H - HANYOYIN SAMUN GAFARA [b0de7885]
H - HANYOYIN SAMUN GAFARA [b0de7885]
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
1
Dukkan yabo da godiya da jinjina da kiraari da kuma neman yarda
sun tabbata ga Allah Maxaukaki. Muna jadda da godiyarmu gareShi
a bisa ni’imomin nan naShi marasa qididdiguwa. Kuma muna
neman taimakonS a ako da yaushe (kuma akan komai). Muna ku ma
neman Ga fararSa . Muna kuma nema n tsarinSa daga sharrorin
kawunanmu da kuma miyagun ayukanmu. Muna roqon Shi da Ya
sanya mu cikin bayinSa waxanda Ya shiryar, Ya kuma tabbatar da
mu akan wannan Tafarki na Shiriya har mutuwa (har abada).
Tsira da Amincin A llah su qara tabbata ga ManzonSa
Muhammadu, shi da iyalansa da Sahabbansa, da sauran duk
waxanda suka biyo bayansu da kyautatawa, har zuwa ranar
sakamako. Da fatan Allah Yasa mu ma muna cikinsu .
Bayan haka :
Sanannen abu ne dai kowa daga cikinmu yana aika ta laifi. Mu duka
muna da zunubai, domin kuwa muna sava wa Allah dare da
rana. Saboda haka kowannen mu y ana da matuqar buqaatar samun
Gafarar Allah Mabuwayi Maxaukaki, don ya samu rabuwa da
waxannan zunubai da yake kannaxe dasu ko ta ina.
Daga cikin Rah amar Allah ga bayinSa, Ya yawaita musu Hanyoyin
Samun GafararSa . Kuma babu wanda zai bi su fahce sai Ubangiji
Mabuwayi Mai Jinqai Ya game shi da GafararSa, kuma sai Ya
lulluve shi da yalwatacciyar RahamarSa wacce ta wadaci komai.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
2
Haqiqa mai lafiyayyen hank ali daga cikin mutane shi ne wanda
yake gaggawar komawa ga Majivincin al’amuran kowa da komai,
ta hanyar riqo da hanyoyin samun Gafararsa (waxanda babu
makawa sai an bi su kaafin a samu biyan buqata).
Ya xan -uwa mai girma! Insha’Allahu Waxannan ‘yan shafu kan
da kake dab da fara karantawa za su qunshi bayani akan wasu daga
cikin Hanyoyin Samun Gafarar Allah (ga duk wanda yabi su kamar yadda
Shari’a tayi bayani). Da faatan Allah Yasa mu cikinsu.
Allah Yasa mu d ace.
Hanyoyin samun Gafara suna da matuqar yawa sosai. Amma zan
kawo mana guda goma daga cikinsu insha’Allah, daga cikin
waxanda malamai masu yawa sun nun a cewa su ne sukafi
muhimmanci.
Su ne kama r haka:
Tuba;
Neman gaafara;
Shiga Musulunci;
Nagartaccen Imani;
Biyayya ga Manzon Allah, da nisantar sava masa;
Sauran ayuka nagari (irinsu rukunan Musulunci da sauransu) ;
Haqurin bawa a bisa wata jarrabawar da ta same shi;
Addu’ar Mumini ga Mumini (m usamman roqa masa gafara);
Ceton Manzon Allah a gobe Qiyamah;
Afuwar Allah ga wanda Ya ga dama cikin bayinSa..
Waxanna n dai su ne manyan kashe kashen. A qarqashin wasu
daga cikinsu kuma akwai wasu qananan kashe -kashe, waxanda za
a ga kowanne a wu rinsa Insha’Allahu.
Da farkon f ari zan fara da roqon Ubangiji Maxaukaki Ya arzu kta
ni da ikhlasi Ya kuma d atar dani wajen gabatar da abinda Zai yarda
dashi, Yasa shi a mizanin kyawawan ayuka, kuma Ya G afarta mana
laifukanmu da kurakuranmu (daga mu har iyayenmu da iyalanmu
da malamanmu da duk sauran ‘yan -uwa mu musulmi baki xaya).
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
3
Ina roqon Allah Mai Karimci Ya sanya mu baki xayanmu cikin
bayinSa masu tsoronSa, masu tsare dokokinSa, masu lafiyayyen
hankalin nan waxanda suke tuban gaske su koma gareShi..
Allah Yasa mu cikin masu kyautata niyyah a yayin aikata duk
wani a ikin da muka sa a gaba, da kuma baki xaya abinda zamu
furta.
Allah Yasa mu cikin bayinSa waxanda Ya tsare su daga sharrin
shaixan, kuma Ya kuvutar damu daga aikata duk abinda zai jawo
mu afka cikin fushinSa da uqubarSa a duniya da lahira. Lallai Shi
Majiy i ne, kuma Mai amsa roqon bawa.
Xan-uwan ku a Musulunci:
Musa Muhammad Sallau Jada
(
Aboomaryam Aljaadawiy
)
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
4
(Hanyoyi Biyu Na Farko)
Kalmar Tuba tana nufin: komawa ga Allah ta hanyar nisant ar
ayukan savo , da kuma neman y afiya daga gareShi.
Ita ma kalmar Istighfa ri tana nufin neman g afarar Allah daga
zunuban da bawa ya aikata . Allah Ya umurce mu da mu
gaggauta Tuba zuwa gareShi. Kuma Ya yi a lqawrin Zai Yafe
mana zunuban mu matuqar munyi hakan. A cikin Suratut -
Tahrim (ayah ta 8) Allah Yana cewa :
[
ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟ
ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ ﭬ ﭭ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ
ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ
]
‚Ya ku waxanda sukayi imani! Ku tuba zuwa ga Ubangijinku
tuba irin na gaskiya. Akwai tabbacin cewa Ubangijinku Zai
kankare m uku munana n ayukan ku, kuma Zai shigar da ku
Aljannatai waxanda koramu ke gudana a qarqashi nsu. A wannan
rana Allah ba Ya kunyata Annabi da waxanda sukayi imani dashi.
Haskensu yana gudana ta gabansu da kuma bangarorinsu na
dama, suna cewa Ya Ubangijinmu Ka cika mana haskenmu, kuma
Kayi mana Gafara, domin k uwa lallai Kai ne mai iko a kan dukkan
komai ‛.
Mu gaggaut a tuba, mu yawaita neman gafara. Domin kuwa
‚Duk wani xan Adam mai kuskure ne. kuma mafiya alkhairi
1.‛ daga cikin masu kuskuren nan, su ne masu tuba
Manzon Allah dai shi yafi kowa yawan Istighfari, tare da
kuma shi yafi kowa matsayi gun Allah , haka kuma shi yafi
kowa tsoron Allah da kuma tsare dokk inSa.
1 (Ahmad: 13072 ), (Tirmidhi: 2499), (Ibn majah: 4251) Daga Sahabi Anas xan Malik
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
5
Allah Ya tabbatar masa cewa Ya riga Ya yafe masa duk
wani abinda ya gabata na zunubansa2 (ballentana da m a bai yi
ba), Ya kuma yafe masa abinda zai yi nan gaba ma (tare da
kuma ba zai tava yin laifi ba har abada) amma duk da haka ya
fi kowa neman gafarar Allah . Akullum kuma ya kasance
yana qara zaburar da al’ummarsa wajen d agewa akan haka
sosai da sosai. Ingantattun H adisai masu yawa sun tabbatar da
hakan , cikin manyan littafan Hadisi daban daban . Shi da
kansa ma yake cewa: ‚Wallahi ni (da kaina) ina Neman
Gafarar Allah kuma ina Tuba z uwa gareShi sama da sau 70 a
yini guda3‛
Manzon Allah yana ma yin Istigh fari sau xari a zama guda,
banda waxanda yakeyi a sauran wurare da lokuta daban -
daban. Sahabbai suka ce a duk inda ya zauna, yana yawaita
faxin:
رَبِّ اغْفِرْ لِي وَتُبْ عَلَيّ، إِنّكَ أَنتَ الت َّوّابُ الرّحِيمُ
‚Ya Ubangiji Kayi min G afara kuma ka karvi tuba na, domin
kuwa Kai ne Mai Yawan karvan tuan nan, Kai ne kuma Mai
JinQai‛
Sahabi Abdullahi xan Umar (Allah qara yarda das u) yace sun
kiyaye Manzon Allah yana maimaita wannan addu’a har
sau xari a zama guda4.
Manzon Allah yace ‚Ya ku mutane! ku Tuba zuwa ga
Allah kuma ku nemi Gafarar Sa. domin ni ma (da kaina) ina
5Tuba zuwa gareShi har sau xari a rana
‛
Allah Ya yi alqawarin Gafarta wa duk wanda ya Tuba ya
koma gareShi. Kum a Zai sanya shi cikin waxanda Yakeso,
domin kuwa Yana son masu Tuba.
2 Duba: Suratul -fat’hi ayah ta biyu (2)
3 Bukhari (hadithi na 6307), daga Sahabi Abu -Hurairah
4 Duba: Sunan Abi -Dawud (hadithi na 1516) Hadithi ne ingantac ce.
5 Saheeh Muslim (Hadithi na 2702 ). Daga Sahabi Al -Agharru xan Yasaaru
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
6
Ya faxi hakan ne a cikin Suratul -Baqara (ayah ta 222) inda
Yake cewa:
[
ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ
]
]
ابلقرة
:
222[
‚..Lallai allah Yana son masu yawan tuban nan, kuma Yana son
masu (kyautata) tsarki .‛
Saboda irin tsant sar Son da Allah Yake wa masu Tuba zuwa
gareShi m a, Yana matuqar farin -ciki6 sosai da bawanSa idan
har ya tuba ya koma gareShi, fiye da irin farin -cikin da
xayanmu zai yi idan dabbarsa ta gudu da abincinsa ta bar shi
a tsakiyar daji sannan sai ta dawo gareshi a daidai lokacin da
ya gama xebe tsammanin ci gaba da rayuwa7.
Saboda haka aka umurcemu idan muka gama alwala mu
riqa cewa:
اللَّهُمَّ اجْعَلْنِي مِنَ الت َّوَّابِينَ وَاجْعَلْنِي مِنَ الْمُتَطَهِّرِينَ
‚Ya Allah Ka sanya mu cikin (bayin nan n aka na gari) masu
yawan tuba, Ka kuma sanya mu cikin masu tsarki
8
(waxanda Kace Kana son su)‛
Allah
Yace Ya na son masu tuba su koma gare Shi, kuma
Yana son masu k yautata tsarki. Wannan kaxai ma isa ya
zama dalilin da zai sa mu gaggauta tuba.
Sananne n abu ne Tsarki mafi girma shi ne tsarkak uwa daga
dattin shirka da kafi rci da munafunci, da qazantar zunubai
da dauxar miyagun ayuka.
Toh tuba zuwa ga Allah da kuma neman gafararSa,
suna daga cikin manya -manyan hanyoyi na samun irin
wannan Tsarki mafi daraja.
6 Farin ciki irin wanda ya da ce da Shi Allah .
7 Bukhari ( 6309 ), Muslim ( 2747 ). Daga Sahabi Anas xan Malik
8 Tirmidhi (Hadisi na 55) Daga Sayyidina Umar
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
7
Wannan dai a taqaice shi ne bayani akan tagwayen
hanyoyin nan biyu na farko daga cikin Hanyoyin Samun
Gafarar Allah
, wato Tuba Da Kuma Istigfari .
Da fatan Allah Ya sanya mu cikin bayin nan naShi
waxanda Yakeso, masu kyautata tsarki (na bayyane da
na voye) kuma masu Tuba su koma gareShi Tuba na
gaskiya.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
8
Musulunci sh i ne mafi girman ni’imar da Allah Yayiwa
bawanSa. Shi ne kaxai tafarkin da bawa zai bi don ya samu
Alkhairan duniya da lahira. Shi ne kaxai Tafarkin ts ira. Shi
ne kaxai yardajjen Addini a wajen Allah . Domin kuwa
Shi Ya bada tabbacin hakan acikin Littaf inSa Mai Tsarki .
Acikin Suratu Ali-‘Imran (ayah ta 19) Allah Yace :
[
ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ
]
]
آل عمران
:
19[
‚Lallai Musulunci shi ne kaxai (karvavven) Addini a wajen Allah ‛
Acikin dai Suratu Ali-‘Imran xin, Allah Yace ba Zai
karvi aikin duk wanda ya bauta maSa da wani addini koma
bayan Musulunci ba. Ya faxi hakan ne a cikin ayah ta 85,
inda Yake cewa:
[
ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ
]
‚Kuma duk wanda ya riqi (wani tafarki na daban) koma bayan
Addinin Musulunci, toh fa ba za a karva daga gareshi ba. Kuma
shi xin a (ranar) lahira zai kasance cikin hasararru ‛
Musulunci sharaxi ne babba daga cikin manyan sharuxan
karvan duk wani aikin da bawa zai gabatar a rayuwarsa . Shi
ne kuma hanya mafi girma daga cikin hanyoyin samun
Gafara. Dole kuma sai bawa ya bi wannan hanya (kuma ya
inganta ta) kafin sauran hanyoyin ma su amfane shi.
Daga cikin dalilai mafiya qarfi akan hakan, Allah Ya kira
musulunci da sunan tuba a cikin wasu gwala -gwalan ayoyi
na Al -Qur’ani Mai girma. Ga kaxan daga cikin misalai
gameda hakan insha’Allahu.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
9
A cikin Suratut -Taubah ( ayah ta 5) Allah Yana cewa:
[
ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ
ﯥ
]
‚Idan har (kafiran nan) suka tuba (suka musulunta) kuma suka
tsaida sallah sannan suka b ada zakkah, toh ku rabu da hanyar su
(ku qyale su, kar ku yaqe su). Domin kuwa A llah Mai g afara ne
mai jinqai ‛
Allah Ya hana mu yaqa rsu, saboda tuban da sukayi
daga kafircin nasu. Daga tuban nan da sukayi dai, toh
shi kena n sun zama ‘yan -uwan mu na addini.
Shi yasa a wata ayah ta daban kuma9 Yake cewa:
[
ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ
ﮤ ﮥ ﮦ
]
‚Idan har suka tuba (suka bar kafircin n asu) kuma suka tsaida
Sallah sannan suka b ada Zakkah, toh (daga nan) sun zama ‘yan -
uwanku na addini. Kuma Muna rarrabe ayoyin nan ne (dalla -
dalla) ga mutane don su sani ‛..
Acikin Suratul -Furqan ma, Allah Ya kira Musulunci da da
sunan Tuba , a inda Yayi bayanin halayen bayinSa na qwarai.
Yace su ne waxanda basu shirka ku ma basu kisan kai sannan
kuma basu yin zina.
Sai Yayi bayanin munin laifin duk wanda ya aikata
waxannan miyagun ayuka masu halakarwa a duniya da
lahira, domin kuwa za a ninka azaba ga duk wanda ya aikata
su.
Sannan sa i Yace:
9 At-Taubah (aayah ta 11)
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
10
[
ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ
ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ
]
‚..Sai kaxai wanda ya tuba (daga cikinsu) kuma yayi imani
kuma ya aikata aiki na qwarai, toh (irin) waxannan za a sauya
munanan ayukan su zuwa ga kyawawa (za a yafe musu
zunubansu, kuma a maye gu rbinsu da ladan kyawawan ayuka).
Saboda Allah Ya kasance Mai yawan Gafara kuma Mai Jinqai..
kuma duk wanda ya tuba kuma yayi aiki na qwarai, toh lallai
(haqiqa wannan) ya koma ga Allah matuqar komawa ‛.
A Suratul -Anfal (ayah ta 38) Allah Yana cewa ManzonS a :
[
ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ
ﮱ ﮲ ﮳
]
‚Kace wa waxanda suka kafirta in har sun hanu (sun tuba sun
daina wannan kafircin nasu) toh za a gafarta musu (duk) abinda
ya gabata (na zunubansu). Idan kuma suka koma (suka cigaba da
kafircin nasu bayan sun ce sun tuba), toh haqiqa hanyar
mutanen farko (kafiran da suka gabata a tarihi) ya riga ya shuxe
(za Mu yi musu irin yadda Mukayiwa magabatan su a kafirci) ‛
In har wannan shi n e alqawarin Allah ga kafirai i n har suka tuba
daga kafirci, ashe kenan mu Musulmi m u ne muka fi dacewa
muyi gaggawar komawa gareShi gaba xaya saboda mu rabau ta.
Babu ko shakka Musulunci yana daga cikin manyan hanyoyin
samun Gafara. Domin kuwa yana rusa duk laifin da bawa yayi
kafin musuluntarsa (y ana shafe duk zunubin da bawa ya aikata
acikin kafirci ).
Haka Manzon Allah Ya faxa wa Sahabin sa Amru xan
‘As , inda yake ce masa:
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
11
‚Shin baka san cewa musulunci yana rusa duk wani abinda
10ya kasance k afin shi (na zunubai) ba?
Mun gode wa Allah Ta’ala akan wannan babbar ni’ima ta
Addinin musul unci. Muna f ata Allah Ya raye mu akan ta,
Ya tsare mana imanin mu, Yasa mu cika da imani, yasa mu
cikin bayin nan n aShi masu rabauta a duniya da l ahira.
10 Duba Saheeh muslim (hadithi na: 121)
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
12
Imanin gaskiya, shi zai sa bawa ya tsaida ing antaccen
Tauhidi. Shi zai sa bawa ya tsare dokokin Allah . Shi zai
sa bawa ya nisanci savon Allah (sawa’un a bayyane ne ko a
voye). Imani y ana kuma daga cikin manya n hanyoyin
samun Gafarar Allah .
Idan muka duba wasu ayoyin Al -Qur’ani Mai Girma, za mu
ga inda Allah Yake yabon wasu bayinSa masu gaskiya
cikin imaninsu, ce wa su kam su na ma yin tawassuli da
imanin nasu wajen neman GafararSa (da kuma neman
tsarinSa daga azabar wuta a gobe qiyamah) .
Wannan yake nuna ashe nagartacce n imani ma yana
daga cikin hanyoyin samun g afara, tunda har ana
tawassuli da shi waj en neman tsira a duniya da lahira .
Za mu ga misalign hakan a cikin Suratu Ali-Imran (ayah
ta: 193), inda Allah Yake cewa (a harshen bayinSa
masu imani):
[
ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥ ﯦ ﯧ
ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ
]
Allah Yace (su waxannan Muminai suna cewa): ‚Ya
Ubangijinmu! Lallai mu mun ji wani mai kira yana kira
zuwa ga imani, yana cewa kuyi imani da Ubangijinku , mu
kuma sai mukayi imani (kamar yadda ya umurce mu).
Saboda haka (muke roqonKa) Ya Ubangijinmu Ka Gafarta
mana zunubanmu, Ka kankare mana munanan ayukanmu,
kuma Ka karvi rayuka mu tare da mutanen kirki (masu yi
maka xa’a) ‛..
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
13
Bayan Allah Ya faxi wasu daga cikin siffofin su a farkon
Suratul -Anfal (kuma Ya tabbatar musu da cewa Ya yarda da
ingancin imanin nasu kuma Ya karvi ayukansu ) sai Yace:
[
ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ
]
‚Waxannan su ne muminai na gaskiya. Suna da wasu darajoji
(maxaukaka) gun Ubangijinsu, tare da Gafara, da kuma wani
irin (yalwataccen) arziki mai girma (daga Ubangiji Mai Karimci
da Baiwa ga bayinSa nagari) ‛..
Kamar yadda suke aikata duk abinda aka umurcesu na
wajibai (har ma da nafilfilu), haka kuma suke matuqar
nisantar duk wata hanyar da za ta sa su afka cikin miyagun
ayukan nan masu halakarwa.
A kullum s una matuqar nisantan waxannan manyan laifuka
ne saboda Tsoron Allah da suke yi , da kuma fatan samun
RahamarSa .
Allah Ya yabe su akan hakan, kuma Ya tabbatar musu
cewa wannan xin wata hanya ce ta samun GafararSa.
A cikin Suratun -Najmi (ayah ta 32) Allah Yace :
[
ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﯡ
]
‚..(Su ne) masu nisantar manyan laifuka (kaba’irai) da
abubuwan alfasha (iri n su zina da kuma miyagun kalamai),
sai dai qananan laifuka (wannan kam zamiya tana kaisu ga
aikatawa). Toh lallai Ubangijinka Mai yalwatacciyar Gafara
ne‛.
wannan gava dai tana qara tabbatar wa masu imani ne cewa
matuqar sun nisanci waxannan manyan laifuk a, matuqar
sun tsare dokokin Allah sun ji tsoronSa, toh Zai gafarta
musu zunubansu.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
14
Ma’ana : Allah Zai Gafarta musu laifukansu saboda
inganta imaninsu da sukayi, da kyautata alaqarsu daShi
da sukayi ta hanyar aikata abinda Ya umurce su, da
kuma nisantar manyan laifukan nan da Ya hanasu
aikatawa.
Sanannen abu ne cewa Shirka ita ce mafi girma (mafi
muni, kuma mafi haxari) daga cikin waxannan manyan
laifuka11.. Toh duk wanda ya nisanci shirka da sauran
miyagun ayukan nan, kuma ya dage wajen yawaita
ayuka nagari (tsakanin farillai da nafilfilu), Allah
(cikin FalalarSa da yalwatacciyar RahamarSa) Zai yafe
masa sauran laifukan da ya aikata.
Allah Ya yi alqawarin hakan a cikin Suratun -Nisa’i
(ayah ta: 31) inda Yake cewa:
[
ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ
ﮜ ﮝ ﮞ
]
‚Idan har kuka nisanci manyan laifukan (nan) da aka hane
ku aikatawa (saboda Tsoron Allah); toh za Mu kan kare
muku munanan ayukanku, kuma za Mu shigar daku (wata
irin babbar) mashiga ta karimci .‛
Sannan kuma Ya yi alqawarin gafarta wa bayin nan
naShi masu tsoron fakewa daga idanun mutane don su
sava maSa, waxanda suka fifita neman YardarSa akan
ta mutane.
11 Duba Saheehul -bukhari (hadithi na 2654 , da 6861 ), Abu -Dawuda da Tirmidhi ma sun
ruwaito shi..
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
15
A cikin Suratul -Mulk (aya ta 12) Allah Yana cewa:
[
ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃ ﰄ ﰅ ﰆ
]
‚Lallai waxanda suke tsoron Ubangijin su a voye (masu tsoron
vuya su sava maSa, saboda yaqinin da suke dashi akan lallai Yana
ganinsu, kuma suna jin kunyarSa); toh suna da wata irin gafara
(mai yawa) da kuma wani irin sakamako mai matuqar girma (daga
wajen Ubangijin n asu Maxaukaki) .‛
Ko shakka babu duk wanda ya doshi aikata wani aikin savo
a voye, sannan sai ya bar wannan aikin saboda ya tuna cewa
ai Allah kam Yana ganinsa, wannan bawan Allah yana da
imani mai qarfin ga ske.
Shi yasa Allah Yace duk mai irin wannan hali toh Ya yi
masa alqawarin G afara da kuma lada mai yawa.
Allah Ya ma ce Aljannah ce makomar duk mai irin
wannan halin.
Haka Ya faxa a can wajen qarshen suratun -Nazi’at (ayah ta
40-41) inda Yake cewa:
[
ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ ﯯ ﯰ ﯱ ﯲ ﯳ ﯴ ﯵ ﯶ ﯷ ﯸ
]
‚Amma duk wanda yaji tsoron tsayuwa gaban Ubangijinsa
(a gobe qiyama) sai ya hana kansa aikata abinda ransa
yakeso (na laifi); toh lallai aljannah ita ce makoma (ga irin
waxannan bayin Allah masu imanin gaskiya) ‛
Kuma Ya yi alkaqwarin cewa in har bawa ya tsare
dokokin Sa kuma Yaji tsoron sa a ko wanne hali, toh Zai
datar da shi da daidai a cikin al’amuran sa na addini da
rayuwa, kuma Zai gafarta masa zunuban sa.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
16
Allah Ya faxi hakan ne a cikin Suratul -Anfal (ayah ta
29) inda Yake cewa:
[
ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ
ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ
]
‚Ya ku waxanda kukayi imani! In har kun tsare dokokin
Allah (kunji tsoron Sa) toh Zai sanya muku mararraba12,
Kuma Zai kankare muku qananan laifukan ku, kuma Zai
Gafarta muku (manyan laifukan ku). Domin kuwa Allah
Ma’abocin falala ne Mai Girma. ‛
Da fatan Allah Yasa da mu cikin masu tsoronSa a
kowanne hali, kuma Yasa mu gama da duniya l afiya..
12 mai rabewa tsakaninku da abinda kuke tsoron gamuwa da shi a duniya da lahira. Kuma
Zai baku ilimi da basira Wacce za ku gane gaskiya daga vata. Kuma Zai datar da ku da
abinda zai sa Ya yarda da ku a kullum.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
17
(Hanya ta Biyar)
Da kuma nisantar sava masa
Bin Tafarkin Manzon Allah , da yi masa b iyayya a
cikin komai na umurni da hani, da barin sava masa ;
wannan shi ne ma Musuluncin gaba xaya .
Shi ne tafarkin shiriya . Shi ne mafi girma daga cikin
manyan alamomin imanin gaskiya .
Shi ne mafi qarfi daga cikin alamomin da suke nuna
lallai da gaske ba wa yana son Allah da manzonSa .
Shi ne mafi girma daga cikin hanyoyin da bawa zai bi
don Allah Yaso shi, kuma Ya yarda da shi .
Kuma yana daga cikin manyan hanyoyin samun Gafarar
Allah .
Za mu gane hakan ne idan muka duba cikin Suratu Ali-
Imran (ayah ta 31 da ta 32), inda Allah Yake cewa:
[
ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ
]
‚Kace (musu): in h ar (da gaske) kun kasance kuna son Allah,
toh ku bi ni. Shi kuma Allah Zai so ku (idan kukayi hakan),
kuma Zai Gafarta muku zunuban ku. Domin kuwa Allah Mai
yawan Gafara ne, kuma Mai Jinqai ‛.
Wannan ayah dai tana nan ne a matsayin mizanin auna
gaskiyar im anin duk wanda yace ya yarda da Allah
da ManzonSa .
Allah Ya sanya xa’a ga ManzonSa a matsayin
sharaxin ingancin imanin duk wanda yayi da’awar
imani da Allah da ManzonSa.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
18
Sannan Ya qara tabbatar da hakan a ayah ta gaba inda
Yake cewa:
[
ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ
]
‚Kace: kuyi xa’a (bi yayya) ga Allah kuma kuyi xa’a ga Manzo
(Muhammadu ). Amman suka juya baya (suka qi bin wannan
umurni), toh fa lallai Allah ba Ya son kafirai .‛
Ko shakka babu lallai tsayuwa akan tafarkin Manzon Allah
da tsare masa haqqoqinsa, da kyautata ladabi gareshi , da
kuma nisantar sava masa: waxannan su ne suke nuna lallai
da gaske bawa ya yi imani da shi. Duk kuma wanda yayi
hakan, Allah Ya yi alqawarin Zai Gafarta masa, kuma
Zai bashi lada mai girma. Domin kuwa dole sai ya aikata su
kafin ya samu tsira a duniy a da lahira.
Shi yasa a farko -farkon Suratul -Hujur at (ayah ta 3) Allah
Yake cewa:
[
ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥ ﯦ ﯧ
ﯨ ﯩ ﯪ
]
‚Lallai waxanda suke sassauta muryoyin su a wurin Manzon
Allah (saboda ladabin da suke masa), waxannan su ne
waxanda Allah Ya jarrabi zukatansu da taqawa (kuma Ya
datar dasu da cin wannan jarrabawa). Saboda haka suna da wata
irin Gafara, da kuma lada mai girma (a wajen Allah )‛.
Tsira da Amincin Allah su qara tabbata ga wannan Manzo mai
daraja, shi da iyalansa da Sahabbansa baki xaya, da kuma
waxanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar
sakamako. Da fatan Allah Yasa har da mu cikinsu.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
19
(Hanya ta Shida)
Lallai ayuka na gari ma suna shafe munana, idan har bawa
yayi sa’a yana da imani kuma ya nisanci s hirka. Annabi
yana cewa:
kaji tsoron Allah a duk inda kake. Ka riqa
bibiyan munanan ayukan ka da kyawawa, saboda su goge
munanan. Kuma ka kyautata yadda kake mu’amala da
13mutane
Wannan hadithi kuma shi yake qara fassara wannan magana
ta Allah inda Yake cewa:
[
ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵
]
:هود{ 114}
‚..Lallai kyawawan ayuka suna tafiyar da munana ..‛
Akwai misalai masu yawa daga cikin ayoyin Al -Qur’ani da kuma
ingantattun hadithai da suke tabbatar da lallai ayuka nagari suna
shafe munana (suna zama sanadiyyar samun gafarar Allah kan
wasu laifukan da bawa ya aikata a baya) ..
A.Kyautata Tsarki da kuma cika Alwala, kamar yadda
Manzon Allah
ya koyar
KYAUTATA TSARKI
Haqiqa kyautata tsarki al’amari ne mai muhimmancin gaske a
cikin addinin Musulunci. Tsarki dai s haraxi ne daga cikin
manyan sharuxan karvar duk wata Ibadar da bawa zai yi a
rayuwarsa. Manzo yace:
14Tsarki shi ne rabin imani
Shi yasa Allah Yake son duk wanda yayi qoqari ya
zama mai kyautata tsarkin sa.
13 Tirmidhi ne ya ruwaito shi (hadithi na 1987 ) daga Sahabi Abu -dharrin Al-ghifari
14 Sahih -Muslim (hadithi na 223) daga Sahabi Abu -Maalik al -Ash’ariy
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
20
Har ma Ya yabi wasu bayinSa saboda hakan, inda Yake
cewa:
[
ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ
(التوبة: 801) ]
‚..A cikinsa ( masallacin Quba) akwai wasu mazaje (mutane)
masu son suyi (kyakkyawan) tsarki, Allah kuma Yana son masu
neman tsakakuwan nan15.‛
Shi yasa ma aka umurce mu da neman Gafarar Allah a
yayinda muka gama tsarki muka fi to daga makewaya.
Manzon Allah ma ya kasance a duk lokacinda ya gama
biyan buqata ya fito, yana cewa:
غُفْرَانَكَ
‚GafararKa nake nema16 (Ya Allah)‛.
Ana neman Gafara yayinda aka fito daga makewaya saboda
wasu dalilai.
Kaxan daga cikinsu dai su ne kamar haka:
Saboda a haxa duk nau’ukan tsarkin biyu (najasar da aka
kawar daga gangan jiki, da kuma dattin zunuban da ake da
su)..
Saboda bawa bai sani ba qila a yayin tsarkin nashi akwai
wata najasar da ta fallatso masa a jiki (cikin rashin sani).
Duk da dai Allah ba Ya kama bawa akan irin wannan
(matuqar dai babu sakaci), amma tare da hakan bawa yake
neman Gafarar Allah da RahamarSa.
Sannan kuma ya tabbata a sunnah lallai rashin kyautata
tsarki yana cikin manyan laifukan da suke jawowa ayi wa
bawa azaba a cikin qabarinsa17.
15 Suratut -Taubah (ayah ta 108)
16 Tirmidhi( 7), Abu -Dawud( 30), Ibnu -Majah( 300).
Dukkan su daga Uwarmu (Nana) A’ishatu Allah Ya qaara mata Yarda da Daraja.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
21
A wani hadithin ma, Manzon Allah cewa yayi:
Kuyi
(ta hanyar kiyayewa sosai yayin qoqarin kuvuta daga fitsari
da kuke tsarki
saboda yawancin azabar qabari daga
irin
wannan)
18. fitsari n ne
Saboda haka aka umurci bawa da neman Gafarar Allah
bayan ya fito daga makewaya , saboda ya samu kuvuta daga
wannan azabar.
Ashe tunda kuwa rashin kyautata tsarki yana da irin wannan
muni, toh lallai wajibi ne mu kiyaye sosai. Musamman
kuma ga shi mun gani cewa kyautata tsarkin yana daga
cikin hanyoyin samun babban matsayi a wajen Allah ,
kuma yana ma daga cikin hanyoyin samun gafarar Allah .
Da fatan Allah Ya tsare mana imaninmu, Ya kuma qara
tabbatar da mu akan karantarwar ManzonSa Annabi
Muhammadu har mutuwa.
CIKA ALWALA
Yin alwala kamar yadda Manzon Allah ya koyar , yana
daga cikin muhimman hanyoyin samun Gafarar Allah
Maxaukaki. Kowa kuma zai samu wannan falala ne
gwargwadon koyinsa da Manzon Allah .
Akwai ingantattun hadithai masu yawa da sukayi bayani
akan wannan al’amari. Ga kaxan daga cikinsu insha‘Allahu:
Manzon Allah yace: ‚ Duk wanda yayi alwala kuma ya
kyautata alwalar, toh laifukan sa za su fice daga jikinsa -hatta
19‛. ma waxanda suke qarqashin faratan sa
Abin nufi: Duk wata gavar da aka wanke a yayin alwala,
toh wannan ruwan alwala zai wanko har da zunuban da aka
17 Bukhari (218), Muslim (212). Daga Sahabi abdullahi xan Abbas Allah Ya qara musu
Yarda
18Ad-daara -qutniy ne ya ruwaito (hadithi na 464) daga Sahabi Abu -huraira
19Sahih Muslim (Hadithi na 245) daga Sayyiduna Usmanu .
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
22
aikata da wannan gava, har bawa ya kasance tsaftatacce
daga zunubai a yayinda ya kamala alwalar20‛
Shi yasa aka kira alwala da sunan tsarki. Saboda bawa yana
tsarkaka daga zunubansa ta hanyar kyautata alwala.
Wata rana21 Manzon Allah (ya tambayi Sahabbansa) yana
cewa: ‚ Shin b azan nuna muku abubuwanda (ta dalilin
aikata su) Allah
Zai share muku laifukan ku ba, kuma Ya
‛ Sai suka ce lallai muna so ka faxa mana xaga darajojin ku?
ya Manzon Allah. Sai yace: ‚ Cika alwala (kyautata shi) a
daidai lokacinda ake qin tava ruwa22, da kuma yawan tattaki
zuwa wuraren sallah (masallatai), da kuma masu jiran sallah
bayan wata sallar23, Waxannan lallai su masu ribaxi ne.
24‛. Lallai waxannan su ne masu ribaxi
Manzon Allah ya kamanta waxannan ayuka gu da uku da
wannan babban al’amari na Jihadi, saboda girman aikin
nasu a wajen Allah .
Da fatan Allah Yasa mu cikinsu.
Wata rana b ayan Sayyiduna Usmanu ya koya wa mutane irin
alwalar Manzon Allah , sai yace musu: Na ga Manzon Allah
20 Sahih Muslim (Hadithi na 244) daga Sahabi Abu -Hurairah .
21 Hadithin yana cikin Sahih Muslim (Hadithi na ) daga Sahabi Abu -hurairah
22 saboda yanayin da ake ciki na tsananin sanyi, yasa kowa yana jin nauyin amfani da ruwa
sosai. Toh su duk da haka suna daurewa suyi alwala mai kyau
23 Misali: Irin zaman nan da akeyi tsakanin Sallar Maghriba da isha’i, ko tsakanin Azahar
da la’asar, ko kuma waxanda suka shigo masallaci sukayi nafila suka zauna suna jiran
lokacinda za a tayar da Iqamar Sallar da take biye, da dai sauran makamantan su..
24 Ribaxi shi ne zaman daqo cikin shiri da kimtsi (shirin ko ta kwana) saboda gabatar da
wani aikin ibada don neman Y ardar Allah. Aiki ne wanda dole s ai an jure kafin a iya yin
shi.
An kira waxannan mutane uku masu ribaxi ne, saboda irin himmar da suke da ita, da kuma
tsantsar jajircewar su akan ibada.
Sannan kuma w axanda aka fi sani da masu ribaxi , su ne waxanda suka z auna suka tare
wushiryar yaqi. Su ne waxanda suka bar komai suka koma suka tare kafar da ake ganin
maqiya za su iya biyowa su farma al’ummah. Su ne Mujahidan nan da suka saida rayukan
su don kare addinin Allah . Da fatan Allah Yasa mu cikinsu.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
23
ya yi irin wannan alwala, sannan sai yace: Duk w anda yayi
alwala kamar haka, za a g afarta masa abinda ya gabata n a
zunuban sa. Sannan tattakin da zaiyi zuwa Masallaci da kuma
Sallar da zai yi a chan, su ma kuma wani irin qarin lada ne
25gareshi
‛
A wani lokacin kuma, shi Sa yyiduna Usmanu xin yake
cewa: ‚Lallai na ji Manzon Allah yana cewa: Babu wani
mutum Musulmi da zai yi alwala kuma ya kyautata alwalarsa
sannan kuma ya sallaci wata sallar, fahce sai Allah
Ya
Gafarta masa abinda yake tsakanin wannan Sallah da kuma
26‛ Sallar da take biye da ita
B. Sallah (ta farillah da ta N afila)
Sallah ita ce mafi girma daga daga cikin dukkan rukunan
Musulunci bayan Kalmar Shahada. Ita ce ma shaidar cewa
mutum Musulmi ne. Daga cikin miliyoyin falalar ta marasa
qidayuwa, Sallah tana cikin man yan hanyoyin samun
Gafara . Idan har bawa ya kiyaye Sallar farillah, kuma ya
dage da nafilfilu kamar yadda Manzon Allah ya koyar,
toh Allah kuma Zai yafe masa zunubansa.
Babban misali akan wannan, shi ne faxin Allah (acikin
Suratu Hud ayah ta 114) inda Yake cewa:
[
ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵ ﮶ ﮷ ﮸ ﮹
]
‚Kuma ka tsaida Sallah a geffan nan biyu na yini da kuma
wani yank i daga dare. Lallai kyawawan ayuka suna tafiyar da
munana. Wannan fa tunatarwa ce ga masu (rabon) tunawa ‛
Saboda amfanin da waxannan sallolin guda biyar suke da
shi ga bawa wajen tsaftace shi daga zunubai ne fa, yasa har
25 Sahih Mus lim (hadithi na 229) daga Sayyidina Usmanu xan Affan
26 Sahih Muslim (hadithi na 227) Daga Sayyidina usmanu xan Affan
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
24
ma Manzon Allah ya kamanta su da wanka sau biyar a
yini.
Wata rana yace da Sahabbansa : ‚Shin baku gani ba; in har
da ace akwai wata korama a qofar (gidan) xayanku, kuma a
kowane yini yakan yi wanka aciki har sau biyar, shin akwai
wani dattin da zai ragu a jikinsa ne? Toh haka ne misalin
sallolin nan biyar. Allah
27 (kamar Yana share laifuka da su
yadda ruwan koramar nan yake wanke dattin jikin bawa) ‛.
Lallai ko shakka babu kiyaye Sallolin nan biyar, da kuma
tattaki saboda halartarsu a cikin jama’a, da kuma zama a
Masallaci saboda jiran S allah; baki xaya waxannan suna
cikin muhimman hanyoyin samun Gafara.
Ya tabbata cewa idan ma bawa ya tashi ya kama hanyar
zuwa Masallaci, toh gwargwadon takun da yayi da sawun sa
shi ne yawan ladan da zai samu da kuma yawan zunuban da
za a kankare masa. Do min kuwa Manzon Allah yana
cewa: ‚ Duk wanda yayi tsarki tun daga gidansa, sannan ya
fito zuwa xaya daga cikin xakunan Allah saboda sauke wani
farali daga cikin farillan Allah (Sallah), toh duk takun da
yayi; xaya zai kankare masa laifi ne, xaya takun kuma zai
xaga masa daraja28 ‛.
Ko shakka babu wannan wata falala ce mai yawan gaske da
Allah Yake wa bawanSa a yayin da ya kama hanyarsa ta
zuwa Masallaci don gabatar da wata Sallah daga cikin
Salloli.
Hakanan kuma duk wanda ya shigo Masallaci ya yi Nafila
sannan ya zauna yana jir an isowar Liman don a tada Sallah
(da kuma wanda ya zauna bayan an idar da Sallah don jiran
lokacin sallah ta gaba ), su ma akwai wata irin falala mai
27 Bukhari( 528), Muslim ( 667) dukkansu daga sahabi Abu -Huraira
28 Sahih Muslim (hadithi na 666) daga Sahabi Ubayyu xan Ka’ab
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
25
yawa da Allah Yake musu. Daga ciki dai, Mala’ikun
Rahama za su nema musu gafara.
Manzon Allah yace: ‚ Malaiku suna addu’a ga xayanku
matuqar yana zaune a inda yayi sallah kuma alwalarsa bata
warware ba. Suna cewa (cikin addu’ar): Y a Allah Ka G afarta
masa, Ya Allah Kayi masa Rahama29‛.
Sallar Juma’a:
Manzon Allah yace: ‚ Tsakanin Sallolin nan biyar (tsakani n
kowacce sallah da ta gabanta), haka kuma tsakanin kowacce
Juma’a da wata juma’ar; waxannan dukka suna kankare zunuban
da aka aikata tsakankaninsu, matuqar dai an nisanci kaba’irai30‛
A wani hadithin ma, Manzo cewa yayi : ‚Duk wanda yayi
wankan Juma’a, sa nnan ya taho Masallacin juma’a ya sallaci iya
abinda aka qaddara masa (na nafilfilu kafin zuwan Liman),
sannan ya zauna ya saurara har sai da Liman ya gama huxubar
sa, sannan yayi sallah tare da shi; toh za a Gafarta masa abinda
yake tsakanin wannan juma’a da wata juma’ar, har ma da qarin
wasu kwananki uku31‛
Sallar Dare (Qiyamul -Laili, ko Tahajjudi)
Sallar dare (ko tsayuwar dare), Sallah ce ta nafila mai xumbin
falala. Tana da lada mai yawa sosai. Lokacinta yana farawa ne
tun daga bayan an gama sallar Isha ’i har zuwa lokacin fitowar
Alfijir. Mutum zai iya yinsa aduk lokacinda ya samu dama.
Amma ingantattun hadis ai sun tabbatar cewa yin wannan
Sallah a qarshe -qarshen dare ya fi falala, ga wanda Allah
Ya baiwa ikon hakan.
29Bukha ri: 445, Muslim: 649, dukkansu daga Sahabi Abi -Huraira
30 Sahih -Muslim (hadithi na 233) daga Sahabi Abu -Huraira
31 Sahih -Muslim (hadithi na 857) daga Sahabi Abu -Huraira
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
26
Wannan Sallah tana daga cik in ayuka n Salihan bayin Allah.
Domin kuwa Allah Ya yabi masu yinta a cikin Al -Qur’ani
mai girma a wurare daban -daban.
A cikin Suratu Ali-Imran (ayah ta 16 da 17) Allah Yana
cewa:
[
ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ
]
‚Sune waxanda suke cewa: Ya Ubangijinmu haqiqa mu muny i
imani, saboda haka (muna roqonKa) Ka Gafarta mana
zunubanmu, kuma Ka tsare mu daga azabar wuta ‛.
Sannan sai Ya cigaba da zayyana siffofinsu a cikin ayah
ta gaba, inda Yake cewa:
[
ﭝ ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ
]
‚Su (waxannan bayin dai) su ne masu haquri kuma masu
gaskiya (a kullum), su ne masu dagewa da Ibada, su ne
masu ciyar da dukiyoyinsu (saboda neman Yardar Allah),
su ne kuma masu neman Gafarar Allah a lokacinnan da ake
kira ‚As -saharu‛ (wato lokacinda alfijir ya kusa fitowa).. ‛
Hakanan ma acikin Suratuz -Zariyat (ayah ta 17 da ta 18),
Allah Yace:
[
ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑ ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ
]
‚Sun kasance b asu yin bacci da dare sai xan kaxan.
Sannan a qarshen daren kuma, suna (dagewa da) neman
Gafara ‛.
Akwai ingantattun hadisai masu yawa da suka tabbatar
mana lallai wannan Sallah tana cikin manyan hayoyin
Samun Gafara. Ga kaxan daga cikinsu insha’Allah:
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
27
A cikin wani Hadithi mai xan tsawo32 Manzon Allah yace
wa Sahabinsa Mu’azu xan Jabal : ‚Shin ba zan nuna maka
wasu qofofin alkhairi ba? Azumi garkuwa ce, ita ma sadaka tana
kankare laifuka kamar yadda ruwa y ake kashe wuta, haka ma
sallar mutum a cikin dare take (tana da tasiri sosai wajen
kankare zunuban b awa)‛.
Sai kuma Manzo ya karanta faxin Allah :
ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ
ﮠ ﮡ
ﮢ
ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ
ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ
ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳
﮴
﮵
﮶ ﮷ ﮸ ﮹ ﮺ ﮻ ﮼ ﮽ ﮾ ﮿ ﯀ ﯁ ﯂
‚Gadajen bayansu suna nisantar makwantansu (a cikin dare),
saboda suna can suna ta roqon Ubangijinsu alhalin suna
tsoronSa kuma suna kwaxayin samun RahamarSa, sannan kuma
(daga cikin ayukansu) suna ciyar da abinda Muka arzuqta su.
Babu wani rai da ta sa n irin abin jin daxin da aka tanadar musu a
voye (a lahira), wanda sakamako ne gameda abinda suka
kasance suna aikatawa (a duniya). Shin wanda ya kasance mai
Imani, yana zama daidai da wanda ya kasance fasiqi? Ba za su
tava zama daidai ba. Amma su waxanda sukayi imani kuma
suka yi ayuka na qwarai, toh suna da (gidajen cikin) Aljannar
tsira a matsayin masauki (na har abada) saboda abinda suka suka
kasance suna aikatawa (na kyawawan ayuka a rayuwarsu ta
duniya)33‛
Allah Ya sanya wannan Sallah cikin manya -manyan
alamomin salihan bayi. Ya kuma tabbatar musu da cewa lallai
duk ibadar da sukeyi, Yana nan Yana adana musu, kuma a
lahira Zai basu kyakkyawan sakamako.
Allah Yasa da mu cikinsu. Ameeen.
32 Cikin Littafin Imam At -Tirmidhi (Hadithi na 2616) daga Sahabi Mu’azu xan Jabal
33 Suratus -Sajdah (daga aya ta 16 zuwa ta 19)
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
28
Ita w annan Sallah fa a kowane dare ma idan akayi ta ana
samun fala la mai yawa, ballentana kuma in har Allah
Yasa muka iya raya dararen watan Ramadan kam,
falalar tana da matuqar yawa sosai da sosai fiye da
sauran watanni.
Manzon Allah yace: ‚Duk wanda yayi tsayuwar dare
34 a cikin Ramadan alhalin yana mai Imani kuma ya yi
ne don neman lada a wajen Allah , toh za a Gafarta
masa abinda ya gabata na zunubansa35‛
Haka kuma yace: ‚Duk wanda yayi tsayuwar dare a
cikin daren Lailatul -qadari alhalin yana mai Imani,
kuma yayi ne don neman lada; toh za a gafarta masa
abinda ya gabata na zubanasa36‛
Shi yasa lokacinda Ma tarsa mai daraja (kuma uwar
muminai) Nana A’isha37 ta tambaye shi addu’ar da za ta
yi idan har Allah Ya datar da ita da daren Lailatul -
qadri, sai yace mata ‚Ki riqa cewa:
اللَّهُمَّ إِنَّكَ عَفُوٌّ تُحِبُّ الْعَفْوَ فَاعْفُ عَنِّي
‚Ya Allah Lallai (Ka kasance) Kai Mai yafiya ne, kuma
Kana son yafiya, saboda haka Ka y afe min ‛
Manzon Allah ya faxa mata hakan ne, saboda babu
abinda bawa yafi buqata sama da Afuwar Allah da
GafararSa da RahamarSa. Wannan kuma shi yafi komai
qima cikin buqatun bawa.
34 Ana kiran ta Sallar Tarawih ko asham, ko Tahajjud, ko Qiyamul -laili, ko wutri, da dai
sauran su.
35 Bukhari 37, Muslim 759, dukkan su daga Sahabi Abu -Huraira
36 Bukhari (35, 1901), Muslim (760), dukkan su da ga Sahabi Abu -Huraira
37 Allah Ya qaara mata Yarda
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
29
Toh a matsayinta na wacce yafi so kuma yafi qauna
daga cikin matan duniya baki xaya, sai ya faxa mata
addu’ar da tafi dacewa ace ta yi a irin wannan lokacin.
Saboda idan har Allah Ya yiwa bawa Afuwa, toh Ya
gama bashi Alkhairan duniya da lahira baki xaya.
Wannan dai kaxan ne daga cikin irin xumbin falalar da
ake samu idan har aka tsaida Sallah kuma aka dage da
nafilfilun da suka tabbata a Sunnah.
Sai mu kyautata niyyah kuma mu da ge sosai da sosai
wajen ganin mun kyautata ibada a cikin xan lokacinda
ya rage mana a rayuwa. Da fatan Allah Yasa mu dace da
aikata abinda zai sama sanadiyyar samun RahamarSa
garemu.
C. Zakkah, da sadaka, da sauran hanyoyin taimako ga
mabuqata
Daga cikin manya -manyan hanyoyin samun Gafarar
Allah , akwai fitar da Zakkah, bayar da Sadaka, da
sauran hanyoyin taimakon mabuqata, da kuma samar da
‘yanci ga duk wanda yake cikin wani qangi38.
Zakkah:
Zakkah tana tsarkake dukiya. Kuma tana daga cikin
alamomin qarfin imanin bawa. Sannan kuma hanya ce
ta tsarkake bawa daga zunubai, saboda zai samu Gafarar
Allah idan ya fitar da ita kamar yadda aka umurce shi
a shari’ance.
38 Bauta, ko gidan yaari, ko kuma wani dabaibayi na quncin rayuwa (musamman waxanda
aka zalunta)
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
30
A cikin Suratut -Taubah (ayah ta 103-104) Allah Yace :
[
ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ
ﮪ ﮫ ﮬ
]
‚Ka karvi sadaka (zakka) daga cikin du kiyoyinsu don ka
tsaftace su kuma ka tsarkake su da yin hakan, sannan kuma kayi
musu addu’a (a yayinda suka fidda wannan zakkar), lallai
addu’arka za ta zamto dalilin samun kwanciyar hankali garesu (a
duniya da lahira), Shi kuma Allah Shi ne Mai jin koma i (daga
cikin akwai roqon bawa), Shi ne kuma Mai cikakkiyar masaniya
akan komai (Ya san buqatar kowa, kuma Ya san abinda ya dace
da kowa cikin bayinSa) ‛.
Sannan sai Ya cigaba da cewa:
[
ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵ ﮶ ﮷ ﮸ ﮹ ﮺ ﮻ ﮼ ﮽
]
‚Shin basu sani bane, cewa lalla i Allah Shi ne (kaxai) Mai
karvan tuban bayinSa, kuma Shi ne (kaxai) Mai karvan
(ayukan da sukayi na bayarda) sadakoki (ga mabuqata),
kuma lallai Allah Shi ne (kaxai) Mai karvar tuba (daga
bayinSa), Shi ne kuma Mai Jinqai? ‛
Sadaka:
Ita ma sadaka xaya ce daga cikin dalilai masu qarfi da suke
nuna lallai bawa yana da gaskiya cikin imaninsa. Tana
kuma yaye wa bawa fushin Ubangiji , Saboda tana xaya
daga cikin hanyoyin samun GafararSa.
Shi yasa Manzon Allah yace: ‚ Ita ma sadaka tana
kashe zunubai (tana ka nkare su) kamar yadda ruwa yake
kashe wuta39‛
39 Tirmidhi (hadithi na 2616) daga Sahabi Mu’azu xan Jabal
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
31
Samar da ‘Yanci ga Bayin Allah, da kuma Qwatar Musu
HakkinSu daga Hannun Azzalumai:
Duk wanda ya kyautata niyyah wajen ‘yanta wani Musulmi
daga qangi na bauta (ko kuma ya ceto shi daga wani qunci
na rayuwa); to h shi ma hakan zai zame masa sanadiyyar
samun Gafarar Allah . Domin kuwa Manzon Allah
yana cewa: ‚ Duk wani mutumin da ya ‘yanta wani mutum
Musulmi, toh shi ma Allah Zai ‘yanta kowacce gava ta
jikinshi daga wuta, da kwatankwacin irin wannan gava ta jikin
wanda ya ‘yanta xin40‛
Duk da dai a wannan zamani n amu ba bu irin waxannan
bayin, amma wannan falalar dai tana nan. Domin kuwa
yanzu haka a tsakankaninmu akwai waxanda suke cikin
wani irin qangi irin na masu bautan.
Wasu daga cikin mutanenmu (saboda rashin galihu) yanzu
haka suna garqame a cikin gidajen yari alha lin kuma babu
laifin da sukayi.
Wasu kuma (saboda rashin mai tsaya musu) an nuna musu
fin qarfi an qwace musu gida ko gona ko fili, da dai sauran
nau’uka na cin zali iri -iri kamar yadda muke gani cikin gida
da waje..
Toh idan har Allah Ya baiwa mutum damar qwato wa
irin waxannan raunana haqqinsu daga hannun azzalumai,
insha’Allahu zai samu irin wannan sakamakon da aka
ambata acikin wannan hadithi mai daraja (matuqar dai ya
kyautata niyyah).
Allah Ya tsare mu daga zalunci da kuma sharri n azzalamai,
Ya rufa mana asiri, kuma Yasa mu dace.
40 Bukhari:2517, Muslim:1509, Abu -Dawud:2964, Tir midhi:1547, Dukkansu daga Sahabi
Abu-Huraira
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
32
Lallai ne muyi amfani da duk wani abinda muka m allaka
(na mulki da dukiya da ilimi da sauransu) wajen neman
Yardar Allah da kuma GafararSa da RahamarSa . Kada
mu bari shaixan ya kai mu ya baro da ruxe -ruxen nan nashi
marasa kan gado . Allah Shi ne mai Alqawarin Gaskiya,
domin kuwa shi ne Ubangijin Gaskiya. Ya yi mana
Alqawarin cewa matuqar mun bi umurninSa mun tsaya kan
karantarwar AddininSa, kuma muka yi amfani da
dukiyoyinmu kamar yadda Ya umurce mu; t oh Zai Gafarta
mana zunubanmu, kuma Zai bamu babban rabo a duniya da
lahira . Acikin Suratul -Baqarah (ayah ta 268) Allah
Yana cewa:
[
ﯔ ﯕ ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ
ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ
]
‚Shaixan yana (ruxar ku kuma yana tsorata ku ta hanyar) yi
muku alqawari da talauci (i n har kuka ciyar da dukiyoyin ku
akan neman yardar Allah), kuma yana umurtan ku da
alfasha (wato yana so kuyi amfani da dukiyoyinku akan
savon Allah). Shi kuma Allah Yana muku alqawarin Gafara
daga gareShi da kuma wata irin babbar falala (in har kuka yi
miShi biyayya kuma kuka sava wa shaixan), domin kuwa
Allah Mawadaci ne kuma Masani ‛..
Allah Ya bamu arziki mai Albarka, wanda zai zama
sanadiyyar samun babban rabo garemu a duniya da lahira.
D. Azumi (na farillah da na nafilah)
Azumi wani irin sirri ne tsak anin bawa da Ubangijinsa.
Wata Ibada ce wacce babu wanda yasan yawan ladan ta
sai Allah .
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
33
Azumi Yana daga cikin manyan hanyoyin shiga Gidan
Rahama . Akwai qofa ma ta musamman a Aljannah da
aka tanadar da ita don masu azumi kaxai. Idan suka
shige za a kulle qofar, babu mai qara biyowa ta nan
kuma har abada.
Sannan kuma Azumi yana daga cikin manya -manya n
hanyoyin samun Gafarar Allah . Shi yasa ma aka
sanya shi acikin jerin galibin nau’ukan kaffarah da aka
xora wa bawa idan ya aikata wasu manyan laifuka.
Kaxan daga cikinsu su ne kamar haka:
Wanda yayi kisan kai a bisa kuskure, akwai diyyah
akansa, da kuma azumin wata biyu (kwana sittin kenan).
Wanda yayi rantsuwa akan abu, sannan sai daga baya
ya karya wannan rantsuwar, cikin nau’ukan kaffararsa
akwai azumi u ku.
Wanda yayi zihari (wato ya kamanta saduwa da matarsa
ta sunnah da kwanciya da mahaifiyarsa), sannan daga baya
ya koma ga matar; toh dole sai ya yi kaffarah kafin ta
halatta gareshi. Daga cikin jerin nau’ukan kaffarar kuma,
akwai azumi sittin.
Wanda ya sadu da iyalinsa da rana alhalin kuma da
azumin Ramadan a bakinsa, shi ma dole sai ya yi kaffarah.
Daga cikin jerin nau’ukan kaffarar kuma akwai azumin
wata biyu.
Wanda yayi wani laifi a cikin aikin hajji, irin laifin da aka
xora masa hukuncin nan da ake k ira fidiya, toh (matuqar ba
mazaunin garin Makka ba ne shi) dole sai ya yi wannan
kaffarah. Daga cikin nau’ukan kaffarar kuma akwai azumi
goma (uku a harami, bakwai kuma idan ya koma gida).
..Da dai sauran su..
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
34
An saka azumi a cikin waxannan nau’ukan k affarah ne,
saboda irin muhimmancin da azumin yake da s hi wajen
kankare zunuban mutum. Da fatan Allah Yasa mu cikin
bayinSa masu himma wajen azumi (na farilla da nafila),
kuma Ya gafarta mana zunubanmu, Yayi mana Afuwa, Ya
kuma Yi mana Rahama.
Azumin Ra madan:
Manzon Allah yana cewa: ‚ Duk wanda ya azumci
Ramadan alhalin yana mai imani, kuma yayi hakan ne don
neman lada a wajen Allah ; toh za a Gafarta masa abinda
ya gabata na zunubansa41‛
Azumin Nafila:
Kamar yadda azumin Farillah yake da falala mai yaw a, haka
ma azumin nafila yake. Domin kuwa Manzon ya
kwaxaitar sosai akan yin azumin nafila , saboda xumbin
falalar da haka n yake da ita.
Tabbas a zumi yana da lada mai yawa sosai, kuma yana daga
cikin manyan hanyoyin samun Gafarar Allah .
Daga cikinsu ak wai azumin ranar Arafah ( 9 ga watan
zulhajji, ranar jajiberen babbar sallah), da kuma ranar
Ashura (wato 10 ga watan Al -Muharram)..
Sahabi Abu Qat adah yana cewa: ‚Wata rana an tambayi
Manzon Allah gameda falalar a zumtar ranar Arafah, sai
yace: Tana k ankare zunuban shekaru biyu, wacce ta gabata
da kuma wacce take biye . Sannan da aka tambayeshi
gameda falalar azumtar ranar ashura’ kuma, sai yace: Tana
kankare zunuban shekara guda, wacce ta gabata42‛
E. Aikin Hajji da Umrah:
41 Bukhari (38, 1901), Muslim (760) Daga Sahabi Abu -huraira
42 Sahih Muslim (Hadithi na 1162)
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
35
Aikin Hajji da Umrah ma suna daga cikin manyan hanyoyin
samun Gafara. A cikin Suratul -Baqarah bayan Allah Ya yi
bayanin wasu dokoki na aikin Hajji, sai Yace43:
[
ﮐ ﮑ ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ
]
‚Sannan sai ku kwararo ta inda sauran mutane suka
kwararo (ku gangaro tare da sauran mutane daga
farfajiyar Arafah zuwa Muzdalifa, can bayan faxuwar
rana), kuma ku nemi Gafarar Allah , Saboda lallai Shi
Allah Mai yawan Gafara ne, kuma Shi Mai yawan
Jinqai ne ‛
Manzon Allah kuma yace: ‚ duk wanda yayi aikin
hajji alhalin bai yi wani rafathu44 ba, kuma bai yi wani
aiki na fasiqanci ba (a yayin wannan aikin hajji nashi)
har ya gama; toh zai dawo (gida) kamar ranar da
mahaifiyarshi ta haife shi45‛
Abin nufi: Allah Zai yafe masa baki xaya laifuk an sa,
har ya zama kamar bai tava aikata wani laifi ba a
rayuwarsa.
A cikin wani hadisin kuma, Manzo yace: ‚ Daga wata
Umrah zuwa wata Umrar (ta daban), ana kankare zunuban da
aka aikata tsakaninsu. Shi kuma Hajji karvavve, bai da wani
sakamako sai Aljannah46‛
Allahu Akbar
43 Acikin ayah ta 199
44 Saduwa da iyali, da duk abinda ya danganci hakan
45 Bukhari:1521, Muslim:1350, daga Sahabi Ab u-Huraira
46 Bukhari:1773, Muslim:1349
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
36
F. Karantar da mutane addinin Allah, da sanar da su hanyoyin
alheri
Daga cikin hanyoyin samun Yardar Allah da Ga fararSa da
RahmarSa; akwai karantar da mutane Addini, da sanar da su
hanyoyin Alkhairi, da umurtansu da kyawawan aiyuka, da
kuma hana su munana, da qyamatar da su aikata dukkan
wani aiki na savo, da kuma nuna musu Girman Allah don su
ji tsoronSa kuma su ts are dokokinSa..
A cikin Suratut -Taubah (ayah ta 112) Allah Ya lissafa
masu irin wannan aiki daga cikin bayinSa na qwarai masu
babban rabo a duniya da lahira, waxanda Yayi musu bishara
saboda Yarda da Yayi da imaninsu. Yace:
[
ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ
ﭘ
ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ
]
‚Su ne masu Tuba, masu kyautata bautarsu, masu yawan
godiya, masu yin tafiye -tafiye don ayukan xa’a (irinsu aikin
hajji, jigadi, ziyara, duba mara lafiya da dai sauransu), su ne
masu umurni da kyawawan ayuka kuma suke hana munana,
su ne masu t sare dokokin Allah. Saboda haka kayi Albishir
ga (irin waxannan bayi) masu imani (an karvi ayukansu
kuma an yafe musu zunubansu) ‛.
Manzo yace: ‚ Lallai shi Malami47, duk waxanda suke
cikin sammai da qassai suna nema masa Gafarar Allah,
hatta kifaye acikin ruwa (su da sauran halittun ruwa baki
xayansu suna nema masa Gafara wajen Allah )48‛
47 Mai karantar da al’ummah da ikhlasi, kuma ya tsaya kan karantarwar Manzon Allah
48 Abu-Dawud (hadithi na 3641), Tirmidhi (hadithi na 2682) daga Sahabi Abud -Dardaa’i
. Hadisin ya inganta. Duba Saheeh_Sunan_Abi -Daw ud hadithi na 3096
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
37
Duk halittun nan da suke cikin sammai da qassai suna nema
wa malami Gafara dare da rana, ta hanyoyin da babu wanda
yasan ma adadinsu sai Allah .
Bayan haka kuma, shi ma yana ta tara lada mai yawan gaske
(saboda yana da ladan duk wani harafi guda xaya da ya
koya wa mutane, sannan kuma duk lokacinda akayi aiki da
wannan ilimin da ya koyar -ko da kuwa bayan nutuwarsa
ne- sai shi ma an bashi kwatankwacin irin ladan da aka
baiwa masu aikin, ba tare da kuma an tauyewa kowa komai
ba).
Ko shakka babu wannan falala ce babba sosai. Babu wanda
ya cancance ta sai Malamai magada Annabawa.
Allah Ya saka wa Malamanmu (na da da na yanzu dukka)
da Alkhairi, Ya Gafarta musu zunubansu, Ya kankare musu
kurakuransu, Ya qara wa iliminsu Albarka, Ya qara kare
mana su daga duk wani sharri, da irin kariyar da Yake wa
manyan bayinSa (a duniya da lahira).
Ya mai karatu! Lallai dole ne mu tashi mu nemi ilimin
addinin Allah , don sanin yadda zamu ba uta maSa kamar
yadda Yai umurni. Dole mu tashi muyi karatu, don mu
kawar wa kawunanmu jahilci, mu kuma kawar wa sauran
Al-ummar da muke rayuwa tare (ta hanyar karantar dasu
addinin gaskiya).
Laifi ne babba a zauna kara zube ba a karatun addini.
Hakan yana da mummunan haxari garemu cikin
addininmu da rayuwarmu baki xaya. Domin kuwa idan
jahilci ya kanannaxe al -ummah, toh babu irin tavarazar
da ba za a gani ba.
Zama cikin jahilci zai sa a koma ana rayuwa irin ta
dabbobi, domin kuwa babu irin varnar da ba za a fito fili
ana aikatawa ba.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
38
Babu kuma wata al’ummar da ta cigaba cikin jahilci.
Kuma baki xaya Annabawa da Manzanni da Salihan
bayi dukkansu sun nemi tsari daga jahilci.
Sannan su ma waxanda Allah Ya zave su Ya sanar
dasu wani abu na ilimi, toh fa waj ibi ne akansu suyi aiki
da shi. Domin kuwa duk wanda ya sani kuma ya take,
toh laifinsa babba ne a wurin Allah . Bal ma azabarsa
daban ce acikin wuta. Saboda tsananin azabar da za ayi
masa ma, har wasu daga cikin ‘yan wutan za su taru
suna kallon yadda ak e masa (tare da su ma xin suna
cikin wutar).
Haka Manzon Allah yace. Hdi sin yana nan cikin
Sahihul -Bukhari49 inda yake cewa: ‚Za a taho da wani
mutum a jefar da shi cikin wuta. Za a xaure shi (da
hanjinsa) kamar yadda ake xaure jaki a jikin tirkensa (da
igiya). Har sauran ‘yan wuta su kewaye shi (suna kallon
irin azabar da ake masa), su riqa ce masa ya kai malam
wane, ba kai ne (a duniya) ka kasance kana umurni da
kyawawan ayuka kuma kana hani da munana ba? Sai
yace musu:
إِنِّي كُنْتُ آمُرُ بِالْمَعْرُوفِ وَالَ أَف ْعَلُوُ، وَأَن ْهَى عَنِ المُنْكَرِ وَأَف ْعَلُوُ
Zai ce (can a bakinsa): ‚Lallai (hakane) ni na kasance ina
umurni da kyawawan ayuka amma ni ba na aikatawa. Ina
kuma hani da munana amma ni ina aikatawa (a voye) ‛.
Wasu hadithai ma sun tabbatar cew a da irin waxannan
shaixanun malamai za a fara hura wutar jahanna a gobe
Qiyamah.
49 Hdithn Sahabi Usaamah xan Zaid Allah Ya qara musu Yarda (shi da mahaifin nashi
dukka). Yana ma cikin Sahih Muslim
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
39
Shi yasa ma wani mawaqi (acikin wasu baitocinsa) yake
cewa:
وَعالِمٌ بِعِلْمِوِ ال ي َعْمَلَنْ # مُعَذَّبٌ ق َبْلَ عُبَّادِ الْوَثَنِ
‚Kuma duk Malamaninda baya aiki da i liminsa, toh
lallai shi za a fara yiwa azaba (a wuta) kafin ma ayiwa
masu bautan gumaka.‛
Haka nan rowar ilimi ma babban laifi ne sosai. Saboda
Manzon Allah yana cewa: ‚ Duk wanda aka tambaye
shi wani ilimi sai ya voye shi (ya qi ya sanar da
mutane), toh za a sanya masa linzamin wuta a ranar
Qiyamah50‛
Su fa masu umurni da kyawawan ayuka kuma suke hana
munana, a kullum cikin nasara suke a rayuwarsu (ta
duniya da lahira). Domin kuwa bayan xumbin ladan da
suke samu ta fiskoki daban daban, da kuma zunubansu
da ake ta kankare musu a kullum, har ila yau kuma su
(da waxanda suka amsa kiransu) ne kaxai suke tsira a
duk lokacinda wata uquba ta sauka ga kangararrun bayi.
Allah Yana tserar da su ne saboda wannan babban
aikin da suka tsaya sukayi ta yi na gadon Annabta.
Allah Ya bamu labarin yadda Yayi ta tserar da
Annabawa da Manzanni masu yawa a cikin Al -Qur’ani
mai girma, su da waxanda sukayi imani dasu cikin
al’ummomin su . Haka kuma Ya ma bamu labarin yadda
Ya tserar da wasu Malamai masu faxakar da al’umma,
su da waxanda suka amsa kiran su.
50 Abu-Dawud (3658), Tirmidhi (2649). Hadithi ne ingantacce, duba Sahih_sunan_Abi -
Dawud (3106)
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
40
Misali a cikin suratul -A’rafi (ayah ta 164 zuwa ta 166)
Allah Yana cewa:
[
ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ
ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ
]
‚Kuma a lokaci nda wasu mutane (marasa gaskiya)
daga cikinsu suka ce (wa masu wa’azi): wai shin me
yasa kuke ta yin wa’azi ga mutanenda tabbas Allah
Zai halaka su, ko kuma Yayi musu azaba mai
tsanani? Sai (su masu wa’azin) suka ce: muna hakan
ne domin neman hanzari zuwa ga Ubangijinku
(saboda kar Ya kama mu da laifin rashin wa’azi ga
mavarnata), da kuma tsammanin (wasu daga cikinsu)
za su (wa’aztu) suyi taqawa (su daina ayukan savon
da sukeyi) ‛.
Wannan akullum itace gwagwarmayar da take tsakanin
Malamai nagari (masu nema n Yardar Allah) da kuma
miyagun malamai (waziran shaixan daga cikin mutane).
Acikin ayah ta gaba kuma sai Allah Yace:
[
ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ ﭬ ﭭ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ
ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ
]
‚Toh a lokacinda suka manta da abinda aka tunatar da
su (suka qi aiki da shi), Mun tserar da wax anda suke
hani da munanan ayuka, kuma Muka k ama waxanda
sukayi zalunci da azaba mai matuqar tsanani, domin
abinda suka kasance sunayi na fasiqanci ‛.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
41
Sannan a gaba kuma sai Yace:
[
ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ
]
‚Sa’nnan a lokacinda suka yi girman kai suka q i barin
abinda aka hanesu aikatawa, sai muka ce musu Ku kasance
birrai qasqantattu (Muka mayar da su birai, sukayi ta
rayuwa cikin qasqanci da wulakanci) ‛.
Wannan yake tabbatar da cewa lallai babu mai tsira a
duniya da lahira sai wanda ya tsaya kan Tafarki n
Manzon Allah . Idan aka duba ayah ta 52 cikin
Suratun -Nur, Allah Yana cewa:
[
ﯹ ﯺ ﯻ ﯼ ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃ
]
‚Kuma duk wanda yayi xa’a ga Allah da ManzonSa,
kuma ya ji tsoron Allah kuma ya tsare dokokinSa, to
waxannan su ne masu babban rabo ‛
Toh malami mai gaskiya cikin i maninsa shi ne wanda zai
kyautata niyyah tsakaninsa da Allah, kuma yake bin tafarkin
Manzon Allah wajen isar da saqon Allah ga bayinSa.
Rashin bin wannan tafarki yana da haxari sosai.
Domin kuwa Manzon Allah yana cewa: ‚ Na rantse da
wanda rayuwa ta ta ke HannunSa! Dole (ku tashi) kuyi
umurni da kyakkyawan aiki, kuma dole kuyi hani da
mummuna. In ba haka ba kuma, toh za a kai wani
yanayinda Allah (Zai yi fushi) Ya saukar muku da uquba
daga gareShi, kuma (a irin lokacin nan) ko kun roqe Shi
(don Ya yaye muku) ma, ba Zai amsa muku roqon naku
ba51 (saboda baku cika sharaxin karvar addu’ah ba) ‛.
51 Tirmidhi (hadithi na 2169 ) daga Sahabi Huzaifah al -Yamaani
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
42
G. Biyyaya ga iyaye, kyautata musu, da kuma barin
sava musu ko cutar da su
Daga cikin manyan hanyoyin samun gafarar Allah ;
akwai kyautata wa iyaye, da kuma nisant ar sava musu.
Domin kuwa Yardar Allah tana cikin yardar iyaye, haka
ma FushinSa yana cikin fushinsu52.
Bayan haqqin Allah da na Manzo babu haqqin da
yakai na iyaye. Shi yasa acikin ayoyi masu yawa ma ake
yawaita kawo batun kyautatwa iyaye da zarar an ga ma
umurni da kaxaita Allah da bauta.
Saboda haka duk mai son gamawa da duniya lafiya; toh fa
dole ne ya sasanta da iyayen shi ya zauna lafiya da su, kuma
ya riqa kyautata musu. Sannan kuma dole ne ya guji sava
musu akan duk abinda ba savon Allah ba ne. Kar kuma ya
yarda ya cutar da su ko ta wane hali ne. Sava wa iyaye laifi
ne mai matuqar girma. Kuma tun daga nan duniya bawa zai
fara xanxana uquba kafin yaje lahira ya tarar da sakamakon
mummunan aikinsa.
Lallai ne duk wani xa nagari yayi qoqarin ganin ya
nemi Aljannah ta hanyar kyautata wa iyayensa.
Manzon Allah yana cewa: ‚ Allah Ya turbuxe hancin
duk wanda ya riski tsufan mahaifansa –sawa’un xaya
daga cikinsu ne ko su biyun dukka - kuma (har suka
mutu) bai yi musu wani abin kyautatawan da zai zama
sanadiy yar shigarsa Aljannah ba53. Allah Ya turbuxe
hancinsa (ma’ana: Allah wadaransa. Domin kuwa ba zai
tava samun dacewa ba a rayuwa) .‛
52 Tirmizi (Had1si na 899) daga Sahabi Abdullahi xan ‘Amru xan Aas (Allah Ya qara
musu Yarda su biyun duka).
53 Sahih Muslim (hadisi na 2551 ) daga Sahabi Abu. -Huraira .
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
43
A cikin wannan hadi si za mu ga ashe biyayya ga iyaye
(da kuma kyautata musu) yana daga cikin hanyoyin
samun Gafarar Allah . Sannan rashin kyautata musu
kuma, yana daga cikin ababenda suke cire albarka a
rayuwar bawa. Allah Ya tsare mana imaninmu.
Sannan kuma akwai hadisan da suke qara tabbatar da
lallai Allah Yana tserar da irin waxannan (masu
kyautatawa iyayensu) daga faxaw a cikin wani haxari ko
bala’i, sakamakon biyayyar da suke wa iyayensu.
Za mu ga misalin hakan a cikin hadithin da Manzon
Allah ya bada labarin wasu mutane su uku da suka
shiga cikin wani qogo suka fake, sai wani qaton dutse
ya gangaro ya rufe qofar qogon alhalin suna ciki (ga shi
kuma acikin qungurmin daji ne mai nisa, saboda haka
babu mutane kusa ballentana su taimake su).
Saboda haka sai suka yanke shawara akan lallai ne
kowanne daga cikinsu yayi tawassuli da wani aikinsa
nagari (wanda yake fatan Allah Ya karva masa)
wajen roqon Allah don Ya kuvutar dasu daga wannan
halakar da suke gani ido da ido.
Sun roqi Allah kuma Ya amsa musu. Domin kuwa
Ya kuvutar dasu daga wannan ramin da suke binne a
ciki da rayukansu.
Toh daga cikinsu akwai wanda yayi tawa ssuli da
biyayyar da yayi wa mahaifan sa (waxanda sun riga sun
tsufa) da kuma kyautata musu da yayi, tare da fifita su
akan akan iyalansa (mata da kuma yara qanana)54.
54 Bukhari ( 2272 ), Muslim ( 2743 ), daga Sahabi Abdulla hi xan Umar, Allah qara musu
yarda.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
44
H. Yiwa mutane Afuwa:
Yafewa mutane abinda suka sukayi na laifi ko kuskure (da
kuma rangw anta musu), wannan babban lamari ne wanda
sai masu babban rabo awajen Allah suke iyawa. Shi Yasa
Allah Ya lissafa wannan aiki cikin halayen manayan
bayinSa. Misali xaya gameda hakan shi ne inda Yake cewa:
[
ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ
]
:الشورى{
37
}
‚..Kuma idan ma sukayi fushi (ma’ana idan aka vata musu
rai ta) sai kaga suna yin gafara ‛
Kenan hakan ya nuna duk mai yafewa wani, toh shi ma
Allah Zai yafe masa. A cikin Suratun -Nur (ayah ta 22)
Allah Yana cewa:
[
ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑ ﮒ ﮓ ﮔ
]
:النور{
22
}
‚Kuma suyi afuwa su qyale (kar su xauki wani mataki na
ramako akan wanda ya cutarda su). Shin ku baku so Allah
Ya Gafarta muku ne? Alhalin kuma Allah Shi ne Mai
Yawan Gafara kuma Shi ne Mai jinqai!!‛
Ka ga ashe hakan yana cikin hanyoyin samun Gafarar Allah
. Kuma Yana cikin hanyoyin samun Soyayyar Allah ga
bawa. Shi Yasa acikin Suratu Ali -Imra n (ayah ta 134 zuwa
136) Allah Yake cewa:
[
ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ
ﭪ ﭫ ﭬ
]
‚Su ne waxanda suke ciyarda dukiyoyinsu (a kullum)
sawa’un ana cikin walwala ne ko ana cikin qunci, suna
haxiye fushinsu, suna yafewa mutane, lallai Allah Yana son
(waxannan bayi n agari) masu kyautatwa ‛.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
45
[
ﭭ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ
ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ
]
‚Kuma su ne dai waxanda idan suka aikata wani laifi ko suka
zalunci kawunansu (ta hanyar savawa Allah ) toh nan take
suke tuna Allah su nemi GafararSa gameda zunubansu, sabod a
babu mai Gafarar zunubai sai Allah , sannan (bayan haka)
basu dogewa su kafe akan abinda suka aikata (na munanan
ayuka) alhalin suna sane (suna gaggauta barin aikin, suyi
nadama akansa, su nemi Gafara Allah, sannan kuma su
qauracewa duk abinda zai iya k usanto da su zuwa ga wannan
mummunan aiki, ballenta su kuma aikata shi nan gaba) ‛.
[
ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑ
ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ
]
‚Irin waxannan suna da sakamakon wata irin G afara daga
Ubangijinsu, da kuma Aljannatai waxanda koramu (na dangin
ababen sa daban daba n) suke gudana a qarqashinsu, za su
dawwama a ciki, Madallah da (irin wannan) lada (wanda yake a
matsayin sakamako) ga waxannan ma’aikata ‛
Ko shakka babu masu yiwa mutane afwa su ma Allah Zai
yafe musu. Saboda haka duk wanda yake kyautata niyyah
ya tausa ya wa wani, toh shi ma Allah Zai tausaya masa.
Domin kuwa Allah Yana jinqan bayinSa masu jinqai.
Shi yasa ma hatta mutumin da yake sassauta wa bayin Allah
a cikin kasuwancinsa, kuma ba ya tsawwala musu, toh shi
ma Allah Zai masa afuwa a duniya da la hira (matuqar ya
mutu ba ya shirka). Allah Zai qara wa dukiyarsa albarka,
Zai rufa masa asiri, kuma Zai kare shi daga uquba.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
46
Manzon Allah yace: ‚ Akwai wani (xan kasuwa) mutumin
kirki wanda ya kasance yana baiwa mutane bashi. A kulumm
yana cewa kowa dag a cikin yaran gidansa idan ka je gun wani
(daga cikin waxanda muke bi bashi) amma ka riske shi cikin
tsananin rashi, toh kayafe masa kawai (ka cire sunan shi daga
cikin jerin waxanda muke binsu bashi), da fatan mu ma (a gobe
Qiyama) Allah Allah Zai Yafe mana (a daidai lokacinda
muka fi matuqar buqatar RangwamenSa da GafararSa da
RahamarSa). Da wannan bawan Allah Ya mutu ya koma ga
Allah kuwa, sai Allah Ya Yafe masa xin55‛
Allah Ya saka masa ne da irin abinda ya kasance
yake yiwa bayin Allah a rayuwarsa ta duniya. Da ma
masu iya Magana suka ce Alkhairi danqo ne, ba ya
faxuwa qasa banza.
Toh da yake ya kasance yana rangwanta wa bayin Allah
mabuqata a nan duniya saboda irin tsananin tausaya musu
da yakeyi, sai shi ma Allah Ya saka masa da irin wannan
sakamako a daidai lokacinda yake matuqar buqatan hakan.
Har ma Allah Yace masa: ‚Mu muka fi cancanta mu
rangwanta wa mabuqata. Saboda haka kai ma jeka na
yafe maka‛.
I.
Musafaha a yayin da aka gamu a na gaisawa:
Musafaha a yayinda aka gamu ana gaisawa (bayan anyiwa
juna Sallama), wannan qarin tabbaci ne gameda amincin da
yake tsakanin ‘yan -uwa Musulmi.
Riqe hannun juna a yayin sallama, yana tafiyar da qiyayya
da gaba tsakanin Musulmi, kuma yana cikin manyan
alamun soyayya da qaunar juna da kuma ‘yan -uwantaka.
55 Bukhari ( 3480 ), Muslim ( 1562 ). Dukkansu daga Sahabi Abu -Hurairah
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
47
Shi yasa babban Malami Al -Imamu Hasanul -Basriy (Allah
Ya Gafarta masa) Yake cewa: ‚Musafaha tana qara qauna
(tsakanin musulmi). Idan xayanku yayi musafaha da xan -
uwansa, toh ya riqe hannunsa da kyau, domin hakan yana
qara danqon qauna (tsakaninsu). Kuma ko da yana xan jin
wani qaiqayi a zuciyarsa gameda shi, toh hakan zai
warware wannan qulli (wanda shaixan ya tufka masa a
zuciya gameda xan -uwansa musulmi)56‛.
Sannan kuma Musafaha tana tsaftace bawa daga dattin
zunubai, domin kuwa hadisai masu yawa sun ta bbatar da
cewa lallai ita ma musafaha tana daga cikin hayoyin samun
Gafarar Allah .
Manzon Allah yana cewa: ‚ Babu wasu Musulmai biyu da
za su gamu kuma suyi musafaha (a yayin sallama, gaisuwa irin
ta Addinin Musulunci) fahce sai an Gafarta musu (zunubansu)
kafin su rabu57 (kafin su saki hannun junansu) ‛.
Da fatan Allah Yasa mu dace.
Manzon Allah yace: ‚Lallai shi mumini idan ya gamu da
(wani xan -uwansa) mumini, sai yayi masa sallama, sannan ya riqe
hannunsa suka gaisa; toh zunubansu za su riqa kakkavowa (daga
jikinsu) kamar yadda (busassun) ganyayyakin bishiya suke
zubowa qasa idan i ska ta kaxa su58‛
Yana da kyau a kiyaye, kuma a riqa raya wannan Sunnah,
saboda fatan samun wannan falala mai yawan gaske da aka
ambata cikin wannan ingantaccen hadithi mai daraja.
56 Duba: Amaaliy na Ibnu Sam’un Al -waa’iz, majalisi na 14, juz’i na farko, sahafi na 230
57 Abu-Dawud (hadithi na 5212 ) daga Sahabi Baraa’u xan Aazib All ah Ya qara musu
Yarda
58 Imam Ax -xabaraniy ne ya ruwaito shi a cikin littafinsa mai suna ‚Mu’jamul -Ausax‛
(Juz’i na farko, shafi na 84, kuma hadisi na 245) daga Sahabi Huzaifah xan Yamaniy
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
48
Ba daidai ba ne irin durquson nan da akeyi ko rusunawa da
sunan wai girmamaw a, da dai sauran nau’ukan gaishe -gaishe
waxanda suka samo asali daga al’ adun al’ummomi daban
daban. Wa nnan kwata -kwata ba gaisuwar Musulunci ba ce.
Karantarwar Manzon Allah ita ce riqe hannun juna ayi
musafaha . Bayan xumbin falalar da yake tattare da su, mun ji
kuma cewa hakan yana cikin hanyoyin samun Gafarar Allah
.
Sannan kuma ba ya halatta Musulmi yayi musafaha da wata
mace wacce ba muharramarsa ba. Haka kuma irin wann an
musafaha da wasu suke yi suna wasa da ‘yan yatsu (har ma a
wasu lokutan ana motsa wa juna sha’awa), wannan ba
karantarwar musulunci ba ce. Amma in har matarka ce ka
kama hannunta, wannan babu matsala, domin kuwa ita kam
ta halatta gareka da ma.
Haka nan kuma ba sunnah ba ne yin musafaha da hannu
biyu dukka. Abinda ya tabbata a sunnah shi ne yi da hannu
xaya kawai (kuma hannun dama, ga wanda yake da hannun
dama xin kenan).
Malamai ma suna tsawatarwa gameda yadda wasu suka tsiri
al’adar yin musafaha a daid ai lokacinda aka sallame sallah.
Har ma wasu sun xauka ko hakan ma mantacciyar sunnah
ce suke rayawa . Ko shakka babu wannan bai da a sali a cikin
karantarwar Manzo . Abinda ya tabbata a Sunnah dai, shi
ne akwai wasu zikirorinda ake karantawa bayan an salla me
sallah. Toh wannan shi ya kamata a shagaltu da shi, ba wai
wata qirqirarriyar musafaha ba.. Sai dai wannan ba zai hana
daga baya a miqawa juna hannu a gaiggaisa ba. Amma riqe
hakan a matsayin wata al’ada, toh wannan ne bai da asali a
cikin karantarwar M anzon Allah . Allah Yasa mu dace.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
49
J. Taruwa don karatun addini , da kuma darasin sa:
Irin wannan taro yana daga cikin wasu manyan taruka guda
uku waxanda a cikinsu ne kaxai ake samun Alkhairan
duniya da lahira, koma bayan wasu tarukan da ba su ba.
Domin kuwa acikin S uratun -Nisa’i (ayah ta 114) Allah
Yana cewa:
[
ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟ ﭠ
ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ ﭬ
]
:النساء{
114
}
‚Babu Alheri cikin da dama daga cikin tarukansu (su
mutane), sai wanda a cikinsa akayi umurni da wata sadaka
(da duk abinda zai amfanar da gangan jikin xan Adam), ko
kuma (umurni da) wani kyakkyawan aiki (da duk abinda zai
amfanar da ruhin xan Adam), ko kuma (tattaunawar da ta
qunshi) sasantawa tsakanin mutane (don a samu wanzuwar
zaman lafiya a cikin al’ummah). Toh duk wanda ya aikata
(xaya daga cikin) wannan alhalin yana mai neman Yardar
Allah , nan gaba (a lahira) Za Mu bashi Lada mai Girma ‛
Manzon allah yana cewa: ‚ Babu wasu mutanen da za
su taru a cikin xaya daga cikin xakunan Allah su riqa
karanta Littafin Allah kuma suna darasin sa a
tsakankaninsu; fahce sai nitsuwa ta sauka akansu, kuma
sai Rahama ta lulluve su, sannan kuma Mala’iku (na
Rahma) za su kewaye su (da Umurnin allah za su
katange su daga dukkanin sharri), sannan kuma allah
zai ambace su a cikin waxanda suke tare da shi59‛.
Allah zai ambaci sunayensu xaya bayan xaya a gaba n
Mala’ikunsa, sannan Yace musu (su Mala’ikun): ‚ Ina
59 Sahih Muslim (hadithi na 2689), daga Sahabi Abu -Hurairah
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
50
mai kafa ku shaida akan cewa lallai haqiqa na Gafarta
musu60 (baki xayansu) ‛
Shi yasa akeso a kowanne lokaci mu riqa qoqarin
halartan wuraren da ake karatun addini, da wurarenda
ake wa’azi. Saboda akwai f alala mai xumbin yawa a
waxannan wurare.
Daga cikinsu dai, akwai samun Gafarar Allah .
Shi yasa aka shar’anta mana karanta ‚Kaff aratul-Majlis‛ ..
A duk lokacinda aka zo tashi daga inda ake zaune61 toh
a riqa karanta wannan addu’a wacce ake kira kaffaratul-
majlis (wato addu’ar neman gafarar Allah gameda
zunuban da aka aikata a cikin wanna n zama da akayi) .
Ga yadda addu’ar take:
سُبْحَانَكَ اللَّهُمَّ وَبِحَمْدِكَ، أَشْهَدُ أَنْ الَ إِلَوَ إِالَّ أَنْتَ، أَسْت َغْفِرُكَ وَأَتُوبُ إِلَيْكَ
Ma’ana: ‚ Dukkan Tsarki da Yabo da Godiya sun tabbata
gareKa Y a Allah. Na shaida lallai babu abin bauta (bauta ta
gaskiya a bisa cancanta) sai Kai (Kai kaxai kake, b aka da
abokin tarayya). Ina neman GafararKa kuma na tuba zuwa
Gareka62‛
Manzon Allah ya kasance yana karanta wannan addu’a a
duk lokacinda yazo tashi daga inda yake zaune. Kuma yace
duk wanda ya ke yin haka, toh Allah Zai yafe masa
zunuban sa.
K. Zikiri (ambaton Allah )
60 Bukhari (2408), Muslim (2689), daga Sahabi Abu -Huraira
61 Ko a ina ne (sawa’un wurin karatu ne ko wata ganawa, ko hira, ko wani aiki, ko
kasuwanci da dai sauransu)
62 Tirmidhi (hadithi na 3433), Ahmad (hadithi na 10420), daga Sahabi Abu -Huraira
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
51
Acikin Suratul -Ahzab ( Ayah ta 35) Allah Ya lissafa
masu yawan zikiri cikin waxanda Yayi musu tanadin Gafara
da kuma lada mai yawa. Yace:
[
ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ
]
‚Har da kum a maza da mata masu zikiri da yawa, toh (baki
xayansu) Allah Ya musu tanadin Gafara da kuma wata Lada
mai Girma ‛.
Akwai hadisai masu yawa da suke tabbatar da cewa lallai
bawa zai samu Gafarar Allah matuqar yana yawan
ambatonSa kamar yadda Shari’a ta kara ntar. Daga cikin
zikirorin da Manzon Allah ya kwaxaitar damu mu riqa
karanta su don samun Gafara da kuma lada mai yawa,
akwai waxannan:
Zikirorin safe da yamma:
Karanta wannan addu’a wacce ake kira Sayyidul -Istighf ar
(mafi girma cikin addu’o’in neman G afara ) safe da yamma:
اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي الَ إِلَوَ إِالَّ أَنْتَ، خَلَقْتَنِي وَأَنَا عَبْدُكَ، وَأَنَا عَلَى عَهْدِكَ وَوَعْدِكَ مَا اسْتَطَ عْتُ،
أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا صَن َعْتُ، أَبُوءُ لَكَ بِنِعْمَتِكَ عَلَيَّ، وَأَبُوءُ لَكَ بِذَنْبِي فَاغْ فِرْ لِي، فَإِنَّوُ الَ
ي َغْفِرُ الذُّنُوبَ إِالَّ أَنْتَ
‚Ya Allah Kai ne Ubangiji na, babu abin bauta (bauta ta
gaskiya a bisa cancanta) sai Kai. Kai ne Ka halicce ni. Kuma
ina nan kan umurnin nan n aKa (da Kayi wa bayinKa) da
kuma alqawarin nan naka (wa nda yake tsakaninKa da
bayinKa) gwargwadon iyawa ta. Ina neman tsarin Ka daga
sharrin abinda na aikata (na laifi). Ina mai iqirari (da kuma
godiya gareKa) gameda ni’imominKa a kaina (waxanda babu
wanda yasan yawansu sai Kai). Na na tabbatar lallai ina da
zunubai (masu yawa), ina kuma neman Ka Gafarta min,
domin kuwa babu mai Gafarar zunubai sai Kai ‛.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
52
Manzon Allah yace: ‚ Lallai duk wanda ya faxe ta da rana
alhali yana mai yaqini da ita63, sannan sai yam utu a ranar
kafin maraice, toh yana cikin ‘yan Aljannah. Haka kuma
duk wanda ya faxe ta da dare alhalin yana mai yaqini da ita,
sai yam utu kafin asubahi, toh yana cikin ‘yan Aljannah64‛
Ko shakka babu wannan addu’a tana da muhimmanci sosai .
Ya kamata mu haddace ta, musan ma’anarta, mu koya wa
iyalanmu, kuma mu riqa karanta ta a kullum. Da fatan Allah
Yasa mu dace.
Kuma a riqa karanta wannan zikirin sau xari ( 100) a rana:
الَ إِلَوَ إِالَّ اللَّوُ، وَحْدَهُ الَ شَرِيكَ لَوُ، لَوُ الْمُلْكُ، وَلَوُ الْحَمْدُ، وَىُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ
‚Babu abin bauta da gaskiya a bias cancanta sai Allah, Shi
kaxai Yake Bai da abokin tarayya, dukkan Mulki da dukkan
yabo da godiya naS hi ne (Shi kaxai), kuma Shi ne Mai
cikakken iko akan dukkan komai ‛
Manzon Allah yace duk wanda ya karanta ta sau xari a
rana, ‚ toh daidai yake da wanda ya ‘yanta bayi goma65, za
kuma a rubuta mishi kyawawan ayuka har guda xari66, a
kuma kankare masa munan an ayuka guda xari. Sannan
kuma (wannan addu’a) za ta zame masa (wata irin) kariya
daga shaixan a duk wannan yini har zuwa maraice. Haka
nan kuma babu wanda zai zo (a lahira) da aikinda yafi
(wannan aikin) nashi falala sai wanda ya aikata sama da
abinda ya aikata67‛
63 Wato ya qu durce a zuci cewa da gaske neman gafara yake, kuma ya yarda cewa Allah
Shi ne kaxai Mai Gafarta wa bayi
64 Sahihul -Bukhari (hadithi na 6306 ) daga Sahabi Shaddau xan Aus
65 Mun riga kuma mun ga irin falalar da ‘yanta bawa xaya ma yake da ita a can baya.
66 Tare da kuma duk wani kyakkyawan aiki guda xaya ana ninka shi sau goma ne har zuwa
sau 700 ko ma fiye da hakan, gwargwadon baiwar da Allah Yayiwa bawanSa.
67 Sahihul -bukhari ( 3293 ), Sahih -muslim (2691), daga Sahabi Abu -Huraira
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
53
Wannan zikiri yana da matuqar muhimmanci sosai.
Saboda yana jaddada tauhidin bawa, kuma Yana qara
masa qarfin imani da kuma yaqini da tawakkali, sannan
kuma yana cire wa bawa tsoron wata halitta.
Daga cikin Hanyoyin Samun Gafarar Allah, akwai f axin
waxannan kalamai m asu daraja sau xari a rana, wato a
ce:
سُبْحَانَ اللَّوِ وَبِحَمْدِهِ
‚Dukkan Tsarki da Godiya sun tabbata ga Allah ‛
Manzon Allah yace duk wand ya faxi wannan zikiri sau
xari (100) a rana guda, ‚ Za a Gafarta masa zunubansa ko da
kuwa sun kai kwatankwacin (yawan) kumfar teku ne68‛
Waxannan kalmomi dai suna da sauqin faxi, ga daxi da
kuma zaqin furtawa. Allah ne Ya zava mana su don mu
riqa furtawa don mu samu GafararSa. Mu riqa kula da kyau,
kar mu manta da wannan Sunnah, saboda mu ma mu samu
Rahamar Allah .
Sai dai abin takaici yanzu za ka iske mutum musulmi yana
da lokacin zama yayi ta zabga surutu a wajen hira, yana da
lokacin sauraren duk wata waqa da duk wata sharholiya,
amma bai da lokacin da zai iya warewa domin nitsuwa ya
ambaci Allah . Allah Ya tsare mu daga sharrin shaixan.
A yayin da aka ji kiran sallah
Idan aka ji Ladani yana Kiran Sallah, toh ana so kowa ya
maida hankal i ya saurara da kyau. Saboda a daidai wannan
lokaci akwai wasu zikirorin da Manzon Allah ya umurce
mu da mu riqa furtawa.
68 Sahihul -Bukhari (Hadithi na 6405) daga Sahabi Abu -Huraira
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
54
Daga cikinsu akwai:
أَشْيَدُ أَنْ َلَ إِلَوَ إَِلا اهللُ وَحْدَهُ َلَ شَرِيكَ لَوُ، وَأَنا مُحَمادًا عَبْدُهُ وَرَسُولُوُ، رَضِيتُ
بِاهللِ رَبًّا وَبِمُحَمادٍ رَسُوَلً
‚Na shaida ba bu abin bauta ( a bisa cancanta) sai Allah , Shi
kaxai Yake Bai da abokin tarayya. Kuma lallai Annabi
Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa. Na yarda da Allah a
matsayin Ubangiji . Na yarda da muhammadu a matsayin
Manzo. Na kuma yarda da Musulunci a matsayin Addini (wanda
dole sai ta hanyarsa kaxai za a bau ta wa Allah Ya karva) ‛
Manzon Allah yace duk wanda ya faxi wannan zikiri (a
irin wannan lokacin) ‚ za a Gafarta masa zunubansa69‛
Faxin Kalmar ‚ Ameen‛ a Yayinda aka kai Qarshen Suratul -
Fathiha
Manzon Allah yana cewa: ‚ Yayinda Liman ke faxin
Ameen , toh ku ma ku fax a (tare da shi). Domin kuwa duk
wanda faxinsa ya dace da faxin Mala’iku, toh za a Gafarta
masa abinda ya gabata na zunuban sa70‛.
Zikirin da ake Karantawa Yayin Xagowa daga Ruku’u
Idan aka xago daga ruku’u, Limami yana cewa:
سَمِعَ اللَّوُ لِمَنْ حَمِدَهُ
‚Allah Yana jin mai gode Masa (Kuma Yana amsa addu’ar
duk mai roqon S a)‛
Shi kuma m amu sai yace:
اللَّهُمَّ رَب َّنَا وَلَكَ الْحَمْدُ
‚Ya Allah Ubangijina, dukkan yabo da godiya sun tabbata
gareKa (Kai kaxai b aKa da abokin tarayya) ‛.
69 Sahih -Muslim (Hadithi na 387) daga Sahabi Sa’adu xan Abu -waqqas
70 Sahihil -Bukhari (Hadisi na 780 ) daga Sahabi Abu -Huraira
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
55
Haka Manzon Allah yayi umurni. Kuma yace duk wanda
ya faxi hakan sannan ya dace da na Mala’iku, to shi ma za a
Gafarta masa abinda ya gabata na zunubansa71‛.
Zikirin da ake karantawa bayan Sallama:
Idan aka sallame sallah ma, ai akwai wasu addu’o’I da
zikrori daban -daban waxan da Sunnah ta koyar a riqa
karantawa k afin a tashi72.
Daga cikinsu akwai Tasbihi sau 33, Hamdala sau 33,
kabbara sau 33, daga qarshe kuma a cike da faxin:
َلَإِلَوَ إَِلا اهللُ وَحْدَهُ َلَشَرِيكَ لَوُ، لَوُ الْمُمْكُ وَلَوُ الْحَمْدُ، وَىُوَ عَمَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ
‚Babu abin bauta da gaskiya a bisa cancanta sai Allah ,
Shi kaxai Yake bai da abokin tarayya, dukkan mulki da
godiya baki xaya n aShi ne (Sh i ne Mamallakin komi da
kowa, kuma Shi ne cikakken abin yabo gameda komai),
Kuma shi mai cikakken iko ne akan dukkan komai ‛.
Duk wanda ya karanta waxannan zikirorin kamar yadda
aka ambata, Manzon Allah yace ‚Za a Yafe masa
laifukansa ko da kuwa sun kai k watankwacin yawan kumfar
teku ne73‛
A yayin da aka gama cin abinci (ko abin sha).
Yin Hamdalah bayan an gama cin abinci, yana daga
cikin muhimman hanyoyin samun gafara, mu samman
ma karanta wannan addu’a kamar haka :
71 Bukhari (Hadisi na 796) daga Sahabi Abu -Huraira
72 Zikrorin nan fa dole ne sai irin wax anda Manzon Allah ya karantar kawai za ayi (babu
qari babu ragi).
73 Sahih -Muslim (Hadithi na 597) daga Sahabi Abu -Huraira
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
56
الْحَمْدُ لِماوِ الاذِي أَطْعَمَنِيىَذَا الطاعَامَ وَرَزَقَنِيوِ مِن غَيْرِ حَوْلٍ مِنِّي وََلَ قُواةَ
‚Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda Ya ciyar
da ni wannan abincin, kuma Ya arzuka ni da shi ba tare da wata
dabara ta ko qarfi daga gareni ba ‛.
Manzon Allah yace ‚duk wa nda ya karanta wannan addu’a
bayan ya agama cin abinci, toh za a G afarta masa abinda ya
gbata na zunubansa ‛
L. Jihadi don xaukaka addinin Allah:
Jihadi shi ne tozon Addinin Musulunci74. Kuma Kasuwanci
ne mai riba sosai tsakanin bawa da Mahaliccinsa. A cik in
Suratut -Taubah (ayah ta 111) Allah Yace:
[
ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ
ﯤ ﯥ ﯦ ﯧ ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ ﯯ ﯰ ﯱ
ﯲ ﯳ ﯴ ﯵ ﯶ ﯷ ﯸ ﯹ ﯺ ﯻ ﯼ ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ
]
‚Lallai Allah Ya sayi rayukan Muminai da kuma
dukiyoyinsu, cewa lallai suna da Aljannah (a matsayin
abinda za a biya su da shi). Suna yin (amfani da dukiyoyin
nasu da kuma rayukansu wajen) yaqi cikin (xaukaka)
tafarkin Allah, domin kuwa (a fagen daga ) suna kashewa
kuma su ma ana kashesu. Alqawari ne tabbatacce wanda
Allah Yayi acikn (littatafan) At -Taurah da Injila da kuma
Al-Qur’ani, kuma babu cikakken mai cika alqawarinda ya
xauka irin Allah . Saboda haka ku kasance cikin Albishir
saboda wannan cinikin naku da kuka qulla daShi. Kuma
wannan shi ne babban rabo mai girman gaske .‛
74 Sahih Muslim (Hadithi na 121) daga Sahabi Amru xan Aas
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
57
Jihadi don xaukaka Addinin Allah , wani irin
kasuwanci ne wanda baki xayansa r iba ce zallah babu
faxuwa, domin kuwa da Allah aka qulla shi. Saboda
haka ma daga cikin farashinsa akwai Gafarar Allah da
kuma Aljannah (bayan nasarar da Allah Yayi alqawarin
Zai baiwa duk wanda ya tsaya ya kyautata niyyah yayi
Jihadin da gaske).
A ciki n Suratus -Saff (ayah ta 10 zuwa ta 13) Allah
Yana cewa:
[
ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ
ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ
ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵ ﮶ ﮷ ﮸ ﮹ ﮺ ﮻ ﮼ ﮽ ﮾ ﮿ ﯀
﯁ ﯂ ﯓ ﯔ
ﯕ ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ
13
]
‚Ya ku waxanda kukayi imani! Shin (kuna so) in nuna
muku wani i rin kasuwanci wanda zai zama sanadiyyar tsirar
ku daga azaba mai raxaxi?‛
Wannan kasuwanci shi ne; Kuyi imani da Allah da
ManzonSa r, kuma kuyi Jihad i don xaukaka tafarkin Allah .
Wannan dai shi ne (yafi zama) Alhairi gareku in har da kun
kasance kun sani‛.
Zai Gafarta muku zunubanku kuma Zai shigar daku
Aljannatai waxanda koramu (na ababen sha iri -iri) suke
gudana a qarqashinsu, Zai b aku wasu irin kyawawan gidaje
masu daxin zama a cikin waxannan aljannatai waxanda
suke an riga ayi tanadinsu , wannan dai b abban rabo ne .
Kuma akwai ma sauran (wasu nau’uka na tukuici) na daban
waxanda (tabbas) kuna son su (a wannan rayuwa ta duniy a),
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
58
su ne; Taimako daga Allah75 da cin nasara (akan abokan
gab) wanda yake nan kusa (za ku samu in har kuka qara
qanqame wannan tafark i madaidaici). Kuma (Y a
Muhammadu) kayiwa Muminan nan (masu Jihadi) bishara
(domin kuwa duk abinda suke buqata a duniya da lahira
sakamakon wannan jajircewa da sukayi don kare wannan
Addini) ‛.
Allah Ya yi alqawarin Gafarta wa Mujahidai; domin
kuwa dasu Yake yaxa addininSa, dasu Yake kare addinin,
kuma dasu Yake xaukaka shi akan duk wani addini na
daban wanda ba shi ba. Matuqar musulmi sunyi riqo da
karantarwar wannan Addini na Allah , toh kuwa ba za su
tave ba har abada.
A cikin Suratul -Anfal (ayah ta 74) Allah Yana cewa:
[
ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥ ﯦ
ﯧ ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ
]
‚Su kuma waxanda sukayi imani kuma sukayi kuma
sukayi Jihadi don xaukaka Tafarkin Allah, da (sauran
Muminai) waxanda suka bayar da masauki (ga masu
hijira) kuma sukayi taimako (da duk abind a Allah Ya
hore musu don xaukaka Addinin Allah); waxannan
(baki xayansu) su ne muminai na gaskiya. Suna da
Gafara da kuma wani irin arziki mai yawa (na ababen ci
da sha da duk sauran ababen more rayuwa) irin na
girmamawa ‛.
75 Ta hanyar qara tabbatar da ku akan wannan tafarki madaidaici,Ya kuma karya lagwan
abokan gaba har kuyi galaba akansu.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
59
Allah Ya musu tanadin wasu ir in gidaje na alfarma
acikin Aljannah.
Manzon Allah Yana cewa: ‚ Lallai a cikin Aljannah
akwai wasu irin (benaye masu) darajoji xari (hawa 100)
waxanda Allah Yayi tanadin su ga masu Jihadi saboda
xaukaka AddininSa. Tsakanin kowacce daraja da wacce take
sama da ita kamar nisan da yake tsakanin sama da qasa76‛.
M. Mutuwar Shah ada77
Mutuwar Shahada (Shahada ta gaskiya) tana daga cikin
manyan ni’imomin da Allah Yake yi ga wasu zavavvu
daga cikin bayinSa na qwarai. Kuma duk wani Salihin
bawa ya kasance yana fat an samun wannan daraja ta
shahada.
Saboda; bayan xumbin lada da kuma falalar da take da
su masu yawa, tana ma cikin manya -manyan hanyoyin
samun Gafarar Allah .
Bayan ayoyin Al -Qur’ani, akwai Hadisai ma masu yawa
da sukayi bayanin falalar mutuwar Shahada.
Falalar mutuwar Shahada
Ga kaxan daga cikinsu78 insha’Allah:
Za a yafe wa mai mutuwar Shahada laifukansa tun a.
daga xigon jininsa na farko a lokacinda yazo mutuw a.
Tun a lokacin za a nuna masa mazauninsa na cikin b.
Aljannah.
76 Sahihul -Bukhari (hadithi na 2790) daga Sahabi Abu -Huraira
77 Mutuwar mumini a yayinda yake fafitikar kare Addini a fagen daga, ko kuma a kashe shi
a yayinda yake faman kare mutuncinsa ko mutuncin iyalansa , ko kuma a yayinda yake
faman kare dukiyarsa, ko kuma wata hanya daga cikin hanyoyin da shari’ah tayi bayani.
Allah Ya arzukta mu da irin wannan mutuwa.
78 Daga kan ‚‛ zuwa ‚ ‛ duk sun zo a dunqule cikin hadisi guda, duba: Tirmizi ( 1663 )
daga Miqdaamu Ibn Ma’adiy -karib
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
60
Za a amintar dashi daga fitinar Qabari (ba za a fitine shi c.
ba, kuma ba za a azabtar da shi ba).
d.
Za a amintar da shi daga wannan firgici mafi girma na
ranar qiyamah (saboda haka bai da fargaba kuma babu
baqin ciki tare da shi har abada79).
A lahira za a xaura masa wani irin kambe na girmamawa e.
a kansa, na yaqutu, wanda guda xaya daga cikinsu ya fi duk
duniya da abinda yake cikinta.
Za a xaura masa aure da wasu mata na musamman (har f.
su 72) daga ci kin matan Aljannah (tun a lokacinda ake z are
ran shi daga gangar jikinsa).
g.
Kuma a lahira za a bashi damar ceton har mutum 70
daga cikin danginsa.
Ba ya jin zafin fitar rai, sai kamar gwargwadon zafin *
cizon cinyaka80
A cikin Aljannah kuma, zai riqa burin inama ayi ta dawo *
dashi duniya a qara kashe shi ta wannan hanya har sau
goma. Ba don komi ba sai saboda irin abinda ya gani na
falalar shahada81, da irin girmamawar da ya samu a cikin
Aljannah .
Waxannan dai suna daga cikin jerin falalolin da mutuwar
shahad a ta gaskiya take tattare da su. Na ce shahada ta gaskiya
ne, saboda akwai waxanda ba na gaskiya ba. Toh su (na
qaryan) banda su a cikin waxanda za su samu wannan falalar
da akayi bayani. Domin kuwa babu wanda zai samu sai wanda
ya cika sharuxan karvar iba da (wato yi don neman Yardar
Allah , da kuma dacewa da karantarwar Manzon Allah ).
79 Za atsare masa iyalansa (waxanda ya mutu ya bari a duniya), ba za su tagayyara ba,
kuma insha’Allah ba za su kauce hanya ba su ma.
80 Imam Ahmad ( 7953 ), Tirmizi (1668), Nasa’i ( 3161 ), Ibn Hibban ( 4655 ).. Daga Abu -
Huraira .
81 Bukhari ( 2817), Muslim ( 1877 ) duk daga Sahabi Anas xan Maalik
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
61
Za mu gane hakan ne idan muka san kashe -kashen
shahada. Ga su nan (a gurguje) kamar haka insha’Allah.
Saboda lura da nassoshin Al -Qur’ani da kuma ingantattun
hadithai, Malamai sun karkasa nau’ukan shahada zuwa kashi
uku. Su ne kamar haka:
1) Sukace akwai masu hukuncin shahda a duniya kaxai, banda
lahira.
Su ne waxanda a idanun mutane dai mutuwar shahda sukayi,
amma a wajen Allah su ba shahidai ba ne, saboda basu cika
sharuxan karvar aiki ba.
Su ba shahidan gaskiya ba ne. Shahidan qarya ne. Amma da
yake babu wanda yasan matsayinsu sai Allah (Masanin
baki xaya voyayyu da bayyanannun al’amura), toh dole za
ayi musu yadda ake wa shahidan gaskiya anan duniya.
Don haka ba za ayi musu wanka ba kuma ba za ayi musu
Sallah ba, A hakan za a xaukesu cikin jinin nasu aje a binne a
maqabartar Musulmi ( tunda a filin yaqi aka kashesu, kuma
babu wanda yasan abinda suka qudurce a zuci sai Allah ).
-Su ne irin munafukan nan waxanda saboda qwarewa a
munafunci har ma sun kai ga suna bin Musulmin qwarai
Jihadi (saboda wasu manufofi nasu na karan kansu), sai k uma
suyi rashin sa’a ta ritsa da su a cikin gumurzun yaqi a kashe
su a can.
-Daga cikin masu irin wannan hukunci akwai wanda zai tashi
yaje filin jihadi kuma a kashe shi a chan, amma ba don kare
addinin Allah yaje ba shi kam. Ya je ne kawai don ya nuna
wa duniya cewa shi ma fa jarumi ne.
Waxannan kam a lahira basu da komai awajen Allah sai
azaba mai tsanani. Suna ma cikin jerin mutum uku waxanda
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
62
dasu ne za a hura wutar jahannama a ranar (su zasu fara shiga
wuta kafin duk wani kafiri).
2) Akwai kuma mai huku ncin shahada a lahira kaxai banda
duniya. Shi kam ana wanke gawarsa, kuma ana masa Sallah,
sannan aje a binne shi a maqbartan Musulmi.
Shi ne wanda ya mutu ta xaya daga cikin waxannan hanyoyi
(alhalin yana musulmi):
-Wanda ya mutu a yayin kare dukiyarsa, d a mutuncinsa dana
iyalansa,
-Wanda akayiwa kisar gilla saboda kaxai ya yi riqo da
Addinin Allah, ko ma yana kira zuwa gareshi (amma ba a
filin yaqi aka kasheshi ba),.
-Irin wanda ruwa ya cinye shi,
-Wanda gini ya rushe akansa ya kashe shi,
-Wanda gobara ta zama ajalinsa,
-Wanda ya mutu sanadiyyar wata annoba ta cuta da ta varke a
garinda yake,
-wanda ya mutu sanadiyyar ciwon ciki (irin matsanacin
ciwon cikin nan mai murxe mutum ya kasha shi lokaci guda,
-Wacce ta mutu sakamakon wahalar naqudar haihuwa,
Da d ai sauran makamantansu waxanda hadisai sukayi
bayanin cewa su ma suna da darajar shahada.
Saboda haka za su samu falalar da shahidin gaskiya yake
samu gwargwadon hali insha’Allah.
3) Sannan akwai kuma wanda aka fi sani da wannan suna na
shahidi, wato mai huk uncin shahada a duniya da lahira baki
xaya.
Shi ne Muminin da aka kashe shi a filin ya qi tsakanin
musulmi da kafirai.
Wannan a duniya hukuncin gawarsa daban ne da sauran
gawaki. Domin kuwa ba a masa wanka, kuma ba a masa
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
63
Sallah. Haka za a xauke shi cikin jinin nashi a binne shi a
wurinda ya mutu xin.
Sannan kuma a lahira, yana da waxancan falalolin da aka
ambata acikin ayoyi da ingantattun hadithan da sukayi
bayanin falalar mutuwar shahada. Daga falalolin dai, akwai
samun Gafarar Allah .
Allah Zai Yafe wa duk wanda yayi mutuwar shahada da
kyakkyawar niyyah (kuma yake kan tafarkin Manzon Allah
). Zai yafe masa baki xaya zunuban da ya aikata. Amma fa
laifukanda yayiwa Allah ne kaxai za a yafe masa, banda
haqqin mutane82.
Domin kuwa Manzon Allah ya ce: ‚ Allah Zai
Gafarta wa Shahidi dukkan komai (na laifinda ya aikata
a rayuwarsa) fahce bashi83 (wanda wasu suke binsa) ‛.
Allah Yasa mu gama da duniya lafiya, Ya tsare mu daga
taurin bashi da kuma rinjayen maqiya, da kuma
mummunan abin ji da mummunan abin gan i a duniya da
lahira.
Allah Ya Arzukta mu da mutuwar Shahada ta gaskiya.
(Hanya ta Bakwai)
(sawa’un a jikinsa ne ko iyalansa ko dukiyarsa)
82 Idan akwai haqqin wani akansa kam, toh wannan hukuncinsa daban. Mun riga mun ga
bayani akan wannan tun a farkon wannan littafi, inda aka lissafo sharuxan tuba. Allah Yasa
mu dace.
83 Sahih -Muslim (hadith i na 1886) daga Sahabi Abdullah xan Amru xan Aas (shi da
Mahaifin naashi baki xayansu sahabbai ne) Allah Ya qara Yarda dasu.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
64
Jarrabawa sunnar Allah ce. Rayuwar ma baki xayanta
jarraba wa ce. Domin kuwa an kawo mu duniya ne don
mu rayu a cikinta na wani lokaci, wanda a ciki ne za mu
aikata abinda za a saka mana da shi bayan mutuwar mu.
Allah Yana cewa (a farkon Suratul -Mulk):
[
ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ
ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ
ﭝ
ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ
]
‚Albarkatun (Allah) sun yawaita, wanda b aki xaya mulki
(mallakar komi da kowa) a hannunSa yake, kuma Shi xin
mai cikakken iko ne akan dukkan komai. Shi ne wanda
wanda Ya halicci mutuwa da rayuwa baki xaya, domin Ya
jarraba ku (Ya w are su waye ne) daga cikinku masu
kyautata ayukansu. Kuma Shi ne Mabuwayi Mai Gafara ‛.
Kowa daga cikin mutane akwai nau’in jarabawar da
Allah Yake masa a rayuwa. Akwai waxanda ake
jarabtar su da jin daxin rayuwa, akwai kuma waxanda
ake jarabtar su da wahalha lun rayuwa.
Wasu ana jarabtar su ta dukiyoyinsu, wasu ta iyalansu,
wasu ta mulkinsu, wasu ta lafiyarsu, wasu ta iliminsu
(na addini ko na zamani), wasu ma ta sashen addininsu,
da dai sauransu. Kowa ana jarabtar shi ta waxannan
fannoni na rayuwa (da ma sau ran da ba’a ambata ba)
imma da jin daxi ko kuma akasin hakan.
Allah Yana cewa:
[
ﯺ ﯻ ﯼ ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃ ﰄ ﰅ
]
:األنبياء{
35
}
‚Kowacce rai (dole) za ta xanxani mutuwa. Kuma Muna
jarabtar ku da sharri (dangin ababenda kuke qi) da kuma
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
65
Alkhairi (dangin ababenda kukeso) don kawai Mu gwada
ku. Kuma gareMu za ku koma (Mu baku sakamakon duk
abinda kuka aikata a rayuwarku ta duniya) ‛
Ga abinda ya dace bawa yayi idan Allah
Ya jarabce
shi da wani abu na jin daxin rayuwa:
Lallai kam daga cikin mutane akwai wanda za a b ashi
xaukaka ko dukiya ko lafiya da sauran ababen jin daxi na
rayuwar duniya (wani za a haxa masa masu yawa, wani
kuma kaxan, wani ma guda xaya za a bashi gwargwadon
hali), ba don komi b a sai don a jarraba godiyarsa.
Mai rabo a wajen Allah shi ne zai go de maSa akan duk
wata ni’imar da Ya bashi. Hakan kuma zai zama sanadiyyar
samun qari daga Allah , da kuma albarkar rayuwa, da tsira
daga uqubarSa a duniya da lahira.
Shi kuma mara rabo, toh zai butulce yaqi gode masa.
Hakan kuma zai zama sanadiyyar fush in Allah da uqubarSa
gareshi a duniya da lahira (in har bai tuba ya koma ga Allah
ba). Don haka a cikin Suratu Ibrahim (ayah ta 7) Allah
Yake cewa:
[
ﭭ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ
7
]
‚Tuna lokacinda Ubangijinku Ya shelanta cewa ‚Lallai in
har kunyi godiya (gam eda ni’imomin da Nayi muku) toh
Zan qara muku. In muka kuka butulce, toh fa (ku sani) lallai
azabah Ta mai tsanani ce ‛
Allah Ya b amu misalai masu yawa akan wannan al’amari
a cikin wasu ayoyi na al -Qur’ani Mai girma, gameda masu
gode miShi da kuma masu bu tulci.
Ya faxi halaye da kuma sakamakon kowanne daga cikinsu.
Duk hanyar da mutum ya zava 9sawa’un shiriya ce ko vata),
toh akwai sakamakon da aka tanadar wa masu bin ta.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
66
Kai tsaye za mu gutsuro kaxan daga cikin kowanne vangare
don buga misali insha’All ah. Da fatan Allah Maxaukaki Ya
sanya mu cikin bayinSa shiryayyu masu gode maSa, Ya
tsare mu daga kasancewa vatattu masu butulce maSa.
Daga cikin Misalan masu godiya akwai labarin Annabi
Sulaimanu84 . yayinda ya ga an bi umurninsa anyi abinda
duk duniya b abu sarkin wani gari da zai iya samun hakan);
sai yace:
[
ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴
﮵
]
:النمل{
40
}
‚Wannan (lallai) falal ce daga cikin falalar Ubangiji na (ba
iyawa ta bace ko dabara ta ko qarfin mulki na). Ya yi hakan
ne kuma don Ya jarabce ni (Ya gani) shin godiya zanyi ko
kuma zan butulce ne? Lallai duk wanda yayi godiya (ga
Allah a bias wata ni’imar da Yayi masa) toh fa ya yi godiyar
ne don kansa (saboda shi ne zai samu sakamakon aikinsa a
gobe qiyamah). Wanda kuma ya butulce (ya qi godewa
Allah, toh fa kansa yayiwa) domin kuwa lallai Ubangiji na
cikakken Mawadaci ne kuma Mai Karimci ‛
A farko -farkon Suratul -Isra’i Allah Ya yabi bawanSa
Annabi Nuhu saboda shi bawa ne mai yawan godiya ga
Allah, inda Yake cewa:
[
ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ
]
:اإلرساء{
3
}
‚Lallai shi (Annabi Nuhu ) ya kasance bawa ne mai
yawan godiya ‛
84 Wanda shi Annabin Allah ne, kuma Allah Ya baashi ilimi mai faxin gaske, sannnan
kuma Ya bashi mulki sama da na kowa daga cikin bayi, domin kuwa bayan mutane har ma
da aljanu da dabbobi dukka yake mulka, kuma idan yayi umurni babu mai sava masa daga
cikinsu.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
67
Duk mai godiya ga Allah (godiya irin ta shari’a85) toh
haqiqa yay i koyi da Annabawan Allah (Tsira da Amincin
Allah su qara tabbata garesu baki xayansu).
Hakan zai sa Allah Ya qara masa, kuma Ya albarkaci
rayuwarsa, kuma Ya yarda da shi, kuma Allah Zai tsare
shi daga uqubarSa ta duniya da lahira (irin wacce Yake yi
wa masu butulci).
Wannan kenan!
Sannan akwai kuma irinsu qaruna, waxanda suka butulce a
yayinda suka ga sun bunqasa. Sai Allah Ya saukar da
uqubarSa akansu, Ya kawar da su.
Wasu Malamai daga cikin mutanensa sun yi ta masa wa’azi
akan ya daina alfahari da kuma girman kai, saboda hakan ba
xabi’a ce ta masu rabo a wajen Allah ba. Shi kuma
qaruna sai qara cika baki yakeyi yana ta taqama. Bai ma
yarda cewa wannan dukiyar tashi daga Allah take ba. Gani
yake kamar iyawarsa ce ta bashi (saboda haka babu wanda
zai godewa, kuma ba zai bi umurnin kowa ba) .
Har ma yana hura hanci yana cewa cewa:
[
ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ
القصص: { ]
78
}
‚Ni fa (wannan du kiyar da kuke gani) na same ta ne
sakamakon ilimin da nake dake da shi (ma’ana: ilimina ne
ya bani, ba Allah ba)‛. Sannan saiYace:
85 Godiya irin wacce ake kira ‚Ash -shukr‛ a larabce; it ace yayin da bawa ya sarrafa duk
wata ni’imar da Allah I Ya baashi ta hanyar da Allah xin Ya yarda da shi. Idan dukiya ce
ko ilimi ko wani vangare na mulki da sauransu, toh lallai ne bawa ya kiyaye haqqin Allah a
ciki kuma Ya tsare dokokin Allah a yayin sarrafa su. Idan ‘ya’ya ne, lallai ne ne bawa ya
tarbiyyantar da su tar biyyah ta addini. Wannan shi ake kira godiya a shari’ance, ba
tsagwaran furta Hamdallah da fatar baaki kawai ba. Allah Yasa mu dace.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
68
[
ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ
ﭪ ﭫ ﭬ ﭭ ﭮ
]
Shin (wannan kangararren bawa) bai san cewa Allah Ya
halakar da waxanda s uka fi shi tsananin qarfi da kuma t arin
dukiya ba a cikin qarnonin da suka shuxe gabanin sa, kuma
ba Ya tambayar masu laifi gameda (dalilin) aikata
zunubansu (idan Ya tashi halakar da su, domin kuwa babu
wani sauran hanzari garesu)‛ A can gaba sai Allah Yace:
[
ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ
ﮧ ﮨ
]
‚Sai muka sanya qasa ta haxiye shi daga shi har (katafaren)
gidan nasa (wanda yake alfahari da shi). Ya kasance bashi
da wasu tarin mutanen da za su iya taimakonshi (babu mai
kuvutar da shi daga wannan halaka) koma bayan Allah ,
kuma shi bai kasance daga cikin masu (ikon) taimakon
kawunansu ba‛
Abinda ya zama wajibi akan duk wanda Allah Ya bashi
wani abu na jin daxi a rayuwarsa ta duniya, shi ne ya gode
wa Allah (ya sarrafa wannan ni’ima ta hanyar neman
yardarSa). Kar yayi butulci, kar yayi xagawa ko taqama ko
cika baki. Banda qoro kuma banda al -mubazzaranci.
Idan ka godewa Allah , toh Zai albarkaci abin, kuma Zai
Yarda da kai. Idan kuma mutum ya butulce, toh ko shakka
babu qarshen lamarin ba zai masa daxi ba. Allah dai Ya
rufa mana asiri.
Idan aka jarabci bawa da wata wahala ko quncin
rayuwa, da sauran ababenda zuciyarshi bata so:
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
69
A irin wannan yanayi ana buqata bawa yayi haquri, ya
maida lamarinsa ga Allah , Ya kuma nemi ladar wannan
wahala a wajenSa.
Jarrabawa Sunnar Allah ce. Kuma babu mai cin
jarrabawar Allah Ta’ala sai wanda Yayi wa gamon katar.
Allah Yasa mu cikin masu rabo.
Jarrabawa mai raxaxi (irinsu talauci da rashin lafiya da
sauransu) ba ta daga cikin alamun da suke nuna wai Allah
ba Ya so n bawanSa. Domin kuwaYa jarabci hatta
manyan bayinSa ma da nau’ukan wahalhalu iri -iri a
rayuwarsu.
Haka kuma samun xaukaka a duniya, da havakar tattalin
arziki da sauransu, ba su suke nuna wai Allah Yana son
mutum sama da waxanda basu samu ba.
Ayoyi da hadithai masu yawa sun tabbatar da cewa ‚Lallai
Annabawa da Manzanni (Tsira da Amincin Allah su qara
tabbata a garesu) su ne suka gamu da jarrabawa mafi tsanani
daga cikin bayin Allah. Sannan kuma duk wanda ya bi
tafarkinsu, toh zai samu jarrabawarsa gwarg wadon iya
koyin da yayi da su. Domin kuwa ana jarabtan bawa ne
gwargwadon qarfin Addininsa.‛
Annabawa da Manzanni masu yawa jama’ansu sun qaryata
su, an zage su, an musu izgilanc i. Wasu an kore su daga
gari, was u an kama su an kulle a gidan y ari anyi ta ga na
musu azaba, wasu ma kisan gilla akayi musu. Wasu daga
cikin Annabawan kuma, tsantsar talauci da matsatsi sukayi
ta fama da shi, akwai wanda ya kamu da rashin lafiya mai
tsanani, akwai ma wanda ya shiga yanayinda har kifi ya
haxiye shi..
Amma duk hakan b ai hana su ci gaba da tabbata akan
wannan Tafarki madaidaici ba. Sun tsayu akai, sun jajirce
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
70
sun cigaba da kiran jama’arsu akai har Allah Ya karvi
rayuwarsu.
Haka akeso mu ma mu zama. Mu nemi taimakon Allah
akan duk wata wahala ta rayuwa, da fatan All ah Ya hana ta
tasiri wajen kautar damu hanya.
Waxannan nau’uka na jarrabawa masu raxaxi suna da nasu
amfani ga bawa matuqar dai ya karvi lamarin da zuciya
guda (matuqar ya yi haquri ya maida komi ga Allah
kuma ya nemi l adan hakan a wajenShi). Idan har y ayi
hakan, toh Zai yafe masa laifukansa kuma Zai bashi lada
mai yawa.
Allah Ya yi alqawarin Zai xaukaka darajar masu haquri,
Zai tabbatarda su akan Tafarkin shiriya, Zai Gafarta musu
zunubansu, sannan kuma Zai musu Rahama a duniya da
lahira.. Babban misa li akan wannan shi ne (cikin Suratul -
Baqara, ayah ta 155 - 157) inda Allah Yake cewa:
[
ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ
ﭬ
البقرة: { ]
155
}
‚Kuma lallai ne, za Mu jarabce ku da wani abu na tsoro da
yunwa, da tawaya daga dukiya, da (asarar) rayuka da na
‘ya’yan itace (amfanin gona). Don haka kayi bishara ga
masu haquri‛
[
ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ
]
:البقرة{
156
}
‚Su ne waxanda suka kasance idan wata masifa ta same su,
sais u ce: lalle mu daga Allah muke, kuma lallai zuwa
gareShi za mu koma‛
[
ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ
]
البقرة{:
157
}
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
71
‚Waxannan lallai akwai Albarkatu da kuma Rahma (da za
su riqa sauka) akansu daga Ubangijinsu, kuma waxannan su
ne shiryayyu‛.
Rashin Lafiya
Idan Musulmi ya kamu da rashin lafiya, wannan ciwo zai
zama kaffarah gareshi (za a kankare masa laifinsa) ma tuqar
ya maida lamari ga Allah , ya yarda da hukuncin Allah ,
ya yarda cewa Allah ne ya xora masa.
Allah Yana xora wa bawa irin waxannan nau’uka na
jarrabawa ne, saboda Ya kankare masa zunubansa dasu,
sannan kuma Ya bashi lada mai yawa, kuma Ya xaga
darajarsa.
Manzon Allah yana cewa: ‚Babu wani abinda zai sami
Musulmi (a rayuwarsa) na yunwa ko rashin lafiya ko
damuwa ko baqin ciki ko wata cutarwa ko wani qunci –har
ma da qayar da za ta soke shi - fahce Allah Ya kankare masa
laifukansa da su86‛
A ciki n wani hadisin (riwayar Tirmidhiy daga Sahabi Abu -
Huraira ) Manzon Allah yace: ‚Jarrabawa ba za ta
gushe ba (tana sauka) ga mumini [da kuma mumina] a cikin
jikinsa ko ‘ya’yansa ko dukiyarsa, har sai gamu da Allah
(a lahira) babu wani laifi akansa (dom in kuwa Zai kankare
masa zunubansa sakamakon raxaxin da yayi ta ji a yayinda
wannan jarrabawa ta same shi)‛.
Ashe idan mumini ya kamu da rashin lafiya, wannan wata
dam ace da Allah Yake bashi don ya tuba ya koma ga
Allah, kuma ya samu ladan haquri, sanna n kuma ciwon ya
zama kaffara gareshi gameda zunuban da ya aikata. Shi yasa
86 Bukhari ( 5643 ), da Muslim ( 2573 ) Daga Abu -huraira t da Abu -Sa’id Al -khudri
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
72
Manzon Allah ya kasance idan yaje duba mara lafiya
musulmi, daga cikin addu’o’inda yake masa akwai:
َلَ بَأْسَ طَيُورٌ إِن شَاءَالماوُ
‚Babu laifi, ciwon naka mai tsarkakewa ne ( daga
zunubanka) in Allah Ya Yarda87‛
Haquri gameda rasuwar xa ko xiya:
Idan bawa yayi haquri ya daure kuma ya nemi lada gun
Allah a yayinda ya rasa xa ko xiya, toh hakan ma
yana daga cikin hanyoyin samun Gafarar Allah (bayan
xumbin ladan da zai samu saka makon hakan)
insha’Allah.
Manzon Allah yace: ‚Babu wasu musulmi biyu (miji
da matarsa) da za su rasa ‘ya’ya qanana har guda uku
(kuma suyi haquri su mayarda lamarinsu ga Allah )
fahce an Gafarta musu88‛
A wata riwayar ma, Manzon Allah cewa yayi: ‚Duk
wanda ya nemi lada (haqurinda yayi) gameda rashin har
(‘ya’ya) uku daga cikin tsatsonsa, toh zai shiga Aljannah
(sakamakon hakan)‛. Sai wata mace tace: ‚Har da mai
biyu ma (Y a Manzon Allah)?‛ Yace mata: ‚Har mai
biyu ma89 (shi ma zai samu irin wannan sakamak o)‛.
Wasu hadisai ma sun tabbatar da cewa hatta wanda ya
rasa xa guda ma zai samu irin wannan sakamako
87 Bukhari ( 3616 ) daga Abdullahi xan Abbas Al lah Ya qara musu Yarda (shi da mahaifin
nashi).
88 Nasa’i (Hadithi na 1874 ) daga Sahabi Abu -Dharrin Al -Ghifariy
89 Musnad na Imamu Ahmad (Hadithi na 27429 ) Daga Sayyida Ummu -Sulaim (Mahaifiyar
Anas xan Malik) Allah Ya qara musu yarda.. Akwai ma’anar wanna n hadithi cikin Sahihul -
Bukhari da kuma Sahih Muslim a wurare daban daban.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
73
insha’Allah. Da sharaxin dai za ayi haquri tun a farkon
fari, a mayar da lamari ga Allah , kuma a nemi ladan
wannan haquri da juriya awajenSa. Toh idan har bawa
ya rasa xansa kuma yayi haquri ya maida komai ga
Ubangijinsa, Allah Zai ce wa Mala’iku: ‚Ku gina wa
bawa Na gida a cikin Aljannah, kuma ku sanya wa
gidan suna بَيْتُ الْحَمْدِ (gidan godiya, wanda sai masu
godiya ga Allah akan komai ne kaxai zas u sami
irinta)90‛
Manzon Allah yace: ‚Babu wani wata kyautar da za
baiwa wani (daga cikin bayi) wacce take cike da
Alkhairi kuma wadatacciya irin kyautar haquri91‛.
Saboda girman matsayin haquri, babu wanda yasan
yawan ladan da bawa zai samu idan yayi haqu ri sai
Allah kaxai.
A cikin Suratuz -Zumar (ayah ta 10) Allah Yana cewa:
[
ﰓ ﰔ ﰕ ﰖ ﰗ ﰘ ﰙ
الزمر: { ]
10
}
‚Masu haquri ne kaxai ake cika musu ladan sub a tare da
qididdiga ba‛
Renon ‘ya’ya mata, da kuma kyautata Tarbiyyarsu har
su girma.
Wannan ma yana dag a cikin muhimman hanyoyin samun
Gafarar Allah , da RahamarSa da AljannarSa.
Manzon Allah yace: ‚Duk wanda aka jarabce shi da
(renon wani adadi daga cikin) waxannan ‘ya’ya mata, kuma
90 Tirmizi (1021) daga Abu -Musa Al -Ash’ari . Hadithi ne mai kyau. Duba As -Sahiha
(1408 ).
91 Bukhari (6470) da Muslim (1053) daga Sahabi Abu -Sa’id Al -khudri
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
74
ya kyautata musu (tarbiyyah), toh za su kasance gareshi
shamaki tsakani nsa da wuta (a gobe qiyamah)92‛.
A wata riwayar Imam Ahmad da Ibnu Majah kuma,
Manzon Allah cewa yayi: ‚Duk wanda ya kasance yana
da ‘ya’ya mata har uku, kuma yayi haquri (ya daure ya
tarbiyyantar dasu) ya ciyar dasu ya shayar dasu ya kuma
tufatar dasu da ga abinda ya mallaka; toh za su kasance
shamaki gareshi daga wuta a ranar tashin qiyamah‛.
Daurewa a kyautata Ibada a yayinda ake cikin tashe -
tashen hankula da kashe -kashe
Sau da dama (musamman a wannan zamani) ana samun
tashe -tashen hankula a yankunan da muke yaruwa. Mutane
za su lalace suyi ta varna, kuma babu mai hana su. Za a
wayi gari ana ta’addanci iri -iri. Masu Mulki su kangare suyi
ta cin zalin talakawansu. Kuma sau da dama babu waxanda
aka fi cutarwa a irin waxannan lokuta irin masu riqo da
addini.
Toh idan bawa yayi haquri ya daure ya jajirce ya tsaya ya
bauta wa Allah a irin wannan lokaci, toh hakan yana daga
cikin hanyoyin samun Gafarar Allah .
Domin kuwa Manzon Allah yana cewa: ‚Bautar Allah
acikin lokaci na haraj (wato kashe -kashe da yaqe -yaqe)
kamar hijira ce zuwa gareni93‛.
Sanannen abu ne kuma Hijira ma tana shafe abinda ya
gabaceta na laifuka, kamar yadda Imam Muslim y a ruwaito
(hadisi na 121) daga Sahabi Abdul lahi xan ‘Amru xan As,
Allah qara Yarda dasu baki xayansu.
92 Bukhari (5995), Muslim (2629), Dukkansu daga Nana A’isha Allah Ya qara Yarda da
ita.
93 Sahih Muslim (Hadithi na 2948) daga Sahabi Ma’aqili xan Yasaar
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
75
Ko shakka babu idan har bawa ya jajirce ya tsaya akan
gaskiya a irin lokacinnan da mutanen banza sukayi yawa
hatta cikin al’ummar Musulmi, toh zai samu babbar daraja
awajen Allah . Allah Zai bashi ladan haquri, kuma Zai
sanya shi cikin bayinSa nagari (mas u rabauta a duniy a da
lahira).
Shi yasa a cikin Suratu -Hud (ayah ta 11) Allah Yake
cewa:
[
ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ
]
‚Sai waxanda sukayi Imani kuma suka aikata ayuka na
qwarai, waxannan kam suna da Gafara da kuma Lada
mai Girma‛
Haka kuma idan bawa yayi haquri saboda wata cutarwar
da akayi masa (aka ci masa mutunci, akayi masa izgili
ko qage da yarfe da qazafi da kuma vata suna) ba don
komai ba sai don kaxai ya yi riqo da addin Allah, Toh
hakan yana daga cikin hanyoyin samun Gafarar Allah,
da AljannarSa.
Allah Yace irin bayin nan naShi waxanda aka cutar dasu
(akayi ta musu izgilanci a duniya sakamakon riqon su da
addini), toh zai saka musu a lahira saboda haqurinda sukayi.
Zai saka musu da Aljannah, kuma Zai goranta wa masu yi
musu izgili (bayan su kuma masu izgilin suna cikin wuta).
Acikin Suratul -Muminun (ayah ta 109 - 111) Allah Yana
cewa:
[
ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ
‚Lallai wani kaso daga cikin bayiNa sun kasance suna cewa
Ya Ubangijin mu munyi imani, saboda haka Ka Gafarta
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
76
mana kuma Kayi mana Rahma, domin kuwa Kai ne Mafi
Jinqan Masu Jinqai.
ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ
Sai ku kuma kuka riqe su ababen yiwa izgili (kuna ta
tsokanarsu saboda sunyi riqo da addini), har (suka shagaltar
daku) suka mantar daku ambato Na, kun kasance kuna ta
musu dariya (saboda kawai sunyi ima ni).
ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑ
]
Toh lallai Ni Na saka musu yau (Na basu Aljannah) saboda
haqurinda sukayi (akan cutarwar da kukayi ta musu a
duniya), lallai kuwa su xinnan su ne masu babban rabo‛.
Shi ma wanda akayiwa qazafi don neman ganin bayansa
saboda kawa i ya yi riqo da addini, Allah Ya yi masa
alqawarin Gafara da kuma girmamawa. Ya faxi hakan ne a
cikin Suratun -Nur (qarshen ayah ta 26, cikin ayoyinda Ya
wanke Uwar mu Nana -A’isha daga qazafinda munafukai
sukayi mata94).
Allah Yace:
[
ﯥ ﯦ ﯧ ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ
]
‚Irin waxannan su ne waxanda ake barrantarwa daga
abinda (masharranta) suke faxa. Suna kuma da Gafara
da kuma wani irin Arziki na girmamawa‛
94 Hadisin wannan qazafi ya zo cikin littatafan hadisi da kuma sirah masu yawa. Babban
misali akan wannan, shi ne hadisi na 4141 cikin Sahihul -Bukhariy, hadithin Nana -A’isha
xin (ita da kanta ta bayar da wannan labara). Waxanda suka kitsa wannan qazafi dai sunyi
ne saboda cin mutunci ga Manzon Allah gameda iyalansa. Kuma abin takaici, ‘yan shi’a
suna ci gaba da zargin ta da wann an laifi, bayan Allah Ya wanke ta a cikin Al -Qur’ani.
Kuma daga baya su saxaxo su ce wai su ma suna qaunar Manzon Allah . wallahi qarya
sukeyi. Su cikakkun maqiya ne ga Allah da ManzonSa da kuma AddininSa.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
77
Idan aka zartar da haddi (irin na shari’a) akan bawa
saboda wani laifinda ya aikata:
Haddin da akayi wa bawa y ana shafe wannan laifinda yayi.
Zai zamto kaffarah gareshi, ta yadda ba za ayi masa uquba
akan wannan laifin ba a lahira. Saboda haka haddi ma yana
daga cikin hanyoyin samun Gafarar Allah kenan.
Za mu ga shaidar hakan a cikin hadisin wata matar da aka
tsayar mata haddin rajamu (jifa da tsakuwa sakamakon an
kama ta da laifin zina alhalin ta tava aure) a zamanin
Manzon Allah .
Bayan ta mutu ai Manzon Allah ne yayi mata Sallah. A
lokacinda ya shige gaba don ya jagoranci Sallar ma, har
Sayyiduna Umar yake cewa: ‚Y a Ma’aikin Allah ta yaya
kuma (kai da kanka) za ka sallaci wannan mata alhali kuma
zina tayi?‛ Sai Manzon Allah yace masa: "Haqiqa ta yi
wani irin tuba wanda ko da za raba wa mutum saba’in daga
cikin mutanen wannan birni na Madinah, da zai is he su95‛
Fitintinun Qabari (Allah Ya tsare mu)
Daga cikin Musulmi ma akwai waxanda za a fitinesu a cikin
qaburburansu. Za a fitini kowa daga cikinsu ne
gwargwadon aikinsa, sai wanda Allah Ya kuvutar dashi
kawai .
Manzon Allah yace Shahidi ne kaxai ba za a fitine shi ba
a cikin qabarinsa96. Har ma yace: ‚Da ace akwai xaya (daga
cikin mutane) da zai kuvuta daga matsa irinta qabari, da
kuwa (Sahabi) Sa’adu xan Mu’azu ne zai tsira97‛
95 Muslim (Hadisi na 1696) daga Sahabi Imran xan Husain .
96 Imam An -Nasa’iy (hadisi na 2053 ). Yana ma cikin littafin At -Ta’liq ar -Raghib ( 2/197 )
97 Imam Ahmad, daga Abdullahi xan Umar (Allah Ya qara yarda da su). Shaykh Albaniy
yace hadisin ya inganta (duba As -Saheeha, hadithi na 1695 )
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
78
Mutane sun kasu har wajen kashi biyar daban -daban a cikin
rayuwar su ta qaba ri:
a. Akwai waxanda su kam azaba ce zallah iri -iri zasu yi ta sha
tun daga cikin qabari har zuwa lahira, kuma za su dawwama
a wuta.. Waxannan su ne Kafirai da kuma Munafukai.
b. Akwai kuma waxanda su ma za su sha azabah a cikin
qabari, kuma a lahira za su shiga wuta su daxe a ciki.
Amma su ba za su dawwama a cikinta ba, saboda ba akan
kafirci suka mutu ba. Illa iyaka za a musu uquba ne
sakamakon zunubansu masu yawa sosai (waxanda har suka
mutu basu tuba sun daina ba), kuma ba’a ga damar yafe
musu ba. Daga baya z a a fitar dasu daga wutar, a wanke su,
a shigar dasu Aljannah.
c. Akwai wanda ni’ima zai ta sha tun daga farko har qarshe a
qabarinsa. Wani ma ko tambaya ba za ayi mas aba. Idan
kuma yaje lahira zai shige totar zuwa Aljannah. Allah Yasa
mu ne.
d. Akwai wani kuma matsa guda kawai za ayi masa na wani
xan lokaci, daga nan shi kenan, babu wata fitina. Kuma a
lahira Aljannah zai shiga.
e. Akwai kuma wanda za ayi masa azaba a Qabarinsa na wani
lokaci don a wanke shi a tsaftace shi daga zunubansa.. Daga
baya sai a xauke wa nnan azabar, a sanyaya masa a musanya
masa da ni’ima.. Irin waxannn ne babban Malami
(Shaykhul -Islam) Ibnu Taymiyyah Rahimahullah yake
cewa: ‚Abindfa yake faruwa a cikin qabari na fitina da shan
matsa da kuma firgici da razani, waxannan suna cikin
ababenda ake kankare laifuka da su98‛
98 Fataawa (juz’i na 7, shafi na 308), bugun Daarul -wafaa’i, Tahqiqi da Takhrijin Aamir
Al-Jazzar da kuma Anwar Al -baaz
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
79
Allah Ya tsare mu daga fitina da kuma azabar qabari, da
kuma azabar wuta. Allah Yasa Aljannah ce makomar mu a
gobe Qiyamah.
Allah Yana karvar addu’ar da mumini yayi w a xan -
uwansa mumini, musamman ma wacce akayi masa a bayan
idonsa (ba tareda ya sani ba).
Malamai suka ce ko wanne Musulmi yana da wasu haqqoqi
akan xan -uwansa Musulmi. Daga cikin waxannan haqqoqin
dai, dol e ne a roqa masa gafara (sawa’un yana raye ne ko
bayan ya mutu).
Akwai ayoyin Qur’ani da ingantattun hadithai da suka
tabbatar da wannan qa’idar da suka ambata . Daga cikinsu
akwai faxin Allah (akan harshen bayinSa na qwarai masu
yiwa magabatansu addu’a):
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
80
[
ﭖ ﭗ ﭘ
ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ
ﭟ
ﭠ
ﭡ ﭢ
ﭣ ﭤ ﭥ
ﭦ ﭧ ﭨ
احلرش: { ]
10
}
‚Ya Ubangijinmu Ka gafarta mana, mu da ‘yan -uwanmu da
suka riga mu da imani (bayinKa na qwarai waxanda suka
shuxe). Kada Ka sanya wani qulli (na qiyayya da gaba) a
cikin zukatanmu gameda waxanda suka yi imani. Ya
Ubangijinmu lallai Kai ne Mai Tausayawa kuma Mai
Jinqai‛
Sannan kuma sanannen abu ne cewa duk wani Musulmin da
ya mutu, toh dole ne sauran ‘yan -wansa Musulmi su yi
masa jana’iza kuma su binne shi. Wannan haqqi ne
tabbatacce a cikin shari’ar Mu sulunci.
Kuma Manzon Allah Ya tabbatar mana cewea matuqar
Musulmi ya sauke wannan hakki, toh fa yana da xumbin
lada wajen Ubangiji .
Yace: ‚Idan har bawa ya halarci Sallar jinaza ta xan -uwansa
Musulmi, toh yana da lada kwatankwacin qiraxi99 guda.
Idan kuma ya tsaya ya raka gawar har aka binne ta, toh yana
da Qiraxi biyu na lada‛
Sannan kuma wannan Sallah da za ayi wa mamaci, tana ma
da amfani gareshi sosai. Saboda tana daga cikin hanyoyin
samun gafara gareshi.
Manzon Allah yana cewa: ‚Babu wani mamaci (cikin
Musulmi) da wani kaso na al’ummar Musulmi za su sallace
shi su kimanin mutum xari, kuma kowanne daga cikinsu
99 Malamai suka ce Kalmar Qiraxi yana nufin: tsauni mai girma, wanda qaraminsa ma ya
kai kamar girman dutsen uhudu (duba Musnad na imam Ahmad, hadisi na 10079 , daga
Sahabi Abu -Huraira ).
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
81
yana neman a b ashi ceton sa, fahce sai an b asu ceton
nashi100‛.
A wata riwaya kuma101, Manzo cewa yayi: ‚Babu wani
mutum musulmi da zai mutu , kuma a samu har mutum
arba’in waxanda basu shirka su tsaya su sallaci gawarsa
fahce sai Allah Ya basu ceton sa (zai gafarta masa
sakamakon wannan addu’ar da sukayi masa, matuqar shi
xin ma ba ya shirka)‛.
Allah Zai yafe masa duk laifukanda yayi masa. Sauran
abinda yake tsakaninsa da mutane kuma, wannan shi dasu.
Sai mu kiyaye sosai gameda haqqin mutane.
Shi yasa ma malamai suka ce yana da kyau mu riqa
rubutawa mu ajiye, saboda wata rana. Amma fa lallai ne
muyi qoqarin biya da kanmu ne. Idan kuma hakan bai samu
ba har lokaci yayi, toh magadanmu za su sani ta hanyar
abinda muka rubuta muka ajiye.
Mu da Allah Yasa muke raye a halin yanzu, ya kamata
mu sani ba fa iyawar mu ba ce. Dole wata rana mu ma za
mu mutu. Kuma na tabbata kowa daga cikinmu yana
buqatar a riqa sanya shi cikin addu’a bayan ya mutu. Toh
yana da kyau mu ma yawaita roqa wa mamatanmu Gafarar
Allah (musamman iyayenmu da sauran makusanta).
Mu gaggauta biya musu basussukan da ake binsu don su
samu sauqi. Tabbas yin hakan yana daga cikin ka yutatawa
garesu a matsayinsu na waxanda suka riga suka rasu.
Idan ma akwai bashin azumi akansu (musammanma na
bakance) mu daure mu rama musu. Idan ma mun samu ikon
zuwa muyi musu aikin Hajji ko Umrah (ko dukka biyun),
toh muyi musu (bayan mu munyi n amu). Waxannan
dukkansu suna cikin kyautatawa garesu. Kuma zasu amfa na
100 Muslim (Hadithi na 947) daga Sayyida Nana A’isha da Anas xan Malik, Allah Ya qara
musu yarda.
101 Muslim (Hadithi na 948) daga Sahabi Abdullahi xan Abbas Allah Ya qara musu Yarda.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
82
da hakan sosai insha’Allah. Mu ma kuma za mu samu lada
insha’Allah.
Babban abinda yafi dacewa dai shi ne; kowa ya dage
yayiwa kansa da kansa. Wannan shi yafi dacewa.
Kar mutum ya tsaya wai y a dogara da abinda magada zasu
yi masa bayan ya mutu. Domin kuwa duk yadda za su tuna
da kai, ba za su tuna ka kamar yadda suke tuna kawunansu
ba. Kuma da ma ba akan komai da komai za su iya maka
wani abu ba (sai cikin wasu ‘yan taqaitattun al’amura ne
kawai). Duk kuma abinda za sum aka xin ma, toh fa wakilci
ne kawai, ba zai kai abinda kai za ka yiwa kanka da kanka
ba. Bahaushe kuma yace zuwa da kai ya fi saqo.
Saboda haka mu dage wajen ganin mun amfana da wannan
damar rayuwa da Allah Ya bamu kafin mu m a ta kuvce
mana. Domin kuwa babu makawa za ta qare.
Allah Ya rufa mana asiri, kuma Yasa mu cika da imani.
Ceton Manzon Allah gaskiya ne. Imani da shi ku ma dole
ne. Babu mai musun hakan sai mara rabo.
Ceton da Allah Yayi izni, kala biyu ne (xaya Ya kevance
ManzonSa Muhammadu shi kaxai, xaya kuma shi da
sauran manyan abyin Allah):
1. An kevance Manzon Allah wajen bashi ceton duk bayi
(mutane da aljanu), don ayi hisabi a baiwa kowa sakamakon
abinda ya aikata a rayuwarsa ta duniya.
-Sannan kuma an kevance shi da ceton ‘yan Aljannah ma. Su
ma zai cece su a gobe qiyamah. Domin kuwa dole sai ya
qwanqwasa qofar Aljannah tukunna kafin a buxe wa bayi su
shiga.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
83
-Haka nan kuma akwai ceton sa ga baffan sa Abu -Talib.
Domin an rage masa raxaxin azabar da ake masa a cikin wuta,
sakamakon irin matsayinsa wajen Manzon Allah . Wannan
dai shi ne iyaka amfanin da zai masa, tunda ya mutu bai
musulunta ba. Allah Yasa mu cika da imani.
2. Sannan akwai ceton da aka bashi amma ba a kevance shi shi
kaxai ba. Hatta Mala’iku da sauran Annabawa da Manzanni
da kuma sauran salihan bayi ma za a basu irin wannan c eto na
biyu; shi ne ceton da za ayi wa masu laifi (wasu za a cece su
daga shiga wuta, wasu kuma sai an shigar da su wuta an fara
musu azaba na wani lokaci sai a bada iznin cetonsu ga masu
ceto daga baya ).
Sannan kuma ceto yana da sharuxa guda biyu ne, waxanda
dole sai sun cika kafin ya tabbata.
a. Dole sai wanda Allah Yayi wa izni ne kaxai zai yi ceto.
b. Kuma dole sai wanda Allah Ya ga dama kaxai za a ceto
daga cikin bayinSa (kuma a lokacinda Ya ga dama).
Ya tabbata cikin littafin Imam At -tirmidhi, Manzon Allah
yana c ewa: ‚Akwai ceto na ga ma’abota kaba’irai (manyan
laifuka) daga cikin Al -ummah ta102‛
Idan fa akace masu aikata kaba’ irai anan; ana nufin masu
aikata sauran kaba’irai ne (banda shirka103a ciki). Dom in shi
kam duk wanda ya mutu bai tuba daga gareshi ba, toh babu
wani ceton da zai amfane shi. Allah yace:
[
ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ
املدثر: { ]
48
}
‚Saboda haka ceton masu ceto ba zai amfane shi ba (saboda
ya mutu bai tuba ba daga kafircinsa ba )‛
102 Tirmidhi ne ya ruwaito shi, daga Sahabi Jabir xan Abdullahi, da kuma Anas xan Malik,
Allah Ya qara musu Yarda su dukansu.
103 Duba Kitabut -Tauhid na Al -Imam Ibnu -khuzaimah (Allah Ya Gafarta masa).
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
84
Don haka dai ceton da Manzao ya ambata a cikin wannan
hadisi, yana nufi cetonsa ga ma’abota kaba’irai ne waxanda
suka mutu basu tuba ba, sannan kuma babu shirka a cikin duk
laifukan nasu. Toh su ne wannan ceto zai shafa Insha’Allah.
Sahabi Auf xan Malik yace wata rana ya ji Manzo yana
cewa: ‚Wani mai tahowa ya taho gareni daga gun Ubangijina,
ya bani zavi tsakanin (ko dai) a shigar da rabin Al -ummah ta
Aljannah ko kuma a bani ceto. Sai na zavi a bani ceton nan.
Kuma shi (ceton) zai kasance ne ga wanda ya mutu (daga
cikin Al’ummah ta) alhalin ba ya haxa Allah da komai a cikin
bauta‛104.
Munyi Imani da ceton Manzon Allah . Kuma muna roqon
Allah Ya arzuqta mu da samun cetonsa a gobe Qiyamah.
Daga cikin Yalwatacciyar Rahamar Allah , akwai wasu
daga cikin bayinSa waxanda Zai Yafe musu a gobe
qiyamah, tareda kuma sun je sun same Shi da t arin zunubai,
amma a cikin laifukan nasu dai babu shirka. Domin kuwa
Allah ba Ya yafewa duk wanda ya mutu bai tuba daga
shirka ba.
A cikin Suratun -Nisa’i ayah ta 48 Allah Yana cewa:
104 Musnad na Imaam Ahmad (Hadithi na 24023), Tirmidhi (Hadithi na 2441), Ibnu Majah
(Hadithi na 4317). Dukkansu daga Sahabi Auf xan Malik .
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
85
[
ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵
﮶
]
‚Lallai Shi fa Allah ba Ya Gafarta wa idan aka y i masa
shirka (kuma har aka mutu aka ba’a tuba ba), amma Yana
yafe wa (idan aka aikata) koma bayan wannan ga wanda Ya
ga dama. Toh duk wanda Ya haxa Allah da wani a yayin
bauta, haqiqa ya qirqiri laifi mai girma‛.
A can gaba kuma (aya ta 116), sai Ya rufe ayar da cewa:
[
ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ
]
{
النساء
:
116
}
‚…Kuma duk wanda ya haxa Allah da wani a yayin bauta,
haqiqa ya vata vata mai nisa‛
Saboda haka ma ya haramta Aljannah kwata -kwata ga
wanda Ya mutu yana shirka. Haka Ya faxa a can cikin
Suratul -Ma’idah (a qar shen ayah ta 72) inda Yake cewa:
[
ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ
]
‚Lallai duk wand a ya haxa Allah da wani a wajen bauta
(kuma har ya mutu bai tuba ba), toh haqiqa Allah Ya
haramta mishi Aljannah, kuma makomarsa it ace wuta,
kuma waxannnan azzalumai (masu shirka) basu da wasu
mataimaka (babu wanda zai taimake su ya kyvutar dasu
daga wannan madawwamiyar azaba)‛
Saboda haka babban sharaxin samun Gafara ta Allah (a
ko da yaushe) shi ne kuvuta daga shirka. Mannzon Allah
yace: Allah Yana cewa: ‚Duk wanda ya same Ni da
zunubai (masu yawa, ko d a kuwa yawan su ya kai) kusan
yawan qassai, amma kuma ya kasance ba ya haxa ni da
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
86
komai wajen bauta, toh Ni kuma Zan zo masa da
kwatankwacin ta na gafara105‛.
Akwai waxanda Allah Zai Yafe musu tun a filin hisabi.
Zai rufa musu asiri Yace su shige kawai, tareda kuma suna
da zunubai masu yawa, amma da Yake babu shirka aciki sai
Yayi musu afuwa.
Su ne waxanda Allah Zai musu hisabi mai sauqi inji
Manzon Allah .
Hadithi ya tabbata kan wannan al’amari a cikin Musnad na
Imamu Ahmad, Hadithi na 6944 , daga Sahabi Abdullahi
xan Amru xan As Allah Ya Qara musu yarda (shi da
mahaifin n ashi dukka).
Akwai kuma waxanda za su shiga wuta sakamakon
zunzurutun zunubansu, kuma duk waxanda aka baiwa izinin
yin ceto sunyi sun gama am ma banda su cikin waxanda za a
ceto xin, sai daga baya Shi kuma Allah Yayi musu afwa
Ya fitar dasu daga wutar, Ya wanke su da wani ruwa mai
suna Ma’ul-Hayati (ruwan rayuwa), sannan Ya shigar da su
Aljannah. Su ne ma talakawan Aljannah, kamar yadda
ingant attun hadithai masu yawa suka tabbatar.
Akwai ma waxanda za a fara ajiye su akan wasu tuddai
dake tsakanin Aljannah da wuta (inda ake kira Tozon
la’arafi a hausance). Za a ajiye su a wajen su zauna na wani
lokaci (suna ganin Aljannah kuma suna ganin wuta, amma
basu shiga kowacce daga ciki ba) har zuwa wani lokacinda
Allah Ya ga dama, sannan daga qarshe su ma Ya shigar
dasu aljannah. Allah Ya bada labarin waxannan bayi
naShi a cikin Suratul -A’araf (wajen ayah ta 46 zuwa 49
haka).
105 Sahih Muslim (Hadithi na 2687) daga Sahabi Abu -Dharrin Al -Ghifaariy
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
87
Ba don komai yasa duk wan nan yake faruwa ba, sai don
kasancewar da ma can Allah ba Ya nufin Ya azabtar da
bayinSa. Ba Ya kuma xora wa bawa sai abinda shi bawan
zai iya xauka.
Babu wanda za a azabtar a lahira fahce shi da kansa ya
tabbatarwa kansa cewa lallai ya cancanci hakan. D omin
kuwa shi ya jawo wa kansa. Saboda haka dole yayi kuka da
kansa, ba da wani ba.
Shi yasa a wani Hadithi Manzon Allah yace: Allah
Yana cewa: ‚Ya ku bayi na! Ku sani duk ayukan nan naku
dai (da kuke aikatawa) ina nan ina kiyaye muku su (babu
abinda z ai salwanta daga ciki). Sannan zan cika wa kowa su
(ta hanyar bashi littafin ayukansa a lahira). Saboda haka duk
wanda ya sami Alkhairi, toh ya godewa Allah (saboda
Shi ne Ya datar dashi da wannan aiki nagari). Wanda kuma
ya samu kishiyar hakan, toh kar ya zargi kowa sai kansa
(saboda shi ya zava wa kansa bin tafarkin shaixan)106‛
Saboda haka duk wanda ya shiga wuta a gobe qiyamah, toh
fa shi ya saya wa kanshi wannan azabah da kuxinsa. Amma
Allah kam, ba Ya nufin wata wahala da bayinSa. Allah
Yace:
[
ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ
البقرة: { ]
185
}
‚Allah Yana nufinku da sauqi, ba Ya nufinku da wahala‛
Saboda haka ne ma Ya sauqaqa mana nau’ukan Ibadah Ya
kuma yawaita mana su, Ya sanya wahala cikin ayukan savo,
Ya yawaita mana hanyoyin samun RahamarSa, Ya buxe
mana qofofi masu yawa na tsira saboda tausayinmu da
Yakeyi.
o Yana ruvanya mana Lada idan muka aikata wani aiki
nagari..
106 Sahih Muslim (Hadithi na 2577 ) daga Sahabi Abu -Dharrin Al -Ghifaariy
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
88
o Yana Gafarta mana zunubanmu107
o A kullum kuma Yana kiranmu zuwa ga neman GafararSa,
don mu rabauta a duniya da l ahira.
A cikin Suratuz -Zumar (daga aya h ta 53 har zuwa ta 55)
Allah Yana cewa:
[
ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳
﮴ ﮵ ﮶ ﮷ ﮸ ﮹ ﮺
]
Allah Yana cewa: ‚(Ya Muhammadu) kace musu (Allah
Yana cewa): Y a ku bayi na waxanda suka yi varna kan
rayukansu (suka zalunci kawunansu ta hanyar aikata
laifuka, sakamakon haka suka tara zunubai masu yawa)!
Toh kada ku yanke qauna daga Rahamar Allah (kada ku
xebe tsammani). Domin kuwa lallai Allah Yana Gafarta
(wa bawa) zunubai gaba xaya. Saboda lallai Shi, Shi ne
kaxai mMai gafara, kuma Mai Jinqai‛
A cikin ayah ta gaba sai Ya cigaba da cewa:
[
﮻ ﮼ ﮽ ﮾ ﮿ ﯀ ﯁ ﯂
]
‚Kuma ku mayar da lamari zuwa ga Ubangijinku, kuma ku
miqa wuya gareShi (kada ku aikata abinda Ya hane ku,
kuma kar ku sava wa umurnin Sa), tun kafin azaba ta zo
muku, sa’annan kuwa ba za a taimake ku ba‛
Sanna kuma sai Yace:
[
ﯓ ﯔ ﯕ
ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ
]
107 Ta hanyar Tuba da Istighfari, ko wani aiki nagari, ko wata hanya ta dab an cikin
waxanda aka ambata a wannan xan littafin (da sauran manyan littattafai na manyan
Malamai, Allah Ya Saka musu da Alkhairi).
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
89
‚Kuma ku bi mafi kyawun abinda aka saukar zuwa gareku
daga Ubangijinku tun gabanin azaba ta zo muku ba tare da
kunyi aune ba, kuma baku sani ba‛
Waxannan ayoyi dai suna nun a mana lallai ne mu gaggauta
tuba daga zunubanmu, mu gyara halayenmu, mu koma ga
Mahaliccinmu, tun kafin wannan dama ta kuvce mana (tun
kafin lokacin karvan tuba ya wuce).
Shi yasa ma Manzon Allah yake cewa: ‚Lallai Allah
Yana shimfixa HannunSa da da re saboda Karvar Tuban
wanda yayi laifi da rana, Yana kuma Shimfixa HannunSa
da rana saboda Karvar Tuban wanda yay laifi da dare, har
zuwa sa’anda rana za ta fito ta mafaxarta108‛
Ya kai/ke mai karatu mai daraja! Inai mana wasiyyah da
tsare dokokin Allah da kuma jin tsoronsa.
Wannan it ace wasiyyar Allah zuwa ga b aki xaya
bayinSa (tun daga kan mutanen farko har zuwa kanmu, ha
ma zuwa na qarshen zuwa duniya) kamar yadda Yake cewa
(cikin Suratun -Nisa’i daga ayah ta 131 zuwa ta 134):
[
ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ
ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ
ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵ ﮶ ﮷ ﮸ ﮹ ﮺ ﮻
]
‚Kuma Allah Shi Yake da Mulkin (baki xaya) abinda ke
cikin sammai da (baki xaya) abinda yake cikin qassai.
Kuma lallai haqiqa Munyi wasici ga waxanda aka baiwa
littafi gabaninku (har ma) da ku (kanku) akan cewa (dole)
ku tsare dokokin Allah (ku ji tsoronSa). Idan kuma kuka
kafirce (kuka kangare kuka qi bin wannan umurni), toh fa
(ku sani) duk abinda yake cikin sammai da qassai baki xaya
108 Sahih Muslim (Hadithi na 2759) daga Sahabi Abu -Musa Al -Ash’ariy
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
90
na Allah ne. Saboda haka Allah Ya kasance Mawadaci
kuma Godajje Ab in godiya (yadda imaninku ya kasance ba
zai qare Shi da komai ba, haka nan rashin imaninku ma ba
zai rage Shi da komai ba).
Ya qara tabbatar da cikar MulkinSa da kuma cikakken
ikonSa akan komai, da kuma cikar wadatarsa, da kuma
buqatuwar baki xaya halittu zuwa gareShi Shi kaxai, inda
Yake cewa (cikin ayah ta gaba):
[
﮼ ﮽ ﮾ ﮿ ﯀ ﯁ ﯂
]
‚Kuma lallai Allah Shi Yake da Mulkin (baki xaya)
abinda ke cikin sammai da (baki xaya) abinda yake cikin
qassai. Saboda haka Allah Ya isa Ya zamto abin dogaro
(Shi kaxai ne Abin nufi da buqata ga baki xaya halittunsa,
Jallah Buwayi Gagara misali).
Saboda haka duk abinda muka aikata, toh fa kanmu mukayi
wa. Shi kam Allah cikakken Mawadaci ne. Idan ma Ya ga
dama cikin qasa da qiftawar ido Zai kawar da mu baki
xaya nmu Ya kawo wasu.
Hakan kuma ba komai ba ne a wajenShi. Domin kuwa Shi
Mai cikakken iko ne akan dukkan komai.
Shi ne a ayah ta gaba sai Allah Ya qara da cewa:
[
ﯓ ﯔ ﯕ
]
‚Idan Ya ga dama Yana iya tafiyar da ku (Ya kawar da ku)
ku dai waxannan mutane, sannan kuma Ya taho da wasu
(mutanen) na daban (Ya maye gurbinku da su). Kuma Allah
Ya kasance Mai (cikakken) iko ne akan hakan‛
KasancewarSa Mai cikakken iko akan komai da komai, Shi
kaxai Yake da ikon baiwa duk wanda Ya ga dama cik in
bayinSa abinda Yake nema na duniya da lahira.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
91
Da ma daga cikin bayi akwai wasu Salihan bayi waxanda
lahira suke so, ko da kuwa sun samu wani abu a duniya, toh
suna amfani da shi wajen neman lahira. Irin waxannan su ne
masu tsira..
Akwai kuma waxanda d uniya kaxai suke so. Ba su da rabo
a lahira, saboda basu yi imani ba.
Toh duk wanda ka nema dai, babu wanda zai baka sai Allah
. Domin kuwa naShi ne Shi kaxai, Bai da abokin tarayya.
Kuma Yana bayarwa ne ga wanda Ya ga dama cikin
bayinSa.
Wannan yake qara tabbatar da tavewar masu dogaro akan
wanin Allah.
Allah Ta’ala Ya tabbatar mana cewa komai da komai naShi
ne, kuma Shi Yake baiwa wanda Yaga dama cikin bayinSa.
Sannan kuma Ya qara tabbatar mana lallai duk wanda yayi
aiki don duniya kaxai, toh fa bai da r abo a lahira. Zai iya
baiwa wanda Ya ga dama wani abu na duniya xin.
Wanda kuma yake neman lahira, toh sh i ma sakamakonsa
na Hannun Shi. Shi yasa a ayah ta gaba sai Yace:
[
ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃ ﰄ ﰅ ﰆ
]
‚Duk wanda ya kasance yana nufin (samun) sakamak on
duniya ne, toh fa a wurin Allah (kaxai) sakamakon
duniya (har ma) da na lahira yake. Kuma Allah Ya
kasance Mai (cikakken) ji, kuma Mai (cikakken) gani (Yana
jin duk abinda kuke faxa, kuma Yana ganin duk abinda
kuke aikatawa, Yana kuma sane da duk ab inda kuke
qudurcewa a zukatanku, saboda haka Zai saka muku da duk
abinda kuka aikata)‛.
Waxannan ayoyi masu daraja suna qunshe da darusa
masu yawa. Kaxan daga cikinsu su ne kamar haka:
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
92
Suna qara tabbatar mana lallai Allah Ya halicce mu ne ba
don komai ba sai don mu kaxaita Shi da bauta. Wannan
bauta kuma dole ne muyi ta Yadda Shi Ya tsara kuma Yayi
umurni, ba yadda muka ga dama ba.
Suna qara tabbatar mana lallai Shi fa Allah ba wai Yana
buqatan wani abu ba ne daga garemu. Imanin masu imani
ba zai qare S hi da komai ba. Haka nan ma duk kafircin
kafir ai ba zai rage Shi da komai ba. Shi cikakken mawadaci
ne, mu ne muke buqatan komai daga gareShi.
Sannan duk kyakkyawan aikinda muka aikata, toh fa
garemu amfanin zai dawo. Haka kuma duk mumunan aikin
da muka ai kata, to akanmu sakamakon zai dawo. Kenan duk
abinda muka shuka a nan duniya, to fa shi za mu girba a
lahira. Saboda haka idan bawa ya samu Alkhairi a can, toh
ya gode wa Allah d omin kuw a Shi Ya datar da shi. Idan
kuma Ya je ya tarar da sharri, toh kar ya z argi kowa sai
kansa (domin kuwa s hi ne haqiqanin s akamakon abinda ya
vata lokacinsa a duniya yana ta aik atawa ).
Saboda haka lallai ne mu zama masu taka -tsan-tsan a
kullum. Mu tsare dokokin Allah, mu dage wajen aikata
ayuka nagari (tun daga farillai har zu wa nafilfilu), mu
nisanci sava wa Allah , mu gaggauta tuba mu koma
gareShi, mu kuma yawaita Istighfari a kullum, saboda fatan
samun Rahamar Allah .
Da fatan Allah Yasa mu dace da aikata abinda Zai Yarda da
mu, Ya qara tabbatar da mu akan Tafarki madaidai ci har
mutuwa, yasa mu cika da imani, Ya kuma sa Aljannah
Firdausi ce makomar mu a gobe qiyamah.
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
93
Haqiqa mai babban rabo a wajen Allah daga cikin
mutane, shi ne wanda zai yi tanadin guzuri tun yana da
sauran dama.
Shi ne wanda zai shirya wa lahira tun k afin mutuwa ta
sauko masa. Yana amfani da damar da Allah Ya bashi
don ganin ya shuka wa kansa Alkhairi kafin ya bar duniya.
Mara rabo a wajen Allah shi ne wanda yake wasa da damar
da Allah ya bashi, shi ne wanda yake shagaltuwa da wasu
al’amura na duniya (ya qi tsayawa ya bautawa Allah har
lokaci Ya qure masa). Sai ya ga azaba ido da ido sannan
yace wai zai tuba, a lokacinda hakan ba zai amfane shi da
komai ba.
Da ma kuma bahaushe yace ba a fafe gora ranar tafiya,
kamar yadda kuma ba a kiwon kare ranar fa rauta.
Sanannen abu ne garemu lallai mafi Alkhairin guzuri shi ne
Tsoron Allah . Da Tsoron Allah ne kaxai bawa zai samu
tsira a ranar tashin qiyama, ranar da dukiya da ‘ya’yan da
mutum ya tara ba za su amfane shi da komai ba.
Saboda haka lallai ne mu ji Tsoron Allah matuqar jin
tsoronSa, mu tsare dokokinSa, mu qara qaimi wajen
yawaita ayukan xa'a, mu nisanci savo. Muyi riqo da
karantarwar Manzon Allah . Mu yawaita Istighfari, mu
Tuba mu koma ga Alla . Shi kuma Allah Ya yi
Alqawarin Zai mana Rahama mat uqar munyi hakan. Shi
kuma Allah ba Ya sava Alqawari.
Idan har mun yarda cewa Alqawarin Allah gaskiya ne,
toh fa lallai ne mu nemi YardarSa ta hanyar bin UmurninSa
da kuma nisantar abinda Ya hanemu. Wannan kuma shi zai
tabbatar da lallai ashe muna kyau tata wa Allah zato.
Manzon Allah yace: ‚Kada xayanku ya mutu fahce (ya
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
94
dage ya y aqi shaixan har ya zamto) yana mai kyautata zato
ga Allah ‛.
Ya faxi wannan magana ana sauran kwana uku kacal ya bar
duniya (kamar yadda Sahabi J abir xan Abdullahi ya faxa ,
Allah Ya q ara Yarda da su baki xaya). Wannan magana
tana daga cikin manyan wasiyoyinda dole ne muyi riqo
dasu sosai don mu samu tsira a duniya da lahira. Domin
kuwa tana cikin maganganun Manzon Allah na qarshe -
qarshe.
Allah Yasa nu dace.
Dukkan Yabo da Godiya marasa misaltuwa sun tabbata ga
Allah Maxaukaki, wanda Ya nuna mana qarshen wannan
xan littafi cikin qoshin lafiya kamar yadda Ya nuna mana
farkonsa.
Muna roqon Allah cikin RahmarSa Ya sanya mu cikin
bayin nan naShi masu gaskiya cikin imaninsu, m asu
kyautata niyyah cikin furucinsu da ayukansu, masu yawan
godiya gareShi gameda ni'imominSa, masu haquri da
dangana gameda duk jarrabawar da ta same su, masu Tuban
gaske zuwa gareShi daga dukkan laifukansu, kuma masu
neman GafararSa daga dukkan zunubai.
Da fatan Allah Mai Jinqai Ya karvi Tuban mu, Ya Gafarta
mana, Ya yafe mana, Yayi mana Jinqai, mu da iyayenmu da
'ya'yanmu da Malamanmu da sauran 'yan -uwanmu Musulmi
baki xaya. Allah Ya Gafarta mana, domin kuwa Shi Mai
yawan Gafara ne kuma Mai Jinqai.
Ya A llah Ka sanya mu cikin yardaddun bayinKa masu
kyautata Ibada. Ka qara tabbatar damu akan Tafarki
HANYOYIN SAMUN GAAFARA
95
Madaidaici har muutuwa, Ka tsare mu daga fitintinu da
kuma azabar qabari, Ka tsare mu daga azabar wuta, Ka sa
Aljannah ce makomar mu a gobe qiy amah.
Ya Allah K ayi daxin Tsira da Aminci ga wannan bawa
naKa kuma ManzonKa Annabi Muhammadu , shi da
Iyalansa da dukkan Sahabbansa, da sauran duk waxanda
suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
Ameeen.
وَالسَّالَمُ عَلَيُْكُْ وَرَْحَْةُاَّللَِّ وَبَرََكَتُهُ
Ana loda PDF...