
عَادَ كَالْعُرْجُونِ الْقَدِيِ
Burujai guda gõma sha biyu ne! kowane bayan kwana talatin (30 ko 29) wata yana canza
Buruji (manãzil) , haka abin yake tun farkon halittar dũniya!
إِنه عِدهةَ الشُّهُورِ عِنْدَ اّلِلهِ اث ْنَا عَشَرَ شَهْرًا ِفِ كِتَابِ اّلِلهِ ي َوْمَ خَلَقَ السهمَاوَاتِ وَاْلَْرْضَ
مِن ْهَا أَرْب َعَة حُرُم ذَلِكَ الد ِينُ الْقَي ِمُ فََلَ تَظْلِمُوا فِيهِنه أَن ْفُسَكُمْ ...
104
104
Lallai ne ƙidãyayyun watanni a wurin Allah wat ã gõma shã biyu ne a cikin Littãfin
Allah, (tun) a Rãnar da Ya halicci sammai da ƙasa , daga cikinsu akwai hu ɗu mãsu
alfarma. Wannan ne addini madaidaici , Sabõda haka kada ku zãlunci kanku a
cikinsu … (9:36)
A mahangar Astronomers (masu binciken sandararrun halittun da suke sama), bayan
rãna da wata, akwai manya -manyan masauƙai masu kama da dũniya da aka musu sũna
da Mercu ry, Venus , Earth , Mars , Asteroids , Jupit er, Saturn , Uranus , Neptune , da Pluto .
A nãsu tunãnin, dukkan wa ɗannan dũniyõyi (guda goma) suna kewaya rãna ne sannan
wata kuma yana kewaya dũniyar da muke ciki. Amma a wajen Astrologers (Tũrãwan
kirdãdon sanin gaibu), rãna da wata duka taur ãri ne sannan kuma akwai Burujai ( Zodiac )
guda gõma sha biyu (12) .
Shi wata, ba wani girma n e dashi wanda za a hau a kafa tũ tõti ba! Kuma kõ da mutãne
sun sãmu damar hawa zuwa sama, to bã zã su wuce yand a shai ɗanu suke zuwa satar
saurãre ba. Ai mafi yawan hatsabĩ banci shai ɗanu suke kõ yar da mutãne .
وَأَنههُ كَانَ رِجَال مِنَ اإلِْنْسِ ي َعُوذُونَ بِرِجَالٍ مِنَ اْلِْن ِ ف َزَادُوهُمْ رَهَقًا
"Kuma lalle ne shi wasu maza daga cikin mutãne, sun kasance sunã neman tsari
(na taimako ) da wasu maza daga cikin aljannu, sabõda haka (mutanen) suka ƙ ãra
musu girman kai (a alja nnun) ." (72:6 )
Cikin watanni biyu da suka gabãta, wassu sunyi rubũtu akan ƙaryar zuwa wata da suke
zargin NASA (Amurka ) da shi ryawa. Sunyi bay ãnin cewa akan shirya dũniyar watan
ne a computer da fasaha irin ta croma key da sauransu sannan a fitar da film ɗin a
mutanen d ũniya. Sun kuma bayyana cewar as ĩrin ƙaryar zuwa dũniyar wata ne yake
tõnuwa. Dũba ƙãrin bayani a wannan shafin : How Could the Moon Landing Be Faked ?
7.1.1 Mutum -mutumĩ da taurãron ɗan-Adam (Robotism and Satellites ).
Kasancewar an lũra komai nisan jifa ƙasa yake fãɗõwa, akwai wani fili a sararin
samãniya ionosphere mai dãwo da iskar maganganun rediyo ( Radio (electromagnetic )
waves ). Idan aka harba lãbãrai daga rediyon BBC zuwa sama, a can ionosphere ne zai
jũyo ya watsu zuwa ƙasãshe daban -daban. To sai dai ionosphere tana shanye ƙarfin
lãbarun rediyo da ake aikawa sama, sabõda haka ne aka ƙirƙiro dabarar taurãron ɗan-
Adam ( satellite ) wacce za ta zauna a sama tana aiki fiye da na ionosph ere.
105
105
Ita satellite , ana harbata sama ta riƙa yãwo a can sabõda kar ta fãdo. Aikinta shine tana
karɓar iska mai ɗauke da bayanai (na rediyo, TV, GSM da sauransu) sannan ta ƙara
musu karfi ( amplif ication ) kafin ta jefasu wassu ƙasashen na daban. Satellite ta na
amfani da hasken rana ne ( solar ) wajen sarrafa kanta da zirga -zirgar yau da kullum .
Rõka (Rocket ) ita ce ake harbawa takai satelliate can sama . Kuma kar ka manta, fasahar
ilimin alƙaluma ne yayi satellite gaba ɗayanta!
Robot shĩne duk wani inji ƙ irar gaɓõɓin ƙarfe (ko na rõba da itãce) wanda aka ha ɗashi
da kã yan wutar lantarki kuma yake aiki irin na mutãne. Robot mai siffar gunkin mutum
shi aka fi sani da robot na asali (mutum -mutumi) . Ana yin amfani da robot kwarai wajen
sama -jannati da sauran ayyukan hatsari ko wa ɗanda ake son aikinsu ya kasance da sauri,
har ma da kayan wasan y ara!
7.2 Geography: Fannin ilimi ne da ya ƙunshi nazarin mutum da dũ niyarsa ( man and his
physical environment ). A abubuwan da suka shafi sama, geography yana nazarin
yanayin tsakanin sama da ƙasa ( atmosphere ) da girgije ( clouds ) da duwãtsu da
ma’ãdanai da aka gina masauƙan watã da su (gami da taurãri)!
Mahangar geographers irin ta Astronomers ne–dũniyõ yi tara masu ɗawãfin (kewaya)
rãna– amma wajen lũra da yanayin girgije da iskõkin da ke ka ɗashi, masana geography
sun yi bayãnai masu yawa.
ROBOTS
Taurãron ɗan-Adam (Satellite)
Rõka (Roket)
106
106
Lũra da sararin samãniya, shekaru arũ -arũ, yasa masana geography suka fahimci siffõfin
girgije kala -kala suka sa musu sũna : kulun-manimbus (Cumulonimbus ), kumulus da
sauransu.
Lũra da girgije (na tsawon shekaru) yasa masana geography kan rarrabe hadarin kãkã
(kaka’ a) da hadarin dãmina har a t sammaci ruwa daga garesu. Tsammanin ruwan sama
daga na u’ikan hadari (girgizai) ba sãbon abu bane.
A lõkacin da Ãdawa suka ƙi musulunta, Allah (SWA) Yayi nufin hallakã su, sai suka
ga wata Iska mai duhu kamar hadirin “kulun -maninbus ”.
ف َلَمها رَأَوْهُ عَارِضًا مُسْت َقْبِلَ أَوْدِيَتِهِمْ قَالُوا هَذَا عَارِض ِمُْطِرَُنَ بَلْ هُوَ مَا اسْت َعْجَلْتُمْ بِهِ رِ يح
فِيهَا عَذَاب أَلِيم
To, a lõkacin da suka ga azãbar (iskar) , kamar hadari (irin nau’in “kulun -
maninbus ” yana ) mai fuskantar rãfukansu, suka ce: "Wannan hadari ne mai yi
mana ruwa. (Annabi Hũdu yace): ôa, (ba hadarin ruwã bane) shĩ na abin da kuke
neman gaggawar saukarsa ne; Iska ce (zur), a cikinta akwai wata azaba mai
raɗaɗi. (46:24)
سَخهرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وََثََانِيَةَ أََيهمٍ حُسُومًا فََتََى الْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَى كَأََّنهُمْ أَعْجَازُ َنَْلٍ
خَاوِيَةٍ ( 7) ف َهَلْ ت َرَى َلَُمْ مِنْ َبَقِيَةٍ ؟
(Allah) Ya hõre ta (iskar mai tsananin sauti) a kansu , a cikin dare bakwai da yini
takwas biye da jũna, sabõda haka, (sai gãshi) kana ganin mutãne a cikinta kwance
kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, wa ɗanda suka fã ɗi. To, kõ kanã ganin abin da ya
yi saurã daga cikinsu? (69:7 -8)
Sabõda haka shĩ tsammanin ruwan sama a lõkacin da aka ga wani hadari ba kamar
tsammaninsa idan anga wani taurãro ya bayyana bane! Tsammãnin ruwan sama sabõda
kãmawar taurãro kafi rci ne amma tsammaninsa idan anga baƙin hadari mai walƙiya ba
laifi bane , sabõda Allah (SWA):
107
107
Shĩ ne Wanda Yake nũna muku walƙiya dõmin tsõro da tsammãni (na ruwan
sama) , kuma (Shĩ) Yake ƙãga halittar girãgizai mãsu nauyi (irin su “kulun -
manimbus ”). (13:12)
7.2.1 Weather forecast (Harsãshen yanayi) irin na masana geography na ranar da ake
ciki (idan an hangi haɗuwar hadari ta satelliate da sauransu) ba laifi bane (kamar irin
tsammãnin da nayi bayani ne), haka kuma tsammanin wani abu na dãmina da hanyar
lũra da ka ɗawar iska.
Cikin d ukkan wa ɗannan bincike na geographers , ka ce:
1. Halittar sammai da ƙasa (Religion geography ).
2. Sãɓãwar dare da yini a ƙasãshen dũniya (Geography of Time Zones ).
3. Teku da tsibiran cikinta , iska mai kaɗa jiragen ruwa (Oceanography ).
4. Ruwan sama da irin yadda yake haɗa dãji (Natural Afforestation ).
5. Jũyãwar iskõki da girgije tsakãnin sama da ƙasa (Atmospheric circulation ).
6. Duhuwar wurãren zama Ecosystem .
Ga dukkan wa ɗannan akwai abubuwan lũra ga wanda yake yana da hankali da tunãni.
Allah (SWA) Yace:
إِنه ِفِ خَلْقِ السهمَاوَاتِ وَاْلَْرْضِ وَاخْتَِلَفِ اللهيْلِ وَالن ههَارِ وَالْفُلْكِ الهيتِ َتَْرِي ِفِ الْبَحْرِ
ِبَِا ي َن ْفَعُ النهاسَ وَمَا أَن ْزَلَ اّلِلهُ مِنَ السه مَاءِ مِنْ مَاءٍ فَأَحْيَا بِهِ اْلَْرْضَ ب َعْدَ مَوِْتَِا وَبَثه فِيهَا
مِنْ كُل ِ دَابهةٍ وَتَصْرِيفِ الر َِيَحِ وَالسهحَابِ الْمُسَخهرِ بَنيَْ السهمَاءِ وَاْلَْرْضِ ْلََيَتٍ لِقَوْمٍ
ي َعْقِلُونَ
Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa, da sã ɓãwar dare da yini, da jirãge
wada ɗanda suke gud ãna a cikin teku ( ɗauke) da abin da yake amfãnin mutãne, da
abin da Allah Ya saukar daga sama daga ruwa, sai Ya rãyar da ƙasa da shi a bãyan
mutuwarta, kuma Ya wãtsa, a cikinta, daga dukan dabba, kuma da jũyãwar i skõki
da girgije hõrarre a tsakãnin sama da ƙasa; haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne mãsu
yin hankali. (2:164)
TABBAS!
Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa da sã ɓãwar dare da yini akwai ãyõyi ga
ma´abũta hankali. (3:190)
108
108
…har sanda asuba ta gab ãto, Manzon Allah (S AW) yana kũka a cikin sallar dare! Bil ãlu
yace: Ya Rasũlullãhi! Me zai s ãka kũka alhãli Allah Yã gãfarta maka abinda ya gabãta
da wanda ya rage? Manzon Allah (S AW) yace Haba Bilãlu , me ze han ãni kũka Allah
Ya sauƙar a cikin wannan dãre:
إِنه ِفِ خَلْقِ السهمَاوَاتِ وَاْلَْرْضِ وَاخْتَِلَفِ اللهيْلِ وَالن ههَارِ ْلََيَتٍ ْلُِوِلِ اْلَْلْبَابِ
Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa da sã ɓãwar dare da yini akwai ãyõyi ga
ma´abũta hankali. (3:190)
Tur da mutu min da ya kara nta wagga ãya bai yi tunãni a cikin ta ba.
(na kimiyyar science da take ɗauke da shi )
(Sahĩhun)
ت َفَكهرُوا ِفِ خَلْقِ اّلِلهِ وََلَ ت َفَكهرُوا ِفِ اّلِلهِ
وَِفِ اْلَْرْضِ آَيَت لِلْمُوقِنِنيَ ( 20 ) وَِفِ أَن ْفُسِكُمْ أَفََلَ ت ُبْصِرُونَ
Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu ya ƙĩni. Kuma a cikin rãyukanku (akwai
ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba? (51:20)
Tabbas a karan kan mutum akwai anatomy na ban mamaki !
Bari mu dawo daga hũtun rabin sã ’a, in sha Allahu sai mu
dũba:
( سُبْحَانَ رَب ِكَ رَب ِ الْعِزهةِ عَمها يَصِفُونَ 180 ( ) وَسََلَم عَلَى الْمُرْسَلِنيَ 181 )
وَاْلَْمْدُ ّلِلِهِ رَب ِ الْعَالَمِنيَ
bamagaj@gmail.com
Ana loda PDF...