بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ
Hausa

H - HANYOYIN SAMUN GAFARA [b0de7885]

H - HANYOYIN SAMUN GAFARA [b0de7885] • 1200

H - HANYOYIN SAMUN GAFARA [b0de7885]

H - HANYOYIN SAMUN GAFARA [b0de7885]

1

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

1

Dukkan yabo da godiya da jinjina da kiraari da kuma neman yarda

sun tabbata ga Allah Maxaukaki. Muna jadda da godiyarmu gareShi

a bisa ni’imomin nan naShi marasa qididdiguwa. Kuma muna

neman taimakonS a ako da yaushe (kuma akan komai). Muna ku ma

neman Ga fararSa . Muna kuma nema n tsarinSa daga sharrorin

kawunanmu da kuma miyagun ayukanmu. Muna roqon Shi da Ya

sanya mu cikin bayinSa waxanda Ya shiryar, Ya kuma tabbatar da

mu akan wannan Tafarki na Shiriya har mutuwa (har abada).

Tsira da Amincin A llah su qara tabbata ga ManzonSa

Muhammadu, shi da iyalansa da Sahabbansa, da sauran duk

waxanda suka biyo bayansu da kyautatawa, har zuwa ranar

sakamako. Da fatan Allah Yasa mu ma muna cikinsu .

Bayan haka :

Sanannen abu ne dai kowa daga cikinmu yana aika ta laifi. Mu duka

muna da zunubai, domin kuwa muna sava wa Allah  dare da

rana. Saboda haka kowannen mu y ana da matuqar buqaatar samun

Gafarar Allah Mabuwayi Maxaukaki, don ya samu rabuwa da

waxannan zunubai da yake kannaxe dasu ko ta ina.

Daga cikin Rah amar Allah ga bayinSa, Ya yawaita musu Hanyoyin

Samun GafararSa . Kuma babu wanda zai bi su fahce sai Ubangiji

Mabuwayi Mai Jinqai Ya game shi da GafararSa, kuma sai Ya

lulluve shi da yalwatacciyar RahamarSa wacce ta wadaci komai.

2

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

2

Haqiqa mai lafiyayyen hank ali daga cikin mutane shi ne wanda

yake gaggawar komawa ga Majivincin al’amuran kowa da komai,

ta hanyar riqo da hanyoyin samun Gafararsa (waxanda babu

makawa sai an bi su kaafin a samu biyan buqata).

Ya xan -uwa mai girma! Insha’Allahu Waxannan ‘yan shafu kan

da kake dab da fara karantawa za su qunshi bayani akan wasu daga

cikin Hanyoyin Samun Gafarar Allah (ga duk wanda yabi su kamar yadda

Shari’a tayi bayani). Da faatan Allah  Yasa mu cikinsu.

Allah Yasa mu d ace.

Hanyoyin samun Gafara suna da matuqar yawa sosai. Amma zan

kawo mana guda goma daga cikinsu insha’Allah, daga cikin

waxanda malamai masu yawa sun nun a cewa su ne sukafi

muhimmanci.

Su ne kama r haka:

 Tuba;

 Neman gaafara;

 Shiga Musulunci;

 Nagartaccen Imani;

 Biyayya ga Manzon Allah, da nisantar sava masa;

 Sauran ayuka nagari (irinsu rukunan Musulunci da sauransu) ;

 Haqurin bawa a bisa wata jarrabawar da ta same shi;

 Addu’ar Mumini ga Mumini (m usamman roqa masa gafara);

 Ceton Manzon Allah a gobe Qiyamah;

 Afuwar Allah ga wanda Ya ga dama cikin bayinSa..

Waxanna n dai su ne manyan kashe kashen. A qarqashin wasu

daga cikinsu kuma akwai wasu qananan kashe -kashe, waxanda za

a ga kowanne a wu rinsa Insha’Allahu.

Da farkon f ari zan fara da roqon Ubangiji Maxaukaki Ya arzu kta

ni da ikhlasi Ya kuma d atar dani wajen gabatar da abinda Zai yarda

dashi, Yasa shi a mizanin kyawawan ayuka, kuma Ya G afarta mana

laifukanmu da kurakuranmu (daga mu har iyayenmu da iyalanmu

da malamanmu da duk sauran ‘yan -uwa mu musulmi baki xaya).

3

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

3

Ina roqon Allah Mai Karimci Ya sanya mu baki xayanmu cikin

bayinSa masu tsoronSa, masu tsare dokokinSa, masu lafiyayyen

hankalin nan waxanda suke tuban gaske su koma gareShi..

Allah Yasa mu cikin masu kyautata niyyah a yayin aikata duk

wani a ikin da muka sa a gaba, da kuma baki xaya abinda zamu

furta.

Allah Yasa mu cikin bayinSa waxanda Ya tsare su daga sharrin

shaixan, kuma Ya kuvutar damu daga aikata duk abinda zai jawo

mu afka cikin fushinSa da uqubarSa a duniya da lahira. Lallai Shi

Majiy i ne, kuma Mai amsa roqon bawa.

Xan-uwan ku a Musulunci:

Musa Muhammad Sallau Jada

(

Aboomaryam Aljaadawiy

)

4

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

4

(Hanyoyi Biyu Na Farko)

Kalmar Tuba tana nufin: komawa ga Allah ta hanyar nisant ar

ayukan savo , da kuma neman y afiya daga gareShi.

Ita ma kalmar Istighfa ri tana nufin neman g afarar Allah daga

zunuban da bawa ya aikata . Allah  Ya umurce mu da mu

gaggauta Tuba zuwa gareShi. Kuma Ya yi a lqawrin Zai Yafe

mana zunuban mu matuqar munyi hakan. A cikin Suratut -

Tahrim (ayah ta 8) Allah  Yana cewa :

[

ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟ

ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ ﭬ ﭭ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ

ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ

]

‚Ya ku waxanda sukayi imani! Ku tuba zuwa ga Ubangijinku

tuba irin na gaskiya. Akwai tabbacin cewa Ubangijinku Zai

kankare m uku munana n ayukan ku, kuma Zai shigar da ku

Aljannatai waxanda koramu ke gudana a qarqashi nsu. A wannan

rana Allah ba Ya kunyata Annabi da waxanda sukayi imani dashi.

Haskensu yana gudana ta gabansu da kuma bangarorinsu na

dama, suna cewa Ya Ubangijinmu Ka cika mana haskenmu, kuma

Kayi mana Gafara, domin k uwa lallai Kai ne mai iko a kan dukkan

komai ‛.

Mu gaggaut a tuba, mu yawaita neman gafara. Domin kuwa

‚Duk wani xan Adam mai kuskure ne. kuma mafiya alkhairi

1.‛ daga cikin masu kuskuren nan, su ne masu tuba

Manzon Allah  dai shi yafi kowa yawan Istighfari, tare da

kuma shi yafi kowa matsayi gun Allah , haka kuma shi yafi

kowa tsoron Allah  da kuma tsare dokk inSa.

1 (Ahmad: 13072 ), (Tirmidhi: 2499), (Ibn majah: 4251) Daga Sahabi Anas xan Malik 

5

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

5

Allah  Ya tabbatar masa cewa Ya riga Ya yafe masa duk

wani abinda ya gabata na zunubansa2 (ballentana da m a bai yi

ba), Ya kuma yafe masa abinda zai yi nan gaba ma (tare da

kuma ba zai tava yin laifi ba har abada) amma duk da haka ya

fi kowa neman gafarar Allah . Akullum kuma ya kasance

yana qara zaburar da al’ummarsa wajen d agewa akan haka

sosai da sosai. Ingantattun H adisai masu yawa sun tabbatar da

hakan , cikin manyan littafan Hadisi daban daban . Shi da

kansa ma yake cewa: ‚Wallahi ni (da kaina) ina Neman

Gafarar Allah kuma ina Tuba z uwa gareShi sama da sau 70 a

yini guda3‛

Manzon Allah  yana ma yin Istigh fari sau xari a zama guda,

banda waxanda yakeyi a sauran wurare da lokuta daban -

daban. Sahabbai suka ce a duk inda ya zauna, yana yawaita

faxin:

رَبِّ اغْفِرْ لِي وَتُبْ عَلَيّ، إِنّكَ أَنتَ الت َّوّابُ الرّحِيمُ

‚Ya Ubangiji Kayi min G afara kuma ka karvi tuba na, domin

kuwa Kai ne Mai Yawan karvan tuan nan, Kai ne kuma Mai

JinQai‛

Sahabi Abdullahi xan Umar (Allah qara yarda das u) yace sun

kiyaye Manzon Allah  yana maimaita wannan addu’a har

sau xari a zama guda4.

Manzon Allah  yace ‚Ya ku mutane! ku Tuba zuwa ga

Allah kuma ku nemi Gafarar Sa. domin ni ma (da kaina) ina

5Tuba zuwa gareShi har sau xari a rana

Allah  Ya yi alqawarin Gafarta wa duk wanda ya Tuba ya

koma gareShi. Kum a Zai sanya shi cikin waxanda Yakeso,

domin kuwa Yana son masu Tuba.

2 Duba: Suratul -fat’hi ayah ta biyu (2)

3 Bukhari (hadithi na 6307), daga Sahabi Abu -Hurairah 

4 Duba: Sunan Abi -Dawud (hadithi na 1516) Hadithi ne ingantac ce.

5 Saheeh Muslim (Hadithi na 2702 ). Daga Sahabi Al -Agharru xan Yasaaru 

6

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

6

Ya faxi hakan ne a cikin Suratul -Baqara (ayah ta 222) inda

Yake cewa:

[

ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ

]

]

ابلقرة

:

222[

‚..Lallai allah Yana son masu yawan tuban nan, kuma Yana son

masu (kyautata) tsarki .‛

Saboda irin tsant sar Son da Allah  Yake wa masu Tuba zuwa

gareShi m a, Yana matuqar farin -ciki6 sosai da bawanSa idan

har ya tuba ya koma gareShi, fiye da irin farin -cikin da

xayanmu zai yi idan dabbarsa ta gudu da abincinsa ta bar shi

a tsakiyar daji sannan sai ta dawo gareshi a daidai lokacin da

ya gama xebe tsammanin ci gaba da rayuwa7.

Saboda haka aka umurcemu idan muka gama alwala mu

riqa cewa:

اللَّهُمَّ اجْعَلْنِي مِنَ الت َّوَّابِينَ وَاجْعَلْنِي مِنَ الْمُتَطَهِّرِينَ

‚Ya Allah Ka sanya mu cikin (bayin nan n aka na gari) masu

yawan tuba, Ka kuma sanya mu cikin masu tsarki

8

(waxanda Kace Kana son su)‛

Allah

Yace Ya na son masu tuba su koma gare Shi, kuma

Yana son masu k yautata tsarki. Wannan kaxai ma isa ya

zama dalilin da zai sa mu gaggauta tuba.

Sananne n abu ne Tsarki mafi girma shi ne tsarkak uwa daga

dattin shirka da kafi rci da munafunci, da qazantar zunubai

da dauxar miyagun ayuka.

 Toh tuba zuwa ga Allah da kuma neman gafararSa,

suna daga cikin manya -manyan hanyoyi na samun irin

wannan Tsarki mafi daraja.

6 Farin ciki irin wanda ya da ce da Shi Allah .

7 Bukhari ( 6309 ), Muslim ( 2747 ). Daga Sahabi Anas xan Malik 

8 Tirmidhi (Hadisi na 55) Daga Sayyidina Umar 

7

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

7

Wannan dai a taqaice shi ne bayani akan tagwayen

hanyoyin nan biyu na farko daga cikin Hanyoyin Samun

Gafarar Allah

, wato Tuba Da Kuma Istigfari .

 Da fatan Allah Ya sanya mu cikin bayin nan naShi

waxanda Yakeso, masu kyautata tsarki (na bayyane da

na voye) kuma masu Tuba su koma gareShi Tuba na

gaskiya.

8

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

8

Musulunci sh i ne mafi girman ni’imar da Allah  Yayiwa

bawanSa. Shi ne kaxai tafarkin da bawa zai bi don ya samu

Alkhairan duniya da lahira. Shi ne kaxai Tafarkin ts ira. Shi

ne kaxai yardajjen Addini a wajen Allah . Domin kuwa

Shi Ya bada tabbacin hakan acikin Littaf inSa Mai Tsarki .

Acikin Suratu Ali-‘Imran (ayah ta 19) Allah  Yace :

[

ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ

]

]

آل عمران

:

19[

‚Lallai Musulunci shi ne kaxai (karvavven) Addini a wajen Allah ‛

Acikin dai Suratu Ali-‘Imran xin, Allah  Yace ba Zai

karvi aikin duk wanda ya bauta maSa da wani addini koma

bayan Musulunci ba. Ya faxi hakan ne a cikin ayah ta 85,

inda Yake cewa:

[

ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ

]

‚Kuma duk wanda ya riqi (wani tafarki na daban) koma bayan

Addinin Musulunci, toh fa ba za a karva daga gareshi ba. Kuma

shi xin a (ranar) lahira zai kasance cikin hasararru ‛

Musulunci sharaxi ne babba daga cikin manyan sharuxan

karvan duk wani aikin da bawa zai gabatar a rayuwarsa . Shi

ne kuma hanya mafi girma daga cikin hanyoyin samun

Gafara. Dole kuma sai bawa ya bi wannan hanya (kuma ya

inganta ta) kafin sauran hanyoyin ma su amfane shi.

Daga cikin dalilai mafiya qarfi akan hakan, Allah Ya kira

musulunci da sunan tuba a cikin wasu gwala -gwalan ayoyi

na Al -Qur’ani Mai girma. Ga kaxan daga cikin misalai

gameda hakan insha’Allahu.

9

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

9

A cikin Suratut -Taubah ( ayah ta 5) Allah  Yana cewa:

[

ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ

]

‚Idan har (kafiran nan) suka tuba (suka musulunta) kuma suka

tsaida sallah sannan suka b ada zakkah, toh ku rabu da hanyar su

(ku qyale su, kar ku yaqe su). Domin kuwa A llah Mai g afara ne

mai jinqai ‛

Allah  Ya hana mu yaqa rsu, saboda tuban da sukayi

daga kafircin nasu. Daga tuban nan da sukayi dai, toh

shi kena n sun zama ‘yan -uwan mu na addini.

Shi yasa a wata ayah ta daban kuma9 Yake cewa:

[

ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ

ﮤ ﮥ ﮦ

]

‚Idan har suka tuba (suka bar kafircin n asu) kuma suka tsaida

Sallah sannan suka b ada Zakkah, toh (daga nan) sun zama ‘yan -

uwanku na addini. Kuma Muna rarrabe ayoyin nan ne (dalla -

dalla) ga mutane don su sani ‛..

Acikin Suratul -Furqan ma, Allah  Ya kira Musulunci da da

sunan Tuba , a inda Yayi bayanin halayen bayinSa na qwarai.

Yace su ne waxanda basu shirka ku ma basu kisan kai sannan

kuma basu yin zina.

Sai Yayi bayanin munin laifin duk wanda ya aikata

waxannan miyagun ayuka masu halakarwa a duniya da

lahira, domin kuwa za a ninka azaba ga duk wanda ya aikata

su.

Sannan sa i Yace:

9 At-Taubah (aayah ta 11)

10

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

10

[

ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ

ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ

]

‚..Sai kaxai wanda ya tuba (daga cikinsu) kuma yayi imani

kuma ya aikata aiki na qwarai, toh (irin) waxannan za a sauya

munanan ayukan su zuwa ga kyawawa (za a yafe musu

zunubansu, kuma a maye gu rbinsu da ladan kyawawan ayuka).

Saboda Allah Ya kasance Mai yawan Gafara kuma Mai Jinqai..

kuma duk wanda ya tuba kuma yayi aiki na qwarai, toh lallai

(haqiqa wannan) ya koma ga Allah matuqar komawa ‛.

A Suratul -Anfal (ayah ta 38) Allah  Yana cewa ManzonS a :

[

ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ

ﮱ ﮲ ﮳

]

‚Kace wa waxanda suka kafirta in har sun hanu (sun tuba sun

daina wannan kafircin nasu) toh za a gafarta musu (duk) abinda

ya gabata (na zunubansu). Idan kuma suka koma (suka cigaba da

kafircin nasu bayan sun ce sun tuba), toh haqiqa hanyar

mutanen farko (kafiran da suka gabata a tarihi) ya riga ya shuxe

(za Mu yi musu irin yadda Mukayiwa magabatan su a kafirci) ‛

In har wannan shi n e alqawarin Allah ga kafirai i n har suka tuba

daga kafirci, ashe kenan mu Musulmi m u ne muka fi dacewa

muyi gaggawar komawa gareShi gaba xaya saboda mu rabau ta.

Babu ko shakka Musulunci yana daga cikin manyan hanyoyin

samun Gafara. Domin kuwa yana rusa duk laifin da bawa yayi

kafin musuluntarsa (y ana shafe duk zunubin da bawa ya aikata

acikin kafirci ).

Haka Manzon Allah  Ya faxa wa Sahabin sa Amru xan

‘As , inda yake ce masa:

11

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

11

‚Shin baka san cewa musulunci yana rusa duk wani abinda

10ya kasance k afin shi (na zunubai) ba?

Mun gode wa Allah Ta’ala akan wannan babbar ni’ima ta

Addinin musul unci. Muna f ata Allah Ya raye mu akan ta,

Ya tsare mana imanin mu, Yasa mu cika da imani, yasa mu

cikin bayin nan n aShi masu rabauta a duniya da l ahira.

10 Duba Saheeh muslim (hadithi na: 121)

12

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

12

Imanin gaskiya, shi zai sa bawa ya tsaida ing antaccen

Tauhidi. Shi zai sa bawa ya tsare dokokin Allah . Shi zai

sa bawa ya nisanci savon Allah (sawa’un a bayyane ne ko a

voye). Imani y ana kuma daga cikin manya n hanyoyin

samun Gafarar Allah .

Idan muka duba wasu ayoyin Al -Qur’ani Mai Girma, za mu

ga inda Allah  Yake yabon wasu bayinSa masu gaskiya

cikin imaninsu, ce wa su kam su na ma yin tawassuli da

imanin nasu wajen neman GafararSa (da kuma neman

tsarinSa daga azabar wuta a gobe qiyamah) .

Wannan yake nuna ashe nagartacce n imani ma yana

daga cikin hanyoyin samun g afara, tunda har ana

tawassuli da shi waj en neman tsira a duniya da lahira .

Za mu ga misalign hakan a cikin Suratu Ali-Imran (ayah

ta: 193), inda Allah  Yake cewa (a harshen bayinSa

masu imani):

[

ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥ ﯦ ﯧ

ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ

]

Allah  Yace (su waxannan Muminai suna cewa): ‚Ya

Ubangijinmu! Lallai mu mun ji wani mai kira yana kira

zuwa ga imani, yana cewa kuyi imani da Ubangijinku , mu

kuma sai mukayi imani (kamar yadda ya umurce mu).

Saboda haka (muke roqonKa) Ya Ubangijinmu Ka Gafarta

mana zunubanmu, Ka kankare mana munanan ayukanmu,

kuma Ka karvi rayuka mu tare da mutanen kirki (masu yi

maka xa’a) ‛..

13

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

13

Bayan Allah  Ya faxi wasu daga cikin siffofin su a farkon

Suratul -Anfal (kuma Ya tabbatar musu da cewa Ya yarda da

ingancin imanin nasu kuma Ya karvi ayukansu ) sai Yace:

[

ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ

]

‚Waxannan su ne muminai na gaskiya. Suna da wasu darajoji

(maxaukaka) gun Ubangijinsu, tare da Gafara, da kuma wani

irin (yalwataccen) arziki mai girma (daga Ubangiji Mai Karimci

da Baiwa ga bayinSa nagari) ‛..

Kamar yadda suke aikata duk abinda aka umurcesu na

wajibai (har ma da nafilfilu), haka kuma suke matuqar

nisantar duk wata hanyar da za ta sa su afka cikin miyagun

ayukan nan masu halakarwa.

A kullum s una matuqar nisantan waxannan manyan laifuka

ne saboda Tsoron Allah da suke yi , da kuma fatan samun

RahamarSa .

Allah  Ya yabe su akan hakan, kuma Ya tabbatar musu

cewa wannan xin wata hanya ce ta samun GafararSa.

A cikin Suratun -Najmi (ayah ta 32) Allah  Yace :

[

ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﯡ

]

‚..(Su ne) masu nisantar manyan laifuka (kaba’irai) da

abubuwan alfasha (iri n su zina da kuma miyagun kalamai),

sai dai qananan laifuka (wannan kam zamiya tana kaisu ga

aikatawa). Toh lallai Ubangijinka Mai yalwatacciyar Gafara

ne‛.

wannan gava dai tana qara tabbatar wa masu imani ne cewa

matuqar sun nisanci waxannan manyan laifuk a, matuqar

sun tsare dokokin Allah sun ji tsoronSa, toh Zai gafarta

musu zunubansu.

14

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

14

Ma’ana : Allah  Zai Gafarta musu laifukansu saboda

inganta imaninsu da sukayi, da kyautata alaqarsu daShi

da sukayi ta hanyar aikata abinda Ya umurce su, da

kuma nisantar manyan laifukan nan da Ya hanasu

aikatawa.

Sanannen abu ne cewa Shirka ita ce mafi girma (mafi

muni, kuma mafi haxari) daga cikin waxannan manyan

laifuka11.. Toh duk wanda ya nisanci shirka da sauran

miyagun ayukan nan, kuma ya dage wajen yawaita

ayuka nagari (tsakanin farillai da nafilfilu), Allah 

(cikin FalalarSa da yalwatacciyar RahamarSa) Zai yafe

masa sauran laifukan da ya aikata.

Allah  Ya yi alqawarin hakan a cikin Suratun -Nisa’i

(ayah ta: 31) inda Yake cewa:

[

ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ

ﮜ ﮝ ﮞ

]

‚Idan har kuka nisanci manyan laifukan (nan) da aka hane

ku aikatawa (saboda Tsoron Allah); toh za Mu kan kare

muku munanan ayukanku, kuma za Mu shigar daku (wata

irin babbar) mashiga ta karimci .‛

Sannan kuma Ya yi alqawarin gafarta wa bayin nan

naShi masu tsoron fakewa daga idanun mutane don su

sava maSa, waxanda suka fifita neman YardarSa akan

ta mutane.

11 Duba Saheehul -bukhari (hadithi na 2654 , da 6861 ), Abu -Dawuda da Tirmidhi ma sun

ruwaito shi..

15

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

15

A cikin Suratul -Mulk (aya ta 12) Allah  Yana cewa:

[

ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃ ﰄ ﰅ ﰆ

]

‚Lallai waxanda suke tsoron Ubangijin su a voye (masu tsoron

vuya su sava maSa, saboda yaqinin da suke dashi akan lallai Yana

ganinsu, kuma suna jin kunyarSa); toh suna da wata irin gafara

(mai yawa) da kuma wani irin sakamako mai matuqar girma (daga

wajen Ubangijin n asu Maxaukaki) .‛

Ko shakka babu duk wanda ya doshi aikata wani aikin savo

a voye, sannan sai ya bar wannan aikin saboda ya tuna cewa

ai Allah kam Yana ganinsa, wannan bawan Allah yana da

imani mai qarfin ga ske.

Shi yasa Allah  Yace duk mai irin wannan hali toh Ya yi

masa alqawarin G afara da kuma lada mai yawa.

Allah  Ya ma ce Aljannah ce makomar duk mai irin

wannan halin.

Haka Ya faxa a can wajen qarshen suratun -Nazi’at (ayah ta

40-41) inda Yake cewa:

[

ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ ﯯ ﯰ ﯱ ﯲ ﯳ ﯴ ﯵ ﯶ ﯷ ﯸ

]

‚Amma duk wanda yaji tsoron tsayuwa gaban Ubangijinsa

(a gobe qiyama) sai ya hana kansa aikata abinda ransa

yakeso (na laifi); toh lallai aljannah ita ce makoma (ga irin

waxannan bayin Allah masu imanin gaskiya) ‛

Kuma Ya yi alkaqwarin cewa in har bawa ya tsare

dokokin Sa kuma Yaji tsoron sa a ko wanne hali, toh Zai

datar da shi da daidai a cikin al’amuran sa na addini da

rayuwa, kuma Zai gafarta masa zunuban sa.

16

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

16

Allah  Ya faxi hakan ne a cikin Suratul -Anfal (ayah ta

29) inda Yake cewa:

[

ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ

ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ

]

‚Ya ku waxanda kukayi imani! In har kun tsare dokokin

Allah (kunji tsoron Sa) toh Zai sanya muku mararraba12,

Kuma Zai kankare muku qananan laifukan ku, kuma Zai

Gafarta muku (manyan laifukan ku). Domin kuwa Allah

Ma’abocin falala ne Mai Girma. ‛

Da fatan Allah  Yasa da mu cikin masu tsoronSa a

kowanne hali, kuma Yasa mu gama da duniya l afiya..

12 mai rabewa tsakaninku da abinda kuke tsoron gamuwa da shi a duniya da lahira. Kuma

Zai baku ilimi da basira Wacce za ku gane gaskiya daga vata. Kuma Zai datar da ku da

abinda zai sa Ya yarda da ku a kullum.

17

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

17

(Hanya ta Biyar)

Da kuma nisantar sava masa

Bin Tafarkin Manzon Allah , da yi masa b iyayya a

cikin komai na umurni da hani, da barin sava masa ;

wannan shi ne ma Musuluncin gaba xaya .

Shi ne tafarkin shiriya . Shi ne mafi girma daga cikin

manyan alamomin imanin gaskiya .

Shi ne mafi qarfi daga cikin alamomin da suke nuna

lallai da gaske ba wa yana son Allah da manzonSa .

Shi ne mafi girma daga cikin hanyoyin da bawa zai bi

don Allah  Yaso shi, kuma Ya yarda da shi .

Kuma yana daga cikin manyan hanyoyin samun Gafarar

Allah .

Za mu gane hakan ne idan muka duba cikin Suratu Ali-

Imran (ayah ta 31 da ta 32), inda Allah  Yake cewa:

[

ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ

]

‚Kace (musu): in h ar (da gaske) kun kasance kuna son Allah,

toh ku bi ni. Shi kuma Allah Zai so ku (idan kukayi hakan),

kuma Zai Gafarta muku zunuban ku. Domin kuwa Allah Mai

yawan Gafara ne, kuma Mai Jinqai ‛.

Wannan ayah dai tana nan ne a matsayin mizanin auna

gaskiyar im anin duk wanda yace ya yarda da Allah 

da ManzonSa .

Allah  Ya sanya xa’a ga ManzonSa a matsayin

sharaxin ingancin imanin duk wanda yayi da’awar

imani da Allah da ManzonSa.

18

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

18

Sannan Ya qara tabbatar da hakan a ayah ta gaba inda

Yake cewa:

[

ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ

]

‚Kace: kuyi xa’a (bi yayya) ga Allah kuma kuyi xa’a ga Manzo

(Muhammadu ). Amman suka juya baya (suka qi bin wannan

umurni), toh fa lallai Allah ba Ya son kafirai .‛

Ko shakka babu lallai tsayuwa akan tafarkin Manzon Allah

 da tsare masa haqqoqinsa, da kyautata ladabi gareshi , da

kuma nisantar sava masa: waxannan su ne suke nuna lallai

da gaske bawa ya yi imani da shi. Duk kuma wanda yayi

hakan, Allah  Ya yi alqawarin Zai Gafarta masa, kuma

Zai bashi lada mai girma. Domin kuwa dole sai ya aikata su

kafin ya samu tsira a duniy a da lahira.

Shi yasa a farko -farkon Suratul -Hujur at (ayah ta 3) Allah 

Yake cewa:

[

ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥ ﯦ ﯧ

ﯨ ﯩ ﯪ

]

‚Lallai waxanda suke sassauta muryoyin su a wurin Manzon

Allah  (saboda ladabin da suke masa), waxannan su ne

waxanda Allah  Ya jarrabi zukatansu da taqawa (kuma Ya

datar dasu da cin wannan jarrabawa). Saboda haka suna da wata

irin Gafara, da kuma lada mai girma (a wajen Allah )‛.

Tsira da Amincin Allah su qara tabbata ga wannan Manzo mai

daraja, shi da iyalansa da Sahabbansa baki xaya, da kuma

waxanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar

sakamako. Da fatan Allah Yasa har da mu cikinsu.

19

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

19

(Hanya ta Shida)

Lallai ayuka na gari ma suna shafe munana, idan har bawa

yayi sa’a yana da imani kuma ya nisanci s hirka. Annabi 

yana cewa:

kaji tsoron Allah a duk inda kake. Ka riqa

bibiyan munanan ayukan ka da kyawawa, saboda su goge

munanan. Kuma ka kyautata yadda kake mu’amala da

13mutane

Wannan hadithi kuma shi yake qara fassara wannan magana

ta Allah  inda Yake cewa:

[

ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵

]

:هود{ 114}

‚..Lallai kyawawan ayuka suna tafiyar da munana ..‛

Akwai misalai masu yawa daga cikin ayoyin Al -Qur’ani da kuma

ingantattun hadithai da suke tabbatar da lallai ayuka nagari suna

shafe munana (suna zama sanadiyyar samun gafarar Allah kan

wasu laifukan da bawa ya aikata a baya) ..

A.Kyautata Tsarki da kuma cika Alwala, kamar yadda

Manzon Allah

ya koyar

KYAUTATA TSARKI

Haqiqa kyautata tsarki al’amari ne mai muhimmancin gaske a

cikin addinin Musulunci. Tsarki dai s haraxi ne daga cikin

manyan sharuxan karvar duk wata Ibadar da bawa zai yi a

rayuwarsa. Manzo  yace:

14Tsarki shi ne rabin imani

Shi yasa Allah  Yake son duk wanda yayi qoqari ya

zama mai kyautata tsarkin sa.

13 Tirmidhi ne ya ruwaito shi (hadithi na 1987 ) daga Sahabi Abu -dharrin Al-ghifari 

14 Sahih -Muslim (hadithi na 223) daga Sahabi Abu -Maalik al -Ash’ariy

20

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

20

Har ma Ya yabi wasu bayinSa saboda hakan, inda Yake

cewa:

[

ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ

(التوبة: 801) ]

‚..A cikinsa ( masallacin Quba) akwai wasu mazaje (mutane)

masu son suyi (kyakkyawan) tsarki, Allah kuma Yana son masu

neman tsakakuwan nan15.‛

Shi yasa ma aka umurce mu da neman Gafarar Allah a

yayinda muka gama tsarki muka fi to daga makewaya.

Manzon Allah  ma ya kasance a duk lokacinda ya gama

biyan buqata ya fito, yana cewa:

غُفْرَانَكَ

‚GafararKa nake nema16 (Ya Allah)‛.

Ana neman Gafara yayinda aka fito daga makewaya saboda

wasu dalilai.

Kaxan daga cikinsu dai su ne kamar haka:

 Saboda a haxa duk nau’ukan tsarkin biyu (najasar da aka

kawar daga gangan jiki, da kuma dattin zunuban da ake da

su)..

 Saboda bawa bai sani ba qila a yayin tsarkin nashi akwai

wata najasar da ta fallatso masa a jiki (cikin rashin sani).

Duk da dai Allah  ba Ya kama bawa akan irin wannan

(matuqar dai babu sakaci), amma tare da hakan bawa yake

neman Gafarar Allah  da RahamarSa.

Sannan kuma ya tabbata a sunnah lallai rashin kyautata

tsarki yana cikin manyan laifukan da suke jawowa ayi wa

bawa azaba a cikin qabarinsa17.

15 Suratut -Taubah (ayah ta 108)

16 Tirmidhi( 7), Abu -Dawud( 30), Ibnu -Majah( 300).

Dukkan su daga Uwarmu (Nana) A’ishatu Allah Ya qaara mata Yarda da Daraja.

21

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

21

A wani hadithin ma, Manzon Allah  cewa yayi:

Kuyi

(ta hanyar kiyayewa sosai yayin qoqarin kuvuta daga fitsari

da kuke tsarki

saboda yawancin azabar qabari daga

irin

wannan)

18. fitsari n ne

Saboda haka aka umurci bawa da neman Gafarar Allah

bayan ya fito daga makewaya , saboda ya samu kuvuta daga

wannan azabar.

Ashe tunda kuwa rashin kyautata tsarki yana da irin wannan

muni, toh lallai wajibi ne mu kiyaye sosai. Musamman

kuma ga shi mun gani cewa kyautata tsarkin yana daga

cikin hanyoyin samun babban matsayi a wajen Allah ,

kuma yana ma daga cikin hanyoyin samun gafarar Allah .

Da fatan Allah  Ya tsare mana imaninmu, Ya kuma qara

tabbatar da mu akan karantarwar ManzonSa Annabi

Muhammadu  har mutuwa.

CIKA ALWALA

Yin alwala kamar yadda Manzon Allah  ya koyar , yana

daga cikin muhimman hanyoyin samun Gafarar Allah

Maxaukaki. Kowa kuma zai samu wannan falala ne

gwargwadon koyinsa da Manzon Allah .

Akwai ingantattun hadithai masu yawa da sukayi bayani

akan wannan al’amari. Ga kaxan daga cikinsu insha‘Allahu:

Manzon Allah  yace: ‚ Duk wanda yayi alwala kuma ya

kyautata alwalar, toh laifukan sa za su fice daga jikinsa -hatta

19‛. ma waxanda suke qarqashin faratan sa

Abin nufi: Duk wata gavar da aka wanke a yayin alwala,

toh wannan ruwan alwala zai wanko har da zunuban da aka

17 Bukhari (218), Muslim (212). Daga Sahabi abdullahi xan Abbas Allah Ya qara musu

Yarda

18Ad-daara -qutniy ne ya ruwaito (hadithi na 464) daga Sahabi Abu -huraira 

19Sahih Muslim (Hadithi na 245) daga Sayyiduna Usmanu .

22

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

22

aikata da wannan gava, har bawa ya kasance tsaftatacce

daga zunubai a yayinda ya kamala alwalar20‛

Shi yasa aka kira alwala da sunan tsarki. Saboda bawa yana

tsarkaka daga zunubansa ta hanyar kyautata alwala.

Wata rana21 Manzon Allah  (ya tambayi Sahabbansa) yana

cewa: ‚ Shin b azan nuna muku abubuwanda (ta dalilin

aikata su) Allah

Zai share muku laifukan ku ba, kuma Ya

‛ Sai suka ce lallai muna so ka faxa mana xaga darajojin ku?

ya Manzon Allah. Sai yace: ‚ Cika alwala (kyautata shi) a

daidai lokacinda ake qin tava ruwa22, da kuma yawan tattaki

zuwa wuraren sallah (masallatai), da kuma masu jiran sallah

bayan wata sallar23, Waxannan lallai su masu ribaxi ne.

24‛. Lallai waxannan su ne masu ribaxi

Manzon Allah  ya kamanta waxannan ayuka gu da uku da

wannan babban al’amari na Jihadi, saboda girman aikin

nasu a wajen Allah .

Da fatan Allah  Yasa mu cikinsu.

Wata rana b ayan Sayyiduna Usmanu  ya koya wa mutane irin

alwalar Manzon Allah , sai yace musu: Na ga Manzon Allah 

20 Sahih Muslim (Hadithi na 244) daga Sahabi Abu -Hurairah .

21 Hadithin yana cikin Sahih Muslim (Hadithi na ) daga Sahabi Abu -hurairah 

22 saboda yanayin da ake ciki na tsananin sanyi, yasa kowa yana jin nauyin amfani da ruwa

sosai. Toh su duk da haka suna daurewa suyi alwala mai kyau

23 Misali: Irin zaman nan da akeyi tsakanin Sallar Maghriba da isha’i, ko tsakanin Azahar

da la’asar, ko kuma waxanda suka shigo masallaci sukayi nafila suka zauna suna jiran

lokacinda za a tayar da Iqamar Sallar da take biye, da dai sauran makamantan su..

24 Ribaxi shi ne zaman daqo cikin shiri da kimtsi (shirin ko ta kwana) saboda gabatar da

wani aikin ibada don neman Y ardar Allah. Aiki ne wanda dole s ai an jure kafin a iya yin

shi.

An kira waxannan mutane uku masu ribaxi ne, saboda irin himmar da suke da ita, da kuma

tsantsar jajircewar su akan ibada.

Sannan kuma w axanda aka fi sani da masu ribaxi , su ne waxanda suka z auna suka tare

wushiryar yaqi. Su ne waxanda suka bar komai suka koma suka tare kafar da ake ganin

maqiya za su iya biyowa su farma al’ummah. Su ne Mujahidan nan da suka saida rayukan

su don kare addinin Allah . Da fatan Allah Yasa mu cikinsu.

23

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

23

ya yi irin wannan alwala, sannan sai yace: Duk w anda yayi

alwala kamar haka, za a g afarta masa abinda ya gabata n a

zunuban sa. Sannan tattakin da zaiyi zuwa Masallaci da kuma

Sallar da zai yi a chan, su ma kuma wani irin qarin lada ne

25gareshi

A wani lokacin kuma, shi Sa yyiduna Usmanu xin yake

cewa: ‚Lallai na ji Manzon Allah  yana cewa: Babu wani

mutum Musulmi da zai yi alwala kuma ya kyautata alwalarsa

sannan kuma ya sallaci wata sallar, fahce sai Allah

Ya

Gafarta masa abinda yake tsakanin wannan Sallah da kuma

26‛ Sallar da take biye da ita

B. Sallah (ta farillah da ta N afila)

Sallah ita ce mafi girma daga daga cikin dukkan rukunan

Musulunci bayan Kalmar Shahada. Ita ce ma shaidar cewa

mutum Musulmi ne. Daga cikin miliyoyin falalar ta marasa

qidayuwa, Sallah tana cikin man yan hanyoyin samun

Gafara . Idan har bawa ya kiyaye Sallar farillah, kuma ya

dage da nafilfilu kamar yadda Manzon Allah  ya koyar,

toh Allah  kuma Zai yafe masa zunubansa.

Babban misali akan wannan, shi ne faxin Allah  (acikin

Suratu Hud ayah ta 114) inda Yake cewa:

[

ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵ ﮶ ﮷ ﮸ ﮹

]

‚Kuma ka tsaida Sallah a geffan nan biyu na yini da kuma

wani yank i daga dare. Lallai kyawawan ayuka suna tafiyar da

munana. Wannan fa tunatarwa ce ga masu (rabon) tunawa ‛

Saboda amfanin da waxannan sallolin guda biyar suke da

shi ga bawa wajen tsaftace shi daga zunubai ne fa, yasa har

25 Sahih Mus lim (hadithi na 229) daga Sayyidina Usmanu xan Affan 

26 Sahih Muslim (hadithi na 227) Daga Sayyidina usmanu xan Affan 

24

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

24

ma Manzon Allah  ya kamanta su da wanka sau biyar a

yini.

Wata rana yace da Sahabbansa : ‚Shin baku gani ba; in har

da ace akwai wata korama a qofar (gidan) xayanku, kuma a

kowane yini yakan yi wanka aciki har sau biyar, shin akwai

wani dattin da zai ragu a jikinsa ne? Toh haka ne misalin

sallolin nan biyar. Allah

27 (kamar Yana share laifuka da su

yadda ruwan koramar nan yake wanke dattin jikin bawa) ‛.

Lallai ko shakka babu kiyaye Sallolin nan biyar, da kuma

tattaki saboda halartarsu a cikin jama’a, da kuma zama a

Masallaci saboda jiran S allah; baki xaya waxannan suna

cikin muhimman hanyoyin samun Gafara. 

Ya tabbata cewa idan ma bawa ya tashi ya kama hanyar

zuwa Masallaci, toh gwargwadon takun da yayi da sawun sa

shi ne yawan ladan da zai samu da kuma yawan zunuban da

za a kankare masa. Do min kuwa Manzon Allah  yana

cewa: ‚ Duk wanda yayi tsarki tun daga gidansa, sannan ya

fito zuwa xaya daga cikin xakunan Allah saboda sauke wani

farali daga cikin farillan Allah (Sallah), toh duk takun da

yayi; xaya zai kankare masa laifi ne, xaya takun kuma zai

xaga masa daraja28 ‛.

Ko shakka babu wannan wata falala ce mai yawan gaske da

Allah  Yake wa bawanSa a yayin da ya kama hanyarsa ta

zuwa Masallaci don gabatar da wata Sallah daga cikin

Salloli.

Hakanan kuma duk wanda ya shigo Masallaci ya yi Nafila

sannan ya zauna yana jir an isowar Liman don a tada Sallah

(da kuma wanda ya zauna bayan an idar da Sallah don jiran

lokacin sallah ta gaba ), su ma akwai wata irin falala mai

27 Bukhari( 528), Muslim ( 667) dukkansu daga sahabi Abu -Huraira 

28 Sahih Muslim (hadithi na 666) daga Sahabi Ubayyu xan Ka’ab 

25

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

25

yawa da Allah  Yake musu. Daga ciki dai, Mala’ikun

Rahama za su nema musu gafara.

Manzon Allah  yace: ‚ Malaiku suna addu’a ga xayanku

matuqar yana zaune a inda yayi sallah kuma alwalarsa bata

warware ba. Suna cewa (cikin addu’ar): Y a Allah Ka G afarta

masa, Ya Allah Kayi masa Rahama29‛.

Sallar Juma’a:

Manzon Allah  yace: ‚ Tsakanin Sallolin nan biyar (tsakani n

kowacce sallah da ta gabanta), haka kuma tsakanin kowacce

Juma’a da wata juma’ar; waxannan dukka suna kankare zunuban

da aka aikata tsakankaninsu, matuqar dai an nisanci kaba’irai30‛

A wani hadithin ma, Manzo  cewa yayi : ‚Duk wanda yayi

wankan Juma’a, sa nnan ya taho Masallacin juma’a ya sallaci iya

abinda aka qaddara masa (na nafilfilu kafin zuwan Liman),

sannan ya zauna ya saurara har sai da Liman ya gama huxubar

sa, sannan yayi sallah tare da shi; toh za a Gafarta masa abinda

yake tsakanin wannan juma’a da wata juma’ar, har ma da qarin

wasu kwananki uku31‛

Sallar Dare (Qiyamul -Laili, ko Tahajjudi)

Sallar dare (ko tsayuwar dare), Sallah ce ta nafila mai xumbin

falala. Tana da lada mai yawa sosai. Lokacinta yana farawa ne

tun daga bayan an gama sallar Isha ’i har zuwa lokacin fitowar

Alfijir. Mutum zai iya yinsa aduk lokacinda ya samu dama.

Amma ingantattun hadis ai sun tabbatar cewa yin wannan

Sallah a qarshe -qarshen dare ya fi falala, ga wanda Allah 

Ya baiwa ikon hakan.

29Bukha ri: 445, Muslim: 649, dukkansu daga Sahabi Abi -Huraira 

30 Sahih -Muslim (hadithi na 233) daga Sahabi Abu -Huraira 

31 Sahih -Muslim (hadithi na 857) daga Sahabi Abu -Huraira 

26

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

26

Wannan Sallah tana daga cik in ayuka n Salihan bayin Allah.

Domin kuwa Allah  Ya yabi masu yinta a cikin Al -Qur’ani

mai girma a wurare daban -daban.

A cikin Suratu Ali-Imran (ayah ta 16 da 17) Allah  Yana

cewa:

[

ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ

]

‚Sune waxanda suke cewa: Ya Ubangijinmu haqiqa mu muny i

imani, saboda haka (muna roqonKa) Ka Gafarta mana

zunubanmu, kuma Ka tsare mu daga azabar wuta ‛.

Sannan sai Ya cigaba da zayyana siffofinsu a cikin ayah

ta gaba, inda Yake cewa:

[

ﭝ ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ

]

‚Su (waxannan bayin dai) su ne masu haquri kuma masu

gaskiya (a kullum), su ne masu dagewa da Ibada, su ne

masu ciyar da dukiyoyinsu (saboda neman Yardar Allah),

su ne kuma masu neman Gafarar Allah a lokacinnan da ake

kira ‚As -saharu‛ (wato lokacinda alfijir ya kusa fitowa).. ‛

Hakanan ma acikin Suratuz -Zariyat (ayah ta 17 da ta 18),

Allah  Yace:

[

ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑ ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ

]

‚Sun kasance b asu yin bacci da dare sai xan kaxan.

Sannan a qarshen daren kuma, suna (dagewa da) neman

Gafara ‛.

Akwai ingantattun hadisai masu yawa da suka tabbatar

mana lallai wannan Sallah tana cikin manyan hayoyin

Samun Gafara. Ga kaxan daga cikinsu insha’Allah:

27

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

27

A cikin wani Hadithi mai xan tsawo32 Manzon Allah  yace

wa Sahabinsa Mu’azu xan Jabal : ‚Shin ba zan nuna maka

wasu qofofin alkhairi ba? Azumi garkuwa ce, ita ma sadaka tana

kankare laifuka kamar yadda ruwa y ake kashe wuta, haka ma

sallar mutum a cikin dare take (tana da tasiri sosai wajen

kankare zunuban b awa)‛.

Sai kuma Manzo  ya karanta faxin Allah :

ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ

ﮠ ﮡ

ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ

ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ

ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳

﮶ ﮷ ﮸ ﮹ ﮺ ﮻ ﮼ ﮽ ﮾ ﮿ ﯀ ﯁ ﯂ ﯃ ﯄

‚Gadajen bayansu suna nisantar makwantansu (a cikin dare),

saboda suna can suna ta roqon Ubangijinsu alhalin suna

tsoronSa kuma suna kwaxayin samun RahamarSa, sannan kuma

(daga cikin ayukansu) suna ciyar da abinda Muka arzuqta su.

Babu wani rai da ta sa n irin abin jin daxin da aka tanadar musu a

voye (a lahira), wanda sakamako ne gameda abinda suka

kasance suna aikatawa (a duniya). Shin wanda ya kasance mai

Imani, yana zama daidai da wanda ya kasance fasiqi? Ba za su

tava zama daidai ba. Amma su waxanda sukayi imani kuma

suka yi ayuka na qwarai, toh suna da (gidajen cikin) Aljannar

tsira a matsayin masauki (na har abada) saboda abinda suka suka

kasance suna aikatawa (na kyawawan ayuka a rayuwarsu ta

duniya)33‛

Allah  Ya sanya wannan Sallah cikin manya -manyan

alamomin salihan bayi. Ya kuma tabbatar musu da cewa lallai

duk ibadar da sukeyi, Yana nan Yana adana musu, kuma a

lahira Zai basu kyakkyawan sakamako.

Allah Yasa da mu cikinsu. Ameeen.

32 Cikin Littafin Imam At -Tirmidhi (Hadithi na 2616) daga Sahabi Mu’azu xan Jabal 

33 Suratus -Sajdah (daga aya ta 16 zuwa ta 19)

28

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

28

Ita w annan Sallah fa a kowane dare ma idan akayi ta ana

samun fala la mai yawa, ballentana kuma in har Allah 

Yasa muka iya raya dararen watan Ramadan kam,

falalar tana da matuqar yawa sosai da sosai fiye da

sauran watanni.

Manzon Allah  yace: ‚Duk wanda yayi tsayuwar dare

34 a cikin Ramadan alhalin yana mai Imani kuma ya yi

ne don neman lada a wajen Allah , toh za a Gafarta

masa abinda ya gabata na zunubansa35‛

Haka kuma yace: ‚Duk wanda yayi tsayuwar dare a

cikin daren Lailatul -qadari alhalin yana mai Imani,

kuma yayi ne don neman lada; toh za a gafarta masa

abinda ya gabata na zubanasa36‛

Shi yasa lokacinda Ma tarsa mai daraja (kuma uwar

muminai) Nana A’isha37 ta tambaye shi addu’ar da za ta

yi idan har Allah  Ya datar da ita da daren Lailatul -

qadri, sai yace mata ‚Ki riqa cewa:

اللَّهُمَّ إِنَّكَ عَفُوٌّ تُحِبُّ الْعَفْوَ فَاعْفُ عَنِّي

‚Ya Allah Lallai (Ka kasance) Kai Mai yafiya ne, kuma

Kana son yafiya, saboda haka Ka y afe min ‛

Manzon Allah  ya faxa mata hakan ne, saboda babu

abinda bawa yafi buqata sama da Afuwar Allah da

GafararSa da RahamarSa. Wannan kuma shi yafi komai

qima cikin buqatun bawa.

34 Ana kiran ta Sallar Tarawih ko asham, ko Tahajjud, ko Qiyamul -laili, ko wutri, da dai

sauran su.

35 Bukhari 37, Muslim 759, dukkan su daga Sahabi Abu -Huraira 

36 Bukhari (35, 1901), Muslim (760), dukkan su da ga Sahabi Abu -Huraira 

37 Allah Ya qaara mata Yarda

29

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

29

Toh a matsayinta na wacce yafi so kuma yafi qauna

daga cikin matan duniya baki xaya, sai ya faxa mata

addu’ar da tafi dacewa ace ta yi a irin wannan lokacin.

Saboda idan har Allah  Ya yiwa bawa Afuwa, toh Ya

gama bashi Alkhairan duniya da lahira baki xaya.

Wannan dai kaxan ne daga cikin irin xumbin falalar da

ake samu idan har aka tsaida Sallah kuma aka dage da

nafilfilun da suka tabbata a Sunnah.

Sai mu kyautata niyyah kuma mu da ge sosai da sosai

wajen ganin mun kyautata ibada a cikin xan lokacinda

ya rage mana a rayuwa. Da fatan Allah Yasa mu dace da

aikata abinda zai sama sanadiyyar samun RahamarSa

garemu.

C. Zakkah, da sadaka, da sauran hanyoyin taimako ga

mabuqata

Daga cikin manya -manyan hanyoyin samun Gafarar

Allah , akwai fitar da Zakkah, bayar da Sadaka, da

sauran hanyoyin taimakon mabuqata, da kuma samar da

‘yanci ga duk wanda yake cikin wani qangi38.

Zakkah:

Zakkah tana tsarkake dukiya. Kuma tana daga cikin

alamomin qarfin imanin bawa. Sannan kuma hanya ce

ta tsarkake bawa daga zunubai, saboda zai samu Gafarar

Allah  idan ya fitar da ita kamar yadda aka umurce shi

a shari’ance.

38 Bauta, ko gidan yaari, ko kuma wani dabaibayi na quncin rayuwa (musamman waxanda

aka zalunta)

30

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

30

A cikin Suratut -Taubah (ayah ta 103-104) Allah  Yace :

[

ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ

ﮪ ﮫ ﮬ

]

‚Ka karvi sadaka (zakka) daga cikin du kiyoyinsu don ka

tsaftace su kuma ka tsarkake su da yin hakan, sannan kuma kayi

musu addu’a (a yayinda suka fidda wannan zakkar), lallai

addu’arka za ta zamto dalilin samun kwanciyar hankali garesu (a

duniya da lahira), Shi kuma Allah  Shi ne Mai jin koma i (daga

cikin akwai roqon bawa), Shi ne kuma Mai cikakkiyar masaniya

akan komai (Ya san buqatar kowa, kuma Ya san abinda ya dace

da kowa cikin bayinSa) ‛.

Sannan sai Ya cigaba da cewa:

[

ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵ ﮶ ﮷ ﮸ ﮹ ﮺ ﮻ ﮼ ﮽

]

‚Shin basu sani bane, cewa lalla i Allah Shi ne (kaxai) Mai

karvan tuban bayinSa, kuma Shi ne (kaxai) Mai karvan

(ayukan da sukayi na bayarda) sadakoki (ga mabuqata),

kuma lallai Allah  Shi ne (kaxai) Mai karvar tuba (daga

bayinSa), Shi ne kuma Mai Jinqai? ‛

Sadaka:

Ita ma sadaka xaya ce daga cikin dalilai masu qarfi da suke

nuna lallai bawa yana da gaskiya cikin imaninsa. Tana

kuma yaye wa bawa fushin Ubangiji , Saboda tana xaya

daga cikin hanyoyin samun GafararSa.

Shi yasa Manzon Allah  yace: ‚ Ita ma sadaka tana

kashe zunubai (tana ka nkare su) kamar yadda ruwa yake

kashe wuta39‛

39 Tirmidhi (hadithi na 2616) daga Sahabi Mu’azu xan Jabal 

31

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

31

Samar da ‘Yanci ga Bayin Allah, da kuma Qwatar Musu

HakkinSu daga Hannun Azzalumai:

Duk wanda ya kyautata niyyah wajen ‘yanta wani Musulmi

daga qangi na bauta (ko kuma ya ceto shi daga wani qunci

na rayuwa); to h shi ma hakan zai zame masa sanadiyyar

samun Gafarar Allah . Domin kuwa Manzon Allah 

yana cewa: ‚ Duk wani mutumin da ya ‘yanta wani mutum

Musulmi, toh shi ma Allah  Zai ‘yanta kowacce gava ta

jikinshi daga wuta, da kwatankwacin irin wannan gava ta jikin

wanda ya ‘yanta xin40‛

Duk da dai a wannan zamani n amu ba bu irin waxannan

bayin, amma wannan falalar dai tana nan. Domin kuwa

yanzu haka a tsakankaninmu akwai waxanda suke cikin

wani irin qangi irin na masu bautan.

Wasu daga cikin mutanenmu (saboda rashin galihu) yanzu

haka suna garqame a cikin gidajen yari alha lin kuma babu

laifin da sukayi.

Wasu kuma (saboda rashin mai tsaya musu) an nuna musu

fin qarfi an qwace musu gida ko gona ko fili, da dai sauran

nau’uka na cin zali iri -iri kamar yadda muke gani cikin gida

da waje..

Toh idan har Allah  Ya baiwa mutum damar qwato wa

irin waxannan raunana haqqinsu daga hannun azzalumai,

insha’Allahu zai samu irin wannan sakamakon da aka

ambata acikin wannan hadithi mai daraja (matuqar dai ya

kyautata niyyah).

Allah Ya tsare mu daga zalunci da kuma sharri n azzalamai,

Ya rufa mana asiri, kuma Yasa mu dace.

40 Bukhari:2517, Muslim:1509, Abu -Dawud:2964, Tir midhi:1547, Dukkansu daga Sahabi

Abu-Huraira 

32

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

32

Lallai ne muyi amfani da duk wani abinda muka m allaka

(na mulki da dukiya da ilimi da sauransu) wajen neman

Yardar Allah  da kuma GafararSa da RahamarSa . Kada

mu bari shaixan ya kai mu ya baro da ruxe -ruxen nan nashi

marasa kan gado . Allah  Shi ne mai Alqawarin Gaskiya,

domin kuwa shi ne Ubangijin Gaskiya. Ya yi mana

Alqawarin cewa matuqar mun bi umurninSa mun tsaya kan

karantarwar AddininSa, kuma muka yi amfani da

dukiyoyinmu kamar yadda Ya umurce mu; t oh Zai Gafarta

mana zunubanmu, kuma Zai bamu babban rabo a duniya da

lahira . Acikin Suratul -Baqarah (ayah ta 268) Allah 

Yana cewa:

[

ﯔ ﯕ ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ

ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ

]

‚Shaixan yana (ruxar ku kuma yana tsorata ku ta hanyar) yi

muku alqawari da talauci (i n har kuka ciyar da dukiyoyin ku

akan neman yardar Allah), kuma yana umurtan ku da

alfasha (wato yana so kuyi amfani da dukiyoyinku akan

savon Allah). Shi kuma Allah Yana muku alqawarin Gafara

daga gareShi da kuma wata irin babbar falala (in har kuka yi

miShi biyayya kuma kuka sava wa shaixan), domin kuwa

Allah Mawadaci ne kuma Masani ‛..

Allah Ya bamu arziki mai Albarka, wanda zai zama

sanadiyyar samun babban rabo garemu a duniya da lahira.

D. Azumi (na farillah da na nafilah)

Azumi wani irin sirri ne tsak anin bawa da Ubangijinsa.

Wata Ibada ce wacce babu wanda yasan yawan ladan ta

sai Allah .

33

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

33

Azumi Yana daga cikin manyan hanyoyin shiga Gidan

Rahama . Akwai qofa ma ta musamman a Aljannah da

aka tanadar da ita don masu azumi kaxai. Idan suka

shige za a kulle qofar, babu mai qara biyowa ta nan

kuma har abada.

Sannan kuma Azumi yana daga cikin manya -manya n

hanyoyin samun Gafarar Allah . Shi yasa ma aka

sanya shi acikin jerin galibin nau’ukan kaffarah da aka

xora wa bawa idan ya aikata wasu manyan laifuka.

Kaxan daga cikinsu su ne kamar haka:

 Wanda yayi kisan kai a bisa kuskure, akwai diyyah

akansa, da kuma azumin wata biyu (kwana sittin kenan).

 Wanda yayi rantsuwa akan abu, sannan sai daga baya

ya karya wannan rantsuwar, cikin nau’ukan kaffararsa

akwai azumi u ku.

 Wanda yayi zihari (wato ya kamanta saduwa da matarsa

ta sunnah da kwanciya da mahaifiyarsa), sannan daga baya

ya koma ga matar; toh dole sai ya yi kaffarah kafin ta

halatta gareshi. Daga cikin jerin nau’ukan kaffarar kuma,

akwai azumi sittin.

 Wanda ya sadu da iyalinsa da rana alhalin kuma da

azumin Ramadan a bakinsa, shi ma dole sai ya yi kaffarah.

Daga cikin jerin nau’ukan kaffarar kuma akwai azumin

wata biyu.

 Wanda yayi wani laifi a cikin aikin hajji, irin laifin da aka

xora masa hukuncin nan da ake k ira fidiya, toh (matuqar ba

mazaunin garin Makka ba ne shi) dole sai ya yi wannan

kaffarah. Daga cikin nau’ukan kaffarar kuma akwai azumi

goma (uku a harami, bakwai kuma idan ya koma gida).

..Da dai sauran su..

34

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

34

An saka azumi a cikin waxannan nau’ukan k affarah ne,

saboda irin muhimmancin da azumin yake da s hi wajen

kankare zunuban mutum. Da fatan Allah  Yasa mu cikin

bayinSa masu himma wajen azumi (na farilla da nafila),

kuma Ya gafarta mana zunubanmu, Yayi mana Afuwa, Ya

kuma Yi mana Rahama.

Azumin Ra madan:

Manzon Allah  yana cewa: ‚ Duk wanda ya azumci

Ramadan alhalin yana mai imani, kuma yayi hakan ne don

neman lada a wajen Allah ; toh za a Gafarta masa abinda

ya gabata na zunubansa41‛

Azumin Nafila:

Kamar yadda azumin Farillah yake da falala mai yaw a, haka

ma azumin nafila yake. Domin kuwa Manzon  ya

kwaxaitar sosai akan yin azumin nafila , saboda xumbin

falalar da haka n yake da ita.

Tabbas a zumi yana da lada mai yawa sosai, kuma yana daga

cikin manyan hanyoyin samun Gafarar Allah .

Daga cikinsu ak wai azumin ranar Arafah ( 9 ga watan

zulhajji, ranar jajiberen babbar sallah), da kuma ranar

Ashura (wato 10 ga watan Al -Muharram)..

Sahabi Abu Qat adah  yana cewa: ‚Wata rana an tambayi

Manzon Allah  gameda falalar a zumtar ranar Arafah, sai

yace: Tana k ankare zunuban shekaru biyu, wacce ta gabata

da kuma wacce take biye . Sannan da aka tambayeshi

gameda falalar azumtar ranar ashura’ kuma, sai yace: Tana

kankare zunuban shekara guda, wacce ta gabata42‛

E. Aikin Hajji da Umrah:

41 Bukhari (38, 1901), Muslim (760) Daga Sahabi Abu -huraira 

42 Sahih Muslim (Hadithi na 1162)

35

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

35

Aikin Hajji da Umrah ma suna daga cikin manyan hanyoyin

samun Gafara. A cikin Suratul -Baqarah bayan Allah  Ya yi

bayanin wasu dokoki na aikin Hajji, sai Yace43:

[

ﮐ ﮑ ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ

]

‚Sannan sai ku kwararo ta inda sauran mutane suka

kwararo (ku gangaro tare da sauran mutane daga

farfajiyar Arafah zuwa Muzdalifa, can bayan faxuwar

rana), kuma ku nemi Gafarar Allah , Saboda lallai Shi

Allah  Mai yawan Gafara ne, kuma Shi Mai yawan

Jinqai ne ‛

Manzon Allah  kuma yace: ‚ duk wanda yayi aikin

hajji alhalin bai yi wani rafathu44 ba, kuma bai yi wani

aiki na fasiqanci ba (a yayin wannan aikin hajji nashi)

har ya gama; toh zai dawo (gida) kamar ranar da

mahaifiyarshi ta haife shi45‛

Abin nufi: Allah  Zai yafe masa baki xaya laifuk an sa,

har ya zama kamar bai tava aikata wani laifi ba a

rayuwarsa.

A cikin wani hadisin kuma, Manzo  yace: ‚ Daga wata

Umrah zuwa wata Umrar (ta daban), ana kankare zunuban da

aka aikata tsakaninsu. Shi kuma Hajji karvavve, bai da wani

sakamako sai Aljannah46‛

Allahu Akbar

43 Acikin ayah ta 199

44 Saduwa da iyali, da duk abinda ya danganci hakan

45 Bukhari:1521, Muslim:1350, daga Sahabi Ab u-Huraira 

46 Bukhari:1773, Muslim:1349

36

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

36

F. Karantar da mutane addinin Allah, da sanar da su hanyoyin

alheri

Daga cikin hanyoyin samun Yardar Allah da Ga fararSa da

RahmarSa; akwai karantar da mutane Addini, da sanar da su

hanyoyin Alkhairi, da umurtansu da kyawawan aiyuka, da

kuma hana su munana, da qyamatar da su aikata dukkan

wani aiki na savo, da kuma nuna musu Girman Allah don su

ji tsoronSa kuma su ts are dokokinSa..

A cikin Suratut -Taubah (ayah ta 112) Allah  Ya lissafa

masu irin wannan aiki daga cikin bayinSa na qwarai masu

babban rabo a duniya da lahira, waxanda Yayi musu bishara

saboda Yarda da Yayi da imaninsu. Yace:

[

ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ

ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ

]

‚Su ne masu Tuba, masu kyautata bautarsu, masu yawan

godiya, masu yin tafiye -tafiye don ayukan xa’a (irinsu aikin

hajji, jigadi, ziyara, duba mara lafiya da dai sauransu), su ne

masu umurni da kyawawan ayuka kuma suke hana munana,

su ne masu t sare dokokin Allah. Saboda haka kayi Albishir

ga (irin waxannan bayi) masu imani (an karvi ayukansu

kuma an yafe musu zunubansu) ‛.

Manzo  yace: ‚ Lallai shi Malami47, duk waxanda suke

cikin sammai da qassai suna nema masa Gafarar Allah,

hatta kifaye acikin ruwa (su da sauran halittun ruwa baki

xayansu suna nema masa Gafara wajen Allah )48‛

47 Mai karantar da al’ummah da ikhlasi, kuma ya tsaya kan karantarwar Manzon Allah 

48 Abu-Dawud (hadithi na 3641), Tirmidhi (hadithi na 2682) daga Sahabi Abud -Dardaa’i

. Hadisin ya inganta. Duba Saheeh_Sunan_Abi -Daw ud hadithi na 3096

37

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

37

Duk halittun nan da suke cikin sammai da qassai suna nema

wa malami Gafara dare da rana, ta hanyoyin da babu wanda

yasan ma adadinsu sai Allah .

Bayan haka kuma, shi ma yana ta tara lada mai yawan gaske

(saboda yana da ladan duk wani harafi guda xaya da ya

koya wa mutane, sannan kuma duk lokacinda akayi aiki da

wannan ilimin da ya koyar -ko da kuwa bayan nutuwarsa

ne- sai shi ma an bashi kwatankwacin irin ladan da aka

baiwa masu aikin, ba tare da kuma an tauyewa kowa komai

ba).

Ko shakka babu wannan falala ce babba sosai. Babu wanda

ya cancance ta sai Malamai magada Annabawa.

Allah Ya saka wa Malamanmu (na da da na yanzu dukka)

da Alkhairi, Ya Gafarta musu zunubansu, Ya kankare musu

kurakuransu, Ya qara wa iliminsu Albarka, Ya qara kare

mana su daga duk wani sharri, da irin kariyar da Yake wa

manyan bayinSa (a duniya da lahira).

Ya mai karatu! Lallai dole ne mu tashi mu nemi ilimin

addinin Allah , don sanin yadda zamu ba uta maSa kamar

yadda Yai umurni. Dole mu tashi muyi karatu, don mu

kawar wa kawunanmu jahilci, mu kuma kawar wa sauran

Al-ummar da muke rayuwa tare (ta hanyar karantar dasu

addinin gaskiya).

Laifi ne babba a zauna kara zube ba a karatun addini.

Hakan yana da mummunan haxari garemu cikin

addininmu da rayuwarmu baki xaya. Domin kuwa idan

jahilci ya kanannaxe al -ummah, toh babu irin tavarazar

da ba za a gani ba.

Zama cikin jahilci zai sa a koma ana rayuwa irin ta

dabbobi, domin kuwa babu irin varnar da ba za a fito fili

ana aikatawa ba.

38

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

38

Babu kuma wata al’ummar da ta cigaba cikin jahilci.

Kuma baki xaya Annabawa da Manzanni da Salihan

bayi dukkansu sun nemi tsari daga jahilci.

Sannan su ma waxanda Allah  Ya zave su Ya sanar

dasu wani abu na ilimi, toh fa waj ibi ne akansu suyi aiki

da shi. Domin kuwa duk wanda ya sani kuma ya take,

toh laifinsa babba ne a wurin Allah . Bal ma azabarsa

daban ce acikin wuta. Saboda tsananin azabar da za ayi

masa ma, har wasu daga cikin ‘yan wutan za su taru

suna kallon yadda ak e masa (tare da su ma xin suna

cikin wutar).

Haka Manzon Allah  yace. Hdi sin yana nan cikin

Sahihul -Bukhari49 inda yake cewa: ‚Za a taho da wani

mutum a jefar da shi cikin wuta. Za a xaure shi (da

hanjinsa) kamar yadda ake xaure jaki a jikin tirkensa (da

igiya). Har sauran ‘yan wuta su kewaye shi (suna kallon

irin azabar da ake masa), su riqa ce masa ya kai malam

wane, ba kai ne (a duniya) ka kasance kana umurni da

kyawawan ayuka kuma kana hani da munana ba? Sai

yace musu:

إِنِّي كُنْتُ آمُرُ بِالْمَعْرُوفِ وَالَ أَف ْعَلُوُ، وَأَن ْهَى عَنِ المُنْكَرِ وَأَف ْعَلُوُ

Zai ce (can a bakinsa): ‚Lallai (hakane) ni na kasance ina

umurni da kyawawan ayuka amma ni ba na aikatawa. Ina

kuma hani da munana amma ni ina aikatawa (a voye) ‛.

Wasu hadithai ma sun tabbatar cew a da irin waxannan

shaixanun malamai za a fara hura wutar jahanna a gobe

Qiyamah.

49 Hdithn Sahabi Usaamah xan Zaid Allah Ya qara musu Yarda (shi da mahaifin nashi

dukka). Yana ma cikin Sahih Muslim

39

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

39

Shi yasa ma wani mawaqi (acikin wasu baitocinsa) yake

cewa:

وَعالِمٌ بِعِلْمِوِ ال ي َعْمَلَنْ # مُعَذَّبٌ ق َبْلَ عُبَّادِ الْوَثَنِ

‚Kuma duk Malamaninda baya aiki da i liminsa, toh

lallai shi za a fara yiwa azaba (a wuta) kafin ma ayiwa

masu bautan gumaka.‛

Haka nan rowar ilimi ma babban laifi ne sosai. Saboda

Manzon Allah  yana cewa: ‚ Duk wanda aka tambaye

shi wani ilimi sai ya voye shi (ya qi ya sanar da

mutane), toh za a sanya masa linzamin wuta a ranar

Qiyamah50‛

Su fa masu umurni da kyawawan ayuka kuma suke hana

munana, a kullum cikin nasara suke a rayuwarsu (ta

duniya da lahira). Domin kuwa bayan xumbin ladan da

suke samu ta fiskoki daban daban, da kuma zunubansu

da ake ta kankare musu a kullum, har ila yau kuma su

(da waxanda suka amsa kiransu) ne kaxai suke tsira a

duk lokacinda wata uquba ta sauka ga kangararrun bayi.

Allah  Yana tserar da su ne saboda wannan babban

aikin da suka tsaya sukayi ta yi na gadon Annabta.

Allah  Ya bamu labarin yadda Yayi ta tserar da

Annabawa da Manzanni masu yawa a cikin Al -Qur’ani

mai girma, su da waxanda sukayi imani dasu cikin

al’ummomin su . Haka kuma Ya ma bamu labarin yadda

Ya tserar da wasu Malamai masu faxakar da al’umma,

su da waxanda suka amsa kiran su.

50 Abu-Dawud (3658), Tirmidhi (2649). Hadithi ne ingantacce, duba Sahih_sunan_Abi -

Dawud (3106)

40

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

40

Misali a cikin suratul -A’rafi (ayah ta 164 zuwa ta 166)

Allah  Yana cewa:

[

ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ

ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ

]

‚Kuma a lokaci nda wasu mutane (marasa gaskiya)

daga cikinsu suka ce (wa masu wa’azi): wai shin me

yasa kuke ta yin wa’azi ga mutanenda tabbas Allah

Zai halaka su, ko kuma Yayi musu azaba mai

tsanani? Sai (su masu wa’azin) suka ce: muna hakan

ne domin neman hanzari zuwa ga Ubangijinku

(saboda kar Ya kama mu da laifin rashin wa’azi ga

mavarnata), da kuma tsammanin (wasu daga cikinsu)

za su (wa’aztu) suyi taqawa (su daina ayukan savon

da sukeyi) ‛.

Wannan akullum itace gwagwarmayar da take tsakanin

Malamai nagari (masu nema n Yardar Allah) da kuma

miyagun malamai (waziran shaixan daga cikin mutane).

Acikin ayah ta gaba kuma sai Allah  Yace:

[

ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ ﭬ ﭭ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ

ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ

]

‚Toh a lokacinda suka manta da abinda aka tunatar da

su (suka qi aiki da shi), Mun tserar da wax anda suke

hani da munanan ayuka, kuma Muka k ama waxanda

sukayi zalunci da azaba mai matuqar tsanani, domin

abinda suka kasance sunayi na fasiqanci ‛.

41

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

41

Sannan a gaba kuma sai Yace:

[

ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ

]

‚Sa’nnan a lokacinda suka yi girman kai suka q i barin

abinda aka hanesu aikatawa, sai muka ce musu Ku kasance

birrai qasqantattu (Muka mayar da su birai, sukayi ta

rayuwa cikin qasqanci da wulakanci) ‛.

Wannan yake tabbatar da cewa lallai babu mai tsira a

duniya da lahira sai wanda ya tsaya kan Tafarki n

Manzon Allah . Idan aka duba ayah ta 52 cikin

Suratun -Nur, Allah  Yana cewa:

[

ﯹ ﯺ ﯻ ﯼ ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃ

]

‚Kuma duk wanda yayi xa’a ga Allah da ManzonSa,

kuma ya ji tsoron Allah kuma ya tsare dokokinSa, to

waxannan su ne masu babban rabo ‛

Toh malami mai gaskiya cikin i maninsa shi ne wanda zai

kyautata niyyah tsakaninsa da Allah, kuma yake bin tafarkin

Manzon Allah  wajen isar da saqon Allah ga bayinSa.

Rashin bin wannan tafarki yana da haxari sosai.

Domin kuwa Manzon Allah  yana cewa: ‚ Na rantse da

wanda rayuwa ta ta ke HannunSa! Dole (ku tashi) kuyi

umurni da kyakkyawan aiki, kuma dole kuyi hani da

mummuna. In ba haka ba kuma, toh za a kai wani

yanayinda Allah  (Zai yi fushi) Ya saukar muku da uquba

daga gareShi, kuma (a irin lokacin nan) ko kun roqe Shi

(don Ya yaye muku) ma, ba Zai amsa muku roqon naku

ba51 (saboda baku cika sharaxin karvar addu’ah ba) ‛.

51 Tirmidhi (hadithi na 2169 ) daga Sahabi Huzaifah al -Yamaani 

42

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

42

G. Biyyaya ga iyaye, kyautata musu, da kuma barin

sava musu ko cutar da su

Daga cikin manyan hanyoyin samun gafarar Allah ;

akwai kyautata wa iyaye, da kuma nisant ar sava musu.

Domin kuwa Yardar Allah tana cikin yardar iyaye, haka

ma FushinSa yana cikin fushinsu52.

Bayan haqqin Allah  da na Manzo  babu haqqin da

yakai na iyaye. Shi yasa acikin ayoyi masu yawa ma ake

yawaita kawo batun kyautatwa iyaye da zarar an ga ma

umurni da kaxaita Allah da bauta.

Saboda haka duk mai son gamawa da duniya lafiya; toh fa

dole ne ya sasanta da iyayen shi ya zauna lafiya da su, kuma

ya riqa kyautata musu. Sannan kuma dole ne ya guji sava

musu akan duk abinda ba savon Allah ba ne. Kar kuma ya

yarda ya cutar da su ko ta wane hali ne. Sava wa iyaye laifi

ne mai matuqar girma. Kuma tun daga nan duniya bawa zai

fara xanxana uquba kafin yaje lahira ya tarar da sakamakon

mummunan aikinsa.

Lallai ne duk wani xa nagari yayi qoqarin ganin ya

nemi Aljannah ta hanyar kyautata wa iyayensa.

Manzon Allah  yana cewa: ‚ Allah Ya turbuxe hancin

duk wanda ya riski tsufan mahaifansa –sawa’un xaya

daga cikinsu ne ko su biyun dukka - kuma (har suka

mutu) bai yi musu wani abin kyautatawan da zai zama

sanadiy yar shigarsa Aljannah ba53. Allah Ya turbuxe

hancinsa (ma’ana: Allah wadaransa. Domin kuwa ba zai

tava samun dacewa ba a rayuwa) .‛

52 Tirmizi (Had1si na 899) daga Sahabi Abdullahi xan ‘Amru xan Aas (Allah Ya qara

musu Yarda su biyun duka).

53 Sahih Muslim (hadisi na 2551 ) daga Sahabi Abu. -Huraira .

43

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

43

A cikin wannan hadi si za mu ga ashe biyayya ga iyaye

(da kuma kyautata musu) yana daga cikin hanyoyin

samun Gafarar Allah . Sannan rashin kyautata musu

kuma, yana daga cikin ababenda suke cire albarka a

rayuwar bawa. Allah Ya tsare mana imaninmu.

Sannan kuma akwai hadisan da suke qara tabbatar da

lallai Allah  Yana tserar da irin waxannan (masu

kyautatawa iyayensu) daga faxaw a cikin wani haxari ko

bala’i, sakamakon biyayyar da suke wa iyayensu.

Za mu ga misalin hakan a cikin hadithin da Manzon

Allah  ya bada labarin wasu mutane su uku da suka

shiga cikin wani qogo suka fake, sai wani qaton dutse

ya gangaro ya rufe qofar qogon alhalin suna ciki (ga shi

kuma acikin qungurmin daji ne mai nisa, saboda haka

babu mutane kusa ballentana su taimake su).

Saboda haka sai suka yanke shawara akan lallai ne

kowanne daga cikinsu yayi tawassuli da wani aikinsa

nagari (wanda yake fatan Allah  Ya karva masa)

wajen roqon Allah  don Ya kuvutar dasu daga wannan

halakar da suke gani ido da ido.

Sun roqi Allah  kuma Ya amsa musu. Domin kuwa

Ya kuvutar dasu daga wannan ramin da suke binne a

ciki da rayukansu.

Toh daga cikinsu akwai wanda yayi tawa ssuli da

biyayyar da yayi wa mahaifan sa (waxanda sun riga sun

tsufa) da kuma kyautata musu da yayi, tare da fifita su

akan akan iyalansa (mata da kuma yara qanana)54.

54 Bukhari ( 2272 ), Muslim ( 2743 ), daga Sahabi Abdulla hi xan Umar, Allah qara musu

yarda.

44

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

44

H. Yiwa mutane Afuwa:

Yafewa mutane abinda suka sukayi na laifi ko kuskure (da

kuma rangw anta musu), wannan babban lamari ne wanda

sai masu babban rabo awajen Allah  suke iyawa. Shi Yasa

Allah  Ya lissafa wannan aiki cikin halayen manayan

bayinSa. Misali xaya gameda hakan shi ne inda Yake cewa:

[

ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ

]

:الشورى{

37

}

‚..Kuma idan ma sukayi fushi (ma’ana idan aka vata musu

rai ta) sai kaga suna yin gafara ‛

Kenan hakan ya nuna duk mai yafewa wani, toh shi ma

Allah  Zai yafe masa. A cikin Suratun -Nur (ayah ta 22)

Allah  Yana cewa:

[

ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑ ﮒ ﮓ ﮔ

]

:النور{

22

}

‚Kuma suyi afuwa su qyale (kar su xauki wani mataki na

ramako akan wanda ya cutarda su). Shin ku baku so Allah

 Ya Gafarta muku ne? Alhalin kuma Allah  Shi ne Mai

Yawan Gafara kuma Shi ne Mai jinqai!!‛

Ka ga ashe hakan yana cikin hanyoyin samun Gafarar Allah

. Kuma Yana cikin hanyoyin samun Soyayyar Allah  ga

bawa. Shi Yasa acikin Suratu Ali -Imra n (ayah ta 134 zuwa

136) Allah  Yake cewa:

[

ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ

ﭪ ﭫ ﭬ

]

‚Su ne waxanda suke ciyarda dukiyoyinsu (a kullum)

sawa’un ana cikin walwala ne ko ana cikin qunci, suna

haxiye fushinsu, suna yafewa mutane, lallai Allah Yana son

(waxannan bayi n agari) masu kyautatwa ‛.

45

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

45

[

ﭭ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ

ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ

]

‚Kuma su ne dai waxanda idan suka aikata wani laifi ko suka

zalunci kawunansu (ta hanyar savawa Allah ) toh nan take

suke tuna Allah su nemi GafararSa gameda zunubansu, sabod a

babu mai Gafarar zunubai sai Allah , sannan (bayan haka)

basu dogewa su kafe akan abinda suka aikata (na munanan

ayuka) alhalin suna sane (suna gaggauta barin aikin, suyi

nadama akansa, su nemi Gafara Allah, sannan kuma su

qauracewa duk abinda zai iya k usanto da su zuwa ga wannan

mummunan aiki, ballenta su kuma aikata shi nan gaba) ‛.

[

ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑ

ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ

]

‚Irin waxannan suna da sakamakon wata irin G afara daga

Ubangijinsu, da kuma Aljannatai waxanda koramu (na dangin

ababen sa daban daba n) suke gudana a qarqashinsu, za su

dawwama a ciki, Madallah da (irin wannan) lada (wanda yake a

matsayin sakamako) ga waxannan ma’aikata ‛

Ko shakka babu masu yiwa mutane afwa su ma Allah  Zai

yafe musu. Saboda haka duk wanda yake kyautata niyyah

ya tausa ya wa wani, toh shi ma Allah  Zai tausaya masa.

Domin kuwa Allah  Yana jinqan bayinSa masu jinqai.

Shi yasa ma hatta mutumin da yake sassauta wa bayin Allah

a cikin kasuwancinsa, kuma ba ya tsawwala musu, toh shi

ma Allah  Zai masa afuwa a duniya da la hira (matuqar ya

mutu ba ya shirka). Allah  Zai qara wa dukiyarsa albarka,

Zai rufa masa asiri, kuma Zai kare shi daga uquba.

46

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

46

Manzon Allah  yace: ‚ Akwai wani (xan kasuwa) mutumin

kirki wanda ya kasance yana baiwa mutane bashi. A kulumm

yana cewa kowa dag a cikin yaran gidansa idan ka je gun wani

(daga cikin waxanda muke bi bashi) amma ka riske shi cikin

tsananin rashi, toh kayafe masa kawai (ka cire sunan shi daga

cikin jerin waxanda muke binsu bashi), da fatan mu ma (a gobe

Qiyama) Allah Allah  Zai Yafe mana (a daidai lokacinda

muka fi matuqar buqatar RangwamenSa da GafararSa da

RahamarSa). Da wannan bawan Allah Ya mutu ya koma ga

Allah kuwa, sai Allah  Ya Yafe masa xin55‛

Allah  Ya saka masa ne da irin abinda ya kasance

yake yiwa bayin Allah a rayuwarsa ta duniya. Da ma

masu iya Magana suka ce Alkhairi danqo ne, ba ya

faxuwa qasa banza.

Toh da yake ya kasance yana rangwanta wa bayin Allah

mabuqata a nan duniya saboda irin tsananin tausaya musu

da yakeyi, sai shi ma Allah  Ya saka masa da irin wannan

sakamako a daidai lokacinda yake matuqar buqatan hakan.

Har ma Allah  Yace masa: ‚Mu muka fi cancanta mu

rangwanta wa mabuqata. Saboda haka kai ma jeka na

yafe maka‛.

I.

Musafaha a yayin da aka gamu a na gaisawa:

Musafaha a yayinda aka gamu ana gaisawa (bayan anyiwa

juna Sallama), wannan qarin tabbaci ne gameda amincin da

yake tsakanin ‘yan -uwa Musulmi.

Riqe hannun juna a yayin sallama, yana tafiyar da qiyayya

da gaba tsakanin Musulmi, kuma yana cikin manyan

alamun soyayya da qaunar juna da kuma ‘yan -uwantaka.

55 Bukhari ( 3480 ), Muslim ( 1562 ). Dukkansu daga Sahabi Abu -Hurairah 

47

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

47

Shi yasa babban Malami Al -Imamu Hasanul -Basriy (Allah

Ya Gafarta masa) Yake cewa: ‚Musafaha tana qara qauna

(tsakanin musulmi). Idan xayanku yayi musafaha da xan -

uwansa, toh ya riqe hannunsa da kyau, domin hakan yana

qara danqon qauna (tsakaninsu). Kuma ko da yana xan jin

wani qaiqayi a zuciyarsa gameda shi, toh hakan zai

warware wannan qulli (wanda shaixan ya tufka masa a

zuciya gameda xan -uwansa musulmi)56‛.

Sannan kuma Musafaha tana tsaftace bawa daga dattin

zunubai, domin kuwa hadisai masu yawa sun ta bbatar da

cewa lallai ita ma musafaha tana daga cikin hayoyin samun

Gafarar Allah .

Manzon Allah  yana cewa: ‚ Babu wasu Musulmai biyu da

za su gamu kuma suyi musafaha (a yayin sallama, gaisuwa irin

ta Addinin Musulunci) fahce sai an Gafarta musu (zunubansu)

kafin su rabu57 (kafin su saki hannun junansu) ‛.

Da fatan Allah Yasa mu dace.

Manzon Allah  yace: ‚Lallai shi mumini idan ya gamu da

(wani xan -uwansa) mumini, sai yayi masa sallama, sannan ya riqe

hannunsa suka gaisa; toh zunubansu za su riqa kakkavowa (daga

jikinsu) kamar yadda (busassun) ganyayyakin bishiya suke

zubowa qasa idan i ska ta kaxa su58‛

Yana da kyau a kiyaye, kuma a riqa raya wannan Sunnah,

saboda fatan samun wannan falala mai yawan gaske da aka

ambata cikin wannan ingantaccen hadithi mai daraja.

56 Duba: Amaaliy na Ibnu Sam’un Al -waa’iz, majalisi na 14, juz’i na farko, sahafi na 230

57 Abu-Dawud (hadithi na 5212 ) daga Sahabi Baraa’u xan Aazib All ah Ya qara musu

Yarda

58 Imam Ax -xabaraniy ne ya ruwaito shi a cikin littafinsa mai suna ‚Mu’jamul -Ausax‛

(Juz’i na farko, shafi na 84, kuma hadisi na 245) daga Sahabi Huzaifah xan Yamaniy 

48

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

48

Ba daidai ba ne irin durquson nan da akeyi ko rusunawa da

sunan wai girmamaw a, da dai sauran nau’ukan gaishe -gaishe

waxanda suka samo asali daga al’ adun al’ummomi daban

daban. Wa nnan kwata -kwata ba gaisuwar Musulunci ba ce.

Karantarwar Manzon Allah  ita ce riqe hannun juna ayi

musafaha . Bayan xumbin falalar da yake tattare da su, mun ji

kuma cewa hakan yana cikin hanyoyin samun Gafarar Allah

.

Sannan kuma ba ya halatta Musulmi yayi musafaha da wata

mace wacce ba muharramarsa ba. Haka kuma irin wann an

musafaha da wasu suke yi suna wasa da ‘yan yatsu (har ma a

wasu lokutan ana motsa wa juna sha’awa), wannan ba

karantarwar musulunci ba ce. Amma in har matarka ce ka

kama hannunta, wannan babu matsala, domin kuwa ita kam

ta halatta gareka da ma.

Haka nan kuma ba sunnah ba ne yin musafaha da hannu

biyu dukka. Abinda ya tabbata a sunnah shi ne yi da hannu

xaya kawai (kuma hannun dama, ga wanda yake da hannun

dama xin kenan).

Malamai ma suna tsawatarwa gameda yadda wasu suka tsiri

al’adar yin musafaha a daid ai lokacinda aka sallame sallah.

Har ma wasu sun xauka ko hakan ma mantacciyar sunnah

ce suke rayawa . Ko shakka babu wannan bai da a sali a cikin

karantarwar Manzo . Abinda ya tabbata a Sunnah dai, shi

ne akwai wasu zikirorinda ake karantawa bayan an salla me

sallah. Toh wannan shi ya kamata a shagaltu da shi, ba wai

wata qirqirarriyar musafaha ba.. Sai dai wannan ba zai hana

daga baya a miqawa juna hannu a gaiggaisa ba. Amma riqe

hakan a matsayin wata al’ada, toh wannan ne bai da asali a

cikin karantarwar M anzon Allah . Allah Yasa mu dace.

49

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

49

J. Taruwa don karatun addini , da kuma darasin sa:

Irin wannan taro yana daga cikin wasu manyan taruka guda

uku waxanda a cikinsu ne kaxai ake samun Alkhairan

duniya da lahira, koma bayan wasu tarukan da ba su ba.

Domin kuwa acikin S uratun -Nisa’i (ayah ta 114) Allah 

Yana cewa:

[

ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟ ﭠ

ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ ﭬ

]

:النساء{

114

}

‚Babu Alheri cikin da dama daga cikin tarukansu (su

mutane), sai wanda a cikinsa akayi umurni da wata sadaka

(da duk abinda zai amfanar da gangan jikin xan Adam), ko

kuma (umurni da) wani kyakkyawan aiki (da duk abinda zai

amfanar da ruhin xan Adam), ko kuma (tattaunawar da ta

qunshi) sasantawa tsakanin mutane (don a samu wanzuwar

zaman lafiya a cikin al’ummah). Toh duk wanda ya aikata

(xaya daga cikin) wannan alhalin yana mai neman Yardar

Allah , nan gaba (a lahira) Za Mu bashi Lada mai Girma ‛

Manzon allah  yana cewa: ‚ Babu wasu mutanen da za

su taru a cikin xaya daga cikin xakunan Allah su riqa

karanta Littafin Allah kuma suna darasin sa a

tsakankaninsu; fahce sai nitsuwa ta sauka akansu, kuma

sai Rahama ta lulluve su, sannan kuma Mala’iku (na

Rahma) za su kewaye su (da Umurnin allah  za su

katange su daga dukkanin sharri), sannan kuma allah 

zai ambace su a cikin waxanda suke tare da shi59‛.

Allah  zai ambaci sunayensu xaya bayan xaya a gaba n

Mala’ikunsa, sannan Yace musu (su Mala’ikun): ‚ Ina

59 Sahih Muslim (hadithi na 2689), daga Sahabi Abu -Hurairah 

50

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

50

mai kafa ku shaida akan cewa lallai haqiqa na Gafarta

musu60 (baki xayansu) ‛

Shi yasa akeso a kowanne lokaci mu riqa qoqarin

halartan wuraren da ake karatun addini, da wurarenda

ake wa’azi. Saboda akwai f alala mai xumbin yawa a

waxannan wurare.

Daga cikinsu dai, akwai samun Gafarar Allah .

Shi yasa aka shar’anta mana karanta ‚Kaff aratul-Majlis‛ ..

A duk lokacinda aka zo tashi daga inda ake zaune61 toh

a riqa karanta wannan addu’a wacce ake kira kaffaratul-

majlis (wato addu’ar neman gafarar Allah  gameda

zunuban da aka aikata a cikin wanna n zama da akayi) .

Ga yadda addu’ar take:

سُبْحَانَكَ اللَّهُمَّ وَبِحَمْدِكَ، أَشْهَدُ أَنْ الَ إِلَوَ إِالَّ أَنْتَ، أَسْت َغْفِرُكَ وَأَتُوبُ إِلَيْكَ

Ma’ana: ‚ Dukkan Tsarki da Yabo da Godiya sun tabbata

gareKa Y a Allah. Na shaida lallai babu abin bauta (bauta ta

gaskiya a bisa cancanta) sai Kai (Kai kaxai kake, b aka da

abokin tarayya). Ina neman GafararKa kuma na tuba zuwa

Gareka62‛

Manzon Allah  ya kasance yana karanta wannan addu’a a

duk lokacinda yazo tashi daga inda yake zaune. Kuma yace

duk wanda ya ke yin haka, toh Allah  Zai yafe masa

zunuban sa.

K. Zikiri (ambaton Allah )

60 Bukhari (2408), Muslim (2689), daga Sahabi Abu -Huraira 

61 Ko a ina ne (sawa’un wurin karatu ne ko wata ganawa, ko hira, ko wani aiki, ko

kasuwanci da dai sauransu)

62 Tirmidhi (hadithi na 3433), Ahmad (hadithi na 10420), daga Sahabi Abu -Huraira 

51

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

51

Acikin Suratul -Ahzab ( Ayah ta 35) Allah  Ya lissafa

masu yawan zikiri cikin waxanda Yayi musu tanadin Gafara

da kuma lada mai yawa. Yace:

[

ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ

]

‚Har da kum a maza da mata masu zikiri da yawa, toh (baki

xayansu) Allah Ya musu tanadin Gafara da kuma wata Lada

mai Girma ‛.

Akwai hadisai masu yawa da suke tabbatar da cewa lallai

bawa zai samu Gafarar Allah  matuqar yana yawan

ambatonSa kamar yadda Shari’a ta kara ntar. Daga cikin

zikirorin da Manzon Allah  ya kwaxaitar damu mu riqa

karanta su don samun Gafara da kuma lada mai yawa,

akwai waxannan:

Zikirorin safe da yamma:

Karanta wannan addu’a wacce ake kira Sayyidul -Istighf ar

(mafi girma cikin addu’o’in neman G afara ) safe da yamma:

اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي الَ إِلَوَ إِالَّ أَنْتَ، خَلَقْتَنِي وَأَنَا عَبْدُكَ، وَأَنَا عَلَى عَهْدِكَ وَوَعْدِكَ مَا اسْتَطَ عْتُ،

أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا صَن َعْتُ، أَبُوءُ لَكَ بِنِعْمَتِكَ عَلَيَّ، وَأَبُوءُ لَكَ بِذَنْبِي فَاغْ فِرْ لِي، فَإِنَّوُ الَ

ي َغْفِرُ الذُّنُوبَ إِالَّ أَنْتَ

‚Ya Allah Kai ne Ubangiji na, babu abin bauta (bauta ta

gaskiya a bisa cancanta) sai Kai. Kai ne Ka halicce ni. Kuma

ina nan kan umurnin nan n aKa (da Kayi wa bayinKa) da

kuma alqawarin nan naka (wa nda yake tsakaninKa da

bayinKa) gwargwadon iyawa ta. Ina neman tsarin Ka daga

sharrin abinda na aikata (na laifi). Ina mai iqirari (da kuma

godiya gareKa) gameda ni’imominKa a kaina (waxanda babu

wanda yasan yawansu sai Kai). Na na tabbatar lallai ina da

zunubai (masu yawa), ina kuma neman Ka Gafarta min,

domin kuwa babu mai Gafarar zunubai sai Kai ‛.

52

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

52

Manzon Allah  yace: ‚ Lallai duk wanda ya faxe ta da rana

alhali yana mai yaqini da ita63, sannan sai yam utu a ranar

kafin maraice, toh yana cikin ‘yan Aljannah. Haka kuma

duk wanda ya faxe ta da dare alhalin yana mai yaqini da ita,

sai yam utu kafin asubahi, toh yana cikin ‘yan Aljannah64‛

Ko shakka babu wannan addu’a tana da muhimmanci sosai .

Ya kamata mu haddace ta, musan ma’anarta, mu koya wa

iyalanmu, kuma mu riqa karanta ta a kullum. Da fatan Allah

Yasa mu dace.

Kuma a riqa karanta wannan zikirin sau xari ( 100) a rana:

الَ إِلَوَ إِالَّ اللَّوُ، وَحْدَهُ الَ شَرِيكَ لَوُ، لَوُ الْمُلْكُ، وَلَوُ الْحَمْدُ، وَىُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ

‚Babu abin bauta da gaskiya a bias cancanta sai Allah, Shi

kaxai Yake Bai da abokin tarayya, dukkan Mulki da dukkan

yabo da godiya naS hi ne (Shi kaxai), kuma Shi ne Mai

cikakken iko akan dukkan komai ‛

Manzon Allah  yace duk wanda ya karanta ta sau xari a

rana, ‚ toh daidai yake da wanda ya ‘yanta bayi goma65, za

kuma a rubuta mishi kyawawan ayuka har guda xari66, a

kuma kankare masa munan an ayuka guda xari. Sannan

kuma (wannan addu’a) za ta zame masa (wata irin) kariya

daga shaixan a duk wannan yini har zuwa maraice. Haka

nan kuma babu wanda zai zo (a lahira) da aikinda yafi

(wannan aikin) nashi falala sai wanda ya aikata sama da

abinda ya aikata67‛

63 Wato ya qu durce a zuci cewa da gaske neman gafara yake, kuma ya yarda cewa Allah

Shi ne kaxai Mai Gafarta wa bayi

64 Sahihul -Bukhari (hadithi na 6306 ) daga Sahabi Shaddau xan Aus 

65 Mun riga kuma mun ga irin falalar da ‘yanta bawa xaya ma yake da ita a can baya.

66 Tare da kuma duk wani kyakkyawan aiki guda xaya ana ninka shi sau goma ne har zuwa

sau 700 ko ma fiye da hakan, gwargwadon baiwar da Allah  Yayiwa bawanSa.

67 Sahihul -bukhari ( 3293 ), Sahih -muslim (2691), daga Sahabi Abu -Huraira 

53

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

53

Wannan zikiri yana da matuqar muhimmanci sosai.

Saboda yana jaddada tauhidin bawa, kuma Yana qara

masa qarfin imani da kuma yaqini da tawakkali, sannan

kuma yana cire wa bawa tsoron wata halitta.

Daga cikin Hanyoyin Samun Gafarar Allah, akwai f axin

waxannan kalamai m asu daraja sau xari a rana, wato a

ce:

سُبْحَانَ اللَّوِ وَبِحَمْدِهِ

‚Dukkan Tsarki da Godiya sun tabbata ga Allah ‛

Manzon Allah  yace duk wand ya faxi wannan zikiri sau

xari (100) a rana guda, ‚ Za a Gafarta masa zunubansa ko da

kuwa sun kai kwatankwacin (yawan) kumfar teku ne68‛

Waxannan kalmomi dai suna da sauqin faxi, ga daxi da

kuma zaqin furtawa. Allah  ne Ya zava mana su don mu

riqa furtawa don mu samu GafararSa. Mu riqa kula da kyau,

kar mu manta da wannan Sunnah, saboda mu ma mu samu

Rahamar Allah .

Sai dai abin takaici yanzu za ka iske mutum musulmi yana

da lokacin zama yayi ta zabga surutu a wajen hira, yana da

lokacin sauraren duk wata waqa da duk wata sharholiya,

amma bai da lokacin da zai iya warewa domin nitsuwa ya

ambaci Allah . Allah Ya tsare mu daga sharrin shaixan.

A yayin da aka ji kiran sallah

Idan aka ji Ladani yana Kiran Sallah, toh ana so kowa ya

maida hankal i ya saurara da kyau. Saboda a daidai wannan

lokaci akwai wasu zikirorin da Manzon Allah ya umurce

mu da mu riqa furtawa.

68 Sahihul -Bukhari (Hadithi na 6405) daga Sahabi Abu -Huraira 

54

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

54

Daga cikinsu akwai:

أَشْيَدُ أَنْ َلَ إِلَوَ إَِلا اهللُ وَحْدَهُ َلَ شَرِيكَ لَوُ، وَأَنا مُحَمادًا عَبْدُهُ وَرَسُولُوُ، رَضِيتُ

بِاهللِ رَبًّا وَبِمُحَمادٍ رَسُوَلً

‚Na shaida ba bu abin bauta ( a bisa cancanta) sai Allah , Shi

kaxai Yake Bai da abokin tarayya. Kuma lallai Annabi

Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa. Na yarda da Allah a

matsayin Ubangiji . Na yarda da muhammadu a matsayin

Manzo. Na kuma yarda da Musulunci a matsayin Addini (wanda

dole sai ta hanyarsa kaxai za a bau ta wa Allah  Ya karva) ‛

Manzon Allah  yace duk wanda ya faxi wannan zikiri (a

irin wannan lokacin) ‚ za a Gafarta masa zunubansa69‛

Faxin Kalmar ‚ Ameen‛ a Yayinda aka kai Qarshen Suratul -

Fathiha

Manzon Allah  yana cewa: ‚ Yayinda Liman ke faxin

Ameen , toh ku ma ku fax a (tare da shi). Domin kuwa duk

wanda faxinsa ya dace da faxin Mala’iku, toh za a Gafarta

masa abinda ya gabata na zunuban sa70‛.

Zikirin da ake Karantawa Yayin Xagowa daga Ruku’u

Idan aka xago daga ruku’u, Limami yana cewa:

سَمِعَ اللَّوُ لِمَنْ حَمِدَهُ

‚Allah Yana jin mai gode Masa (Kuma Yana amsa addu’ar

duk mai roqon S a)‛

Shi kuma m amu sai yace:

اللَّهُمَّ رَب َّنَا وَلَكَ الْحَمْدُ

‚Ya Allah Ubangijina, dukkan yabo da godiya sun tabbata

gareKa (Kai kaxai b aKa da abokin tarayya) ‛.

69 Sahih -Muslim (Hadithi na 387) daga Sahabi Sa’adu xan Abu -waqqas 

70 Sahihil -Bukhari (Hadisi na 780 ) daga Sahabi Abu -Huraira 

55

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

55

Haka Manzon Allah  yayi umurni. Kuma yace duk wanda

ya faxi hakan sannan ya dace da na Mala’iku, to shi ma za a

Gafarta masa abinda ya gabata na zunubansa71‛.

Zikirin da ake karantawa bayan Sallama:

Idan aka sallame sallah ma, ai akwai wasu addu’o’I da

zikrori daban -daban waxan da Sunnah ta koyar a riqa

karantawa k afin a tashi72.

Daga cikinsu akwai Tasbihi sau 33, Hamdala sau 33,

kabbara sau 33, daga qarshe kuma a cike da faxin:

َلَإِلَوَ إَِلا اهللُ وَحْدَهُ َلَشَرِيكَ لَوُ، لَوُ الْمُمْكُ وَلَوُ الْحَمْدُ، وَىُوَ عَمَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ

‚Babu abin bauta da gaskiya a bisa cancanta sai Allah ,

Shi kaxai Yake bai da abokin tarayya, dukkan mulki da

godiya baki xaya n aShi ne (Sh i ne Mamallakin komi da

kowa, kuma Shi ne cikakken abin yabo gameda komai),

Kuma shi mai cikakken iko ne akan dukkan komai ‛.

Duk wanda ya karanta waxannan zikirorin kamar yadda

aka ambata, Manzon Allah  yace ‚Za a Yafe masa

laifukansa ko da kuwa sun kai k watankwacin yawan kumfar

teku ne73‛

A yayin da aka gama cin abinci (ko abin sha).

Yin Hamdalah bayan an gama cin abinci, yana daga

cikin muhimman hanyoyin samun gafara, mu samman

ma karanta wannan addu’a kamar haka :

71 Bukhari (Hadisi na 796) daga Sahabi Abu -Huraira 

72 Zikrorin nan fa dole ne sai irin wax anda Manzon Allah  ya karantar kawai za ayi (babu

qari babu ragi).

73 Sahih -Muslim (Hadithi na 597) daga Sahabi Abu -Huraira 

56

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

56

الْحَمْدُ لِماوِ الاذِي أَطْعَمَنِيىَذَا الطاعَامَ وَرَزَقَنِيوِ مِن غَيْرِ حَوْلٍ مِنِّي وََلَ قُواةَ

‚Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda Ya ciyar

da ni wannan abincin, kuma Ya arzuka ni da shi ba tare da wata

dabara ta ko qarfi daga gareni ba ‛.

Manzon Allah  yace ‚duk wa nda ya karanta wannan addu’a

bayan ya agama cin abinci, toh za a G afarta masa abinda ya

gbata na zunubansa ‛

L. Jihadi don xaukaka addinin Allah:

Jihadi shi ne tozon Addinin Musulunci74. Kuma Kasuwanci

ne mai riba sosai tsakanin bawa da Mahaliccinsa. A cik in

Suratut -Taubah (ayah ta 111) Allah  Yace:

[

ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ

ﯤ ﯥ ﯦ ﯧ ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ ﯯ ﯰ ﯱ

ﯲ ﯳ ﯴ ﯵ ﯶ ﯷ ﯸ ﯹ ﯺ ﯻ ﯼ ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ

]

‚Lallai Allah  Ya sayi rayukan Muminai da kuma

dukiyoyinsu, cewa lallai suna da Aljannah (a matsayin

abinda za a biya su da shi). Suna yin (amfani da dukiyoyin

nasu da kuma rayukansu wajen) yaqi cikin (xaukaka)

tafarkin Allah, domin kuwa (a fagen daga ) suna kashewa

kuma su ma ana kashesu. Alqawari ne tabbatacce wanda

Allah  Yayi acikn (littatafan) At -Taurah da Injila da kuma

Al-Qur’ani, kuma babu cikakken mai cika alqawarinda ya

xauka irin Allah . Saboda haka ku kasance cikin Albishir

saboda wannan cinikin naku da kuka qulla daShi. Kuma

wannan shi ne babban rabo mai girman gaske .‛

74 Sahih Muslim (Hadithi na 121) daga Sahabi Amru xan Aas 

57

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

57

Jihadi don xaukaka Addinin Allah , wani irin

kasuwanci ne wanda baki xayansa r iba ce zallah babu

faxuwa, domin kuwa da Allah  aka qulla shi. Saboda

haka ma daga cikin farashinsa akwai Gafarar Allah da

kuma Aljannah (bayan nasarar da Allah Yayi alqawarin

Zai baiwa duk wanda ya tsaya ya kyautata niyyah yayi

Jihadin da gaske).

A ciki n Suratus -Saff (ayah ta 10 zuwa ta 13) Allah 

Yana cewa:

[

ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ

ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ

ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵ ﮶ ﮷ ﮸ ﮹ ﮺ ﮻ ﮼ ﮽ ﮾ ﮿ ﯀

﯁ ﯂ ﯃ ﯄ ﯅ ﯆ ﯇ ﯈ ﯉ ﯊ ﯋ ﯌ ﯍ ﯎ ﯏ ﯐ ﯑ ﯒ ﯓ ﯔ

ﯕ ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ

13

]

‚Ya ku waxanda kukayi imani! Shin (kuna so) in nuna

muku wani i rin kasuwanci wanda zai zama sanadiyyar tsirar

ku daga azaba mai raxaxi?‛

Wannan kasuwanci shi ne; Kuyi imani da Allah  da

ManzonSa r, kuma kuyi Jihad i don xaukaka tafarkin Allah .

Wannan dai shi ne (yafi zama) Alhairi gareku in har da kun

kasance kun sani‛.

Zai Gafarta muku zunubanku kuma Zai shigar daku

Aljannatai waxanda koramu (na ababen sha iri -iri) suke

gudana a qarqashinsu, Zai b aku wasu irin kyawawan gidaje

masu daxin zama a cikin waxannan aljannatai waxanda

suke an riga ayi tanadinsu , wannan dai b abban rabo ne .

Kuma akwai ma sauran (wasu nau’uka na tukuici) na daban

waxanda (tabbas) kuna son su (a wannan rayuwa ta duniy a),

58

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

58

su ne; Taimako daga Allah75 da cin nasara (akan abokan

gab) wanda yake nan kusa (za ku samu in har kuka qara

qanqame wannan tafark i madaidaici). Kuma (Y a

Muhammadu) kayiwa Muminan nan (masu Jihadi) bishara

(domin kuwa duk abinda suke buqata a duniya da lahira

sakamakon wannan jajircewa da sukayi don kare wannan

Addini) ‛.

Allah  Ya yi alqawarin Gafarta wa Mujahidai; domin

kuwa dasu Yake yaxa addininSa, dasu Yake kare addinin,

kuma dasu Yake xaukaka shi akan duk wani addini na

daban wanda ba shi ba. Matuqar musulmi sunyi riqo da

karantarwar wannan Addini na Allah , toh kuwa ba za su

tave ba har abada.

A cikin Suratul -Anfal (ayah ta 74) Allah  Yana cewa:

[

ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ ﯤ ﯥ ﯦ

ﯧ ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ

]

‚Su kuma waxanda sukayi imani kuma sukayi kuma

sukayi Jihadi don xaukaka Tafarkin Allah, da (sauran

Muminai) waxanda suka bayar da masauki (ga masu

hijira) kuma sukayi taimako (da duk abind a Allah  Ya

hore musu don xaukaka Addinin Allah); waxannan

(baki xayansu) su ne muminai na gaskiya. Suna da

Gafara da kuma wani irin arziki mai yawa (na ababen ci

da sha da duk sauran ababen more rayuwa) irin na

girmamawa ‛.

75 Ta hanyar qara tabbatar da ku akan wannan tafarki madaidaici,Ya kuma karya lagwan

abokan gaba har kuyi galaba akansu.

59

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

59

Allah  Ya musu tanadin wasu ir in gidaje na alfarma

acikin Aljannah.

Manzon Allah  Yana cewa: ‚ Lallai a cikin Aljannah

akwai wasu irin (benaye masu) darajoji xari (hawa 100)

waxanda Allah  Yayi tanadin su ga masu Jihadi saboda

xaukaka AddininSa. Tsakanin kowacce daraja da wacce take

sama da ita kamar nisan da yake tsakanin sama da qasa76‛.

M. Mutuwar Shah ada77

Mutuwar Shahada (Shahada ta gaskiya) tana daga cikin

manyan ni’imomin da Allah Yake yi ga wasu zavavvu

daga cikin bayinSa na qwarai. Kuma duk wani Salihin

bawa ya kasance yana fat an samun wannan daraja ta

shahada.

Saboda; bayan xumbin lada da kuma falalar da take da

su masu yawa, tana ma cikin manya -manyan hanyoyin

samun Gafarar Allah .

Bayan ayoyin Al -Qur’ani, akwai Hadisai ma masu yawa

da sukayi bayanin falalar mutuwar Shahada.

Falalar mutuwar Shahada

Ga kaxan daga cikinsu78 insha’Allah:

Za a yafe wa mai mutuwar Shahada laifukansa tun a.

daga xigon jininsa na farko a lokacinda yazo mutuw a.

Tun a lokacin za a nuna masa mazauninsa na cikin b.

Aljannah.

76 Sahihul -Bukhari (hadithi na 2790) daga Sahabi Abu -Huraira 

77 Mutuwar mumini a yayinda yake fafitikar kare Addini a fagen daga, ko kuma a kashe shi

a yayinda yake faman kare mutuncinsa ko mutuncin iyalansa , ko kuma a yayinda yake

faman kare dukiyarsa, ko kuma wata hanya daga cikin hanyoyin da shari’ah tayi bayani.

Allah Ya arzukta mu da irin wannan mutuwa.

78 Daga kan ‚‛ zuwa ‚ ‛ duk sun zo a dunqule cikin hadisi guda, duba: Tirmizi ( 1663 )

daga Miqdaamu Ibn Ma’adiy -karib 

60

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

60

Za a amintar dashi daga fitinar Qabari (ba za a fitine shi c.

ba, kuma ba za a azabtar da shi ba).

d.

Za a amintar da shi daga wannan firgici mafi girma na

ranar qiyamah (saboda haka bai da fargaba kuma babu

baqin ciki tare da shi har abada79).

A lahira za a xaura masa wani irin kambe na girmamawa e.

a kansa, na yaqutu, wanda guda xaya daga cikinsu ya fi duk

duniya da abinda yake cikinta.

Za a xaura masa aure da wasu mata na musamman (har f.

su 72) daga ci kin matan Aljannah (tun a lokacinda ake z are

ran shi daga gangar jikinsa).

g.

Kuma a lahira za a bashi damar ceton har mutum 70

daga cikin danginsa.

Ba ya jin zafin fitar rai, sai kamar gwargwadon zafin *

cizon cinyaka80

A cikin Aljannah kuma, zai riqa burin inama ayi ta dawo *

dashi duniya a qara kashe shi ta wannan hanya har sau

goma. Ba don komi ba sai saboda irin abinda ya gani na

falalar shahada81, da irin girmamawar da ya samu a cikin

Aljannah .

Waxannan dai suna daga cikin jerin falalolin da mutuwar

shahad a ta gaskiya take tattare da su. Na ce shahada ta gaskiya

ne, saboda akwai waxanda ba na gaskiya ba. Toh su (na

qaryan) banda su a cikin waxanda za su samu wannan falalar

da akayi bayani. Domin kuwa babu wanda zai samu sai wanda

ya cika sharuxan karvar iba da (wato yi don neman Yardar

Allah , da kuma dacewa da karantarwar Manzon Allah ).

79 Za atsare masa iyalansa (waxanda ya mutu ya bari a duniya), ba za su tagayyara ba,

kuma insha’Allah ba za su kauce hanya ba su ma.

80 Imam Ahmad ( 7953 ), Tirmizi (1668), Nasa’i ( 3161 ), Ibn Hibban ( 4655 ).. Daga Abu -

Huraira .

81 Bukhari ( 2817), Muslim ( 1877 ) duk daga Sahabi Anas xan Maalik 

61

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

61

Za mu gane hakan ne idan muka san kashe -kashen

shahada. Ga su nan (a gurguje) kamar haka insha’Allah.

Saboda lura da nassoshin Al -Qur’ani da kuma ingantattun

hadithai, Malamai sun karkasa nau’ukan shahada zuwa kashi

uku. Su ne kamar haka:

1) Sukace akwai masu hukuncin shahda a duniya kaxai, banda

lahira.

Su ne waxanda a idanun mutane dai mutuwar shahda sukayi,

amma a wajen Allah su ba shahidai ba ne, saboda basu cika

sharuxan karvar aiki ba.

Su ba shahidan gaskiya ba ne. Shahidan qarya ne. Amma da

yake babu wanda yasan matsayinsu sai Allah  (Masanin

baki xaya voyayyu da bayyanannun al’amura), toh dole za

ayi musu yadda ake wa shahidan gaskiya anan duniya.

Don haka ba za ayi musu wanka ba kuma ba za ayi musu

Sallah ba, A hakan za a xaukesu cikin jinin nasu aje a binne a

maqabartar Musulmi ( tunda a filin yaqi aka kashesu, kuma

babu wanda yasan abinda suka qudurce a zuci sai Allah ).

-Su ne irin munafukan nan waxanda saboda qwarewa a

munafunci har ma sun kai ga suna bin Musulmin qwarai

Jihadi (saboda wasu manufofi nasu na karan kansu), sai k uma

suyi rashin sa’a ta ritsa da su a cikin gumurzun yaqi a kashe

su a can.

-Daga cikin masu irin wannan hukunci akwai wanda zai tashi

yaje filin jihadi kuma a kashe shi a chan, amma ba don kare

addinin Allah yaje ba shi kam. Ya je ne kawai don ya nuna

wa duniya cewa shi ma fa jarumi ne.

Waxannan kam a lahira basu da komai awajen Allah sai

azaba mai tsanani. Suna ma cikin jerin mutum uku waxanda

62

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

62

dasu ne za a hura wutar jahannama a ranar (su zasu fara shiga

wuta kafin duk wani kafiri).

2) Akwai kuma mai huku ncin shahada a lahira kaxai banda

duniya. Shi kam ana wanke gawarsa, kuma ana masa Sallah,

sannan aje a binne shi a maqbartan Musulmi.

Shi ne wanda ya mutu ta xaya daga cikin waxannan hanyoyi

(alhalin yana musulmi):

-Wanda ya mutu a yayin kare dukiyarsa, d a mutuncinsa dana

iyalansa,

-Wanda akayiwa kisar gilla saboda kaxai ya yi riqo da

Addinin Allah, ko ma yana kira zuwa gareshi (amma ba a

filin yaqi aka kasheshi ba),.

-Irin wanda ruwa ya cinye shi,

-Wanda gini ya rushe akansa ya kashe shi,

-Wanda gobara ta zama ajalinsa,

-Wanda ya mutu sanadiyyar wata annoba ta cuta da ta varke a

garinda yake,

-wanda ya mutu sanadiyyar ciwon ciki (irin matsanacin

ciwon cikin nan mai murxe mutum ya kasha shi lokaci guda,

-Wacce ta mutu sakamakon wahalar naqudar haihuwa,

Da d ai sauran makamantansu waxanda hadisai sukayi

bayanin cewa su ma suna da darajar shahada.

Saboda haka za su samu falalar da shahidin gaskiya yake

samu gwargwadon hali insha’Allah.

3) Sannan akwai kuma wanda aka fi sani da wannan suna na

shahidi, wato mai huk uncin shahada a duniya da lahira baki

xaya.

Shi ne Muminin da aka kashe shi a filin ya qi tsakanin

musulmi da kafirai.

Wannan a duniya hukuncin gawarsa daban ne da sauran

gawaki. Domin kuwa ba a masa wanka, kuma ba a masa

63

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

63

Sallah. Haka za a xauke shi cikin jinin nashi a binne shi a

wurinda ya mutu xin.

Sannan kuma a lahira, yana da waxancan falalolin da aka

ambata acikin ayoyi da ingantattun hadithan da sukayi

bayanin falalar mutuwar shahada. Daga falalolin dai, akwai

samun Gafarar Allah .

Allah  Zai Yafe wa duk wanda yayi mutuwar shahada da

kyakkyawar niyyah (kuma yake kan tafarkin Manzon Allah

). Zai yafe masa baki xaya zunuban da ya aikata. Amma fa

laifukanda yayiwa Allah ne kaxai za a yafe masa, banda

haqqin mutane82.

Domin kuwa Manzon Allah  ya ce: ‚ Allah  Zai

Gafarta wa Shahidi dukkan komai (na laifinda ya aikata

a rayuwarsa) fahce bashi83 (wanda wasu suke binsa) ‛.

Allah Yasa mu gama da duniya lafiya, Ya tsare mu daga

taurin bashi da kuma rinjayen maqiya, da kuma

mummunan abin ji da mummunan abin gan i a duniya da

lahira.

Allah Ya Arzukta mu da mutuwar Shahada ta gaskiya.

(Hanya ta Bakwai)

(sawa’un a jikinsa ne ko iyalansa ko dukiyarsa)

82 Idan akwai haqqin wani akansa kam, toh wannan hukuncinsa daban. Mun riga mun ga

bayani akan wannan tun a farkon wannan littafi, inda aka lissafo sharuxan tuba. Allah Yasa

mu dace.

83 Sahih -Muslim (hadith i na 1886) daga Sahabi Abdullah xan Amru xan Aas (shi da

Mahaifin naashi baki xayansu sahabbai ne) Allah Ya qara Yarda dasu.

64

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

64

Jarrabawa sunnar Allah  ce. Rayuwar ma baki xayanta

jarraba wa ce. Domin kuwa an kawo mu duniya ne don

mu rayu a cikinta na wani lokaci, wanda a ciki ne za mu

aikata abinda za a saka mana da shi bayan mutuwar mu.

Allah  Yana cewa (a farkon Suratul -Mulk):

[

ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ

۝

ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ

ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ

]

‚Albarkatun (Allah) sun yawaita, wanda b aki xaya mulki

(mallakar komi da kowa) a hannunSa yake, kuma Shi xin

mai cikakken iko ne akan dukkan komai. Shi ne wanda

wanda Ya halicci mutuwa da rayuwa baki xaya, domin Ya

jarraba ku (Ya w are su waye ne) daga cikinku masu

kyautata ayukansu. Kuma Shi ne Mabuwayi Mai Gafara ‛.

Kowa daga cikin mutane akwai nau’in jarabawar da

Allah  Yake masa a rayuwa. Akwai waxanda ake

jarabtar su da jin daxin rayuwa, akwai kuma waxanda

ake jarabtar su da wahalha lun rayuwa.

Wasu ana jarabtar su ta dukiyoyinsu, wasu ta iyalansu,

wasu ta mulkinsu, wasu ta lafiyarsu, wasu ta iliminsu

(na addini ko na zamani), wasu ma ta sashen addininsu,

da dai sauransu. Kowa ana jarabtar shi ta waxannan

fannoni na rayuwa (da ma sau ran da ba’a ambata ba)

imma da jin daxi ko kuma akasin hakan.

Allah  Yana cewa:

[

ﯺ ﯻ ﯼ ﯽ ﯾ ﯿ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃ ﰄ ﰅ

]

:األنبياء{

35

}

‚Kowacce rai (dole) za ta xanxani mutuwa. Kuma Muna

jarabtar ku da sharri (dangin ababenda kuke qi) da kuma

65

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

65

Alkhairi (dangin ababenda kukeso) don kawai Mu gwada

ku. Kuma gareMu za ku koma (Mu baku sakamakon duk

abinda kuka aikata a rayuwarku ta duniya) ‛

Ga abinda ya dace bawa yayi idan Allah

Ya jarabce

shi da wani abu na jin daxin rayuwa:

Lallai kam daga cikin mutane akwai wanda za a b ashi

xaukaka ko dukiya ko lafiya da sauran ababen jin daxi na

rayuwar duniya (wani za a haxa masa masu yawa, wani

kuma kaxan, wani ma guda xaya za a bashi gwargwadon

hali), ba don komi b a sai don a jarraba godiyarsa.

Mai rabo a wajen Allah  shi ne zai go de maSa akan duk

wata ni’imar da Ya bashi. Hakan kuma zai zama sanadiyyar

samun qari daga Allah , da kuma albarkar rayuwa, da tsira

daga uqubarSa a duniya da lahira.

Shi kuma mara rabo, toh zai butulce yaqi gode masa.

Hakan kuma zai zama sanadiyyar fush in Allah da uqubarSa

gareshi a duniya da lahira (in har bai tuba ya koma ga Allah

ba). Don haka a cikin Suratu Ibrahim  (ayah ta 7) Allah

 Yake cewa:

[

ﭭ ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ

7

]

‚Tuna lokacinda Ubangijinku Ya shelanta cewa ‚Lallai in

har kunyi godiya (gam eda ni’imomin da Nayi muku) toh

Zan qara muku. In muka kuka butulce, toh fa (ku sani) lallai

azabah Ta mai tsanani ce ‛

Allah  Ya b amu misalai masu yawa akan wannan al’amari

a cikin wasu ayoyi na al -Qur’ani Mai girma, gameda masu

gode miShi da kuma masu bu tulci.

Ya faxi halaye da kuma sakamakon kowanne daga cikinsu.

Duk hanyar da mutum ya zava 9sawa’un shiriya ce ko vata),

toh akwai sakamakon da aka tanadar wa masu bin ta.

66

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

66

Kai tsaye za mu gutsuro kaxan daga cikin kowanne vangare

don buga misali insha’All ah. Da fatan Allah Maxaukaki Ya

sanya mu cikin bayinSa shiryayyu masu gode maSa, Ya

tsare mu daga kasancewa vatattu masu butulce maSa.

Daga cikin Misalan masu godiya akwai labarin Annabi

Sulaimanu84 . yayinda ya ga an bi umurninsa anyi abinda

duk duniya b abu sarkin wani gari da zai iya samun hakan);

sai yace:

[

ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴

]

:النمل{

40

}

‚Wannan (lallai) falal ce daga cikin falalar Ubangiji na (ba

iyawa ta bace ko dabara ta ko qarfin mulki na). Ya yi hakan

ne kuma don Ya jarabce ni (Ya gani) shin godiya zanyi ko

kuma zan butulce ne? Lallai duk wanda yayi godiya (ga

Allah a bias wata ni’imar da Yayi masa) toh fa ya yi godiyar

ne don kansa (saboda shi ne zai samu sakamakon aikinsa a

gobe qiyamah). Wanda kuma ya butulce (ya qi godewa

Allah, toh fa kansa yayiwa) domin kuwa lallai Ubangiji na

cikakken Mawadaci ne kuma Mai Karimci ‛

A farko -farkon Suratul -Isra’i Allah  Ya yabi bawanSa

Annabi Nuhu  saboda shi bawa ne mai yawan godiya ga

Allah, inda Yake cewa:

[

ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ

]

:اإلرساء{

3

}

‚Lallai shi (Annabi Nuhu ) ya kasance bawa ne mai

yawan godiya ‛

84 Wanda shi Annabin Allah ne, kuma Allah  Ya baashi ilimi mai faxin gaske, sannnan

kuma Ya bashi mulki sama da na kowa daga cikin bayi, domin kuwa bayan mutane har ma

da aljanu da dabbobi dukka yake mulka, kuma idan yayi umurni babu mai sava masa daga

cikinsu.

67

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

67

Duk mai godiya ga Allah (godiya irin ta shari’a85) toh

haqiqa yay i koyi da Annabawan Allah (Tsira da Amincin

Allah su qara tabbata garesu baki xayansu).

Hakan zai sa Allah  Ya qara masa, kuma Ya albarkaci

rayuwarsa, kuma Ya yarda da shi, kuma Allah  Zai tsare

shi daga uqubarSa ta duniya da lahira (irin wacce Yake yi

wa masu butulci).

Wannan kenan!

Sannan akwai kuma irinsu qaruna, waxanda suka butulce a

yayinda suka ga sun bunqasa. Sai Allah  Ya saukar da

uqubarSa akansu, Ya kawar da su.

Wasu Malamai daga cikin mutanensa sun yi ta masa wa’azi

akan ya daina alfahari da kuma girman kai, saboda hakan ba

xabi’a ce ta masu rabo a wajen Allah  ba. Shi kuma

qaruna sai qara cika baki yakeyi yana ta taqama. Bai ma

yarda cewa wannan dukiyar tashi daga Allah take ba. Gani

yake kamar iyawarsa ce ta bashi (saboda haka babu wanda

zai godewa, kuma ba zai bi umurnin kowa ba) .

Har ma yana hura hanci yana cewa cewa:

[

ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ ﭖ ﭗ

القصص: { ]

78

}

‚Ni fa (wannan du kiyar da kuke gani) na same ta ne

sakamakon ilimin da nake dake da shi (ma’ana: ilimina ne

ya bani, ba Allah ba)‛. Sannan saiYace:

85 Godiya irin wacce ake kira ‚Ash -shukr‛ a larabce; it ace yayin da bawa ya sarrafa duk

wata ni’imar da Allah I Ya baashi ta hanyar da Allah xin Ya yarda da shi. Idan dukiya ce

ko ilimi ko wani vangare na mulki da sauransu, toh lallai ne bawa ya kiyaye haqqin Allah a

ciki kuma Ya tsare dokokin Allah a yayin sarrafa su. Idan ‘ya’ya ne, lallai ne ne bawa ya

tarbiyyantar da su tar biyyah ta addini. Wannan shi ake kira godiya a shari’ance, ba

tsagwaran furta Hamdallah da fatar baaki kawai ba. Allah Yasa mu dace.

68

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

68

[

ﭘ ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ ﭟ ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ

ﭪ ﭫ ﭬ ﭭ ﭮ

]

Shin (wannan kangararren bawa) bai san cewa Allah  Ya

halakar da waxanda s uka fi shi tsananin qarfi da kuma t arin

dukiya ba a cikin qarnonin da suka shuxe gabanin sa, kuma

ba Ya tambayar masu laifi gameda (dalilin) aikata

zunubansu (idan Ya tashi halakar da su, domin kuwa babu

wani sauran hanzari garesu)‛ A can gaba sai Allah  Yace:

[

ﮗ ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ

ﮧ ﮨ

]

‚Sai muka sanya qasa ta haxiye shi daga shi har (katafaren)

gidan nasa (wanda yake alfahari da shi). Ya kasance bashi

da wasu tarin mutanen da za su iya taimakonshi (babu mai

kuvutar da shi daga wannan halaka) koma bayan Allah ,

kuma shi bai kasance daga cikin masu (ikon) taimakon

kawunansu ba‛

Abinda ya zama wajibi akan duk wanda Allah  Ya bashi

wani abu na jin daxi a rayuwarsa ta duniya, shi ne ya gode

wa Allah  (ya sarrafa wannan ni’ima ta hanyar neman

yardarSa). Kar yayi butulci, kar yayi xagawa ko taqama ko

cika baki. Banda qoro kuma banda al -mubazzaranci.

Idan ka godewa Allah , toh Zai albarkaci abin, kuma Zai

Yarda da kai. Idan kuma mutum ya butulce, toh ko shakka

babu qarshen lamarin ba zai masa daxi ba. Allah dai Ya

rufa mana asiri.

Idan aka jarabci bawa da wata wahala ko quncin

rayuwa, da sauran ababenda zuciyarshi bata so:

69

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

69

A irin wannan yanayi ana buqata bawa yayi haquri, ya

maida lamarinsa ga Allah , Ya kuma nemi ladar wannan

wahala a wajenSa.

Jarrabawa Sunnar Allah  ce. Kuma babu mai cin

jarrabawar Allah Ta’ala sai wanda Yayi wa gamon katar.

Allah Yasa mu cikin masu rabo.

Jarrabawa mai raxaxi (irinsu talauci da rashin lafiya da

sauransu) ba ta daga cikin alamun da suke nuna wai Allah

 ba Ya so n bawanSa. Domin kuwaYa jarabci hatta

manyan bayinSa ma da nau’ukan wahalhalu iri -iri a

rayuwarsu.

Haka kuma samun xaukaka a duniya, da havakar tattalin

arziki da sauransu, ba su suke nuna wai Allah  Yana son

mutum sama da waxanda basu samu ba.

Ayoyi da hadithai masu yawa sun tabbatar da cewa ‚Lallai

Annabawa da Manzanni (Tsira da Amincin Allah su qara

tabbata a garesu) su ne suka gamu da jarrabawa mafi tsanani

daga cikin bayin Allah. Sannan kuma duk wanda ya bi

tafarkinsu, toh zai samu jarrabawarsa gwarg wadon iya

koyin da yayi da su. Domin kuwa ana jarabtan bawa ne

gwargwadon qarfin Addininsa.‛

Annabawa da Manzanni masu yawa jama’ansu sun qaryata

su, an zage su, an musu izgilanc i. Wasu an kore su daga

gari, was u an kama su an kulle a gidan y ari anyi ta ga na

musu azaba, wasu ma kisan gilla akayi musu. Wasu daga

cikin Annabawan kuma, tsantsar talauci da matsatsi sukayi

ta fama da shi, akwai wanda ya kamu da rashin lafiya mai

tsanani, akwai ma wanda ya shiga yanayinda har kifi ya

haxiye shi..

Amma duk hakan b ai hana su ci gaba da tabbata akan

wannan Tafarki madaidaici ba. Sun tsayu akai, sun jajirce

70

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

70

sun cigaba da kiran jama’arsu akai har Allah  Ya karvi

rayuwarsu.

Haka akeso mu ma mu zama. Mu nemi taimakon Allah 

akan duk wata wahala ta rayuwa, da fatan All ah Ya hana ta

tasiri wajen kautar damu hanya.

Waxannan nau’uka na jarrabawa masu raxaxi suna da nasu

amfani ga bawa matuqar dai ya karvi lamarin da zuciya

guda (matuqar ya yi haquri ya maida komi ga Allah 

kuma ya nemi l adan hakan a wajenShi). Idan har y ayi

hakan, toh Zai yafe masa laifukansa kuma Zai bashi lada

mai yawa.

Allah  Ya yi alqawarin Zai xaukaka darajar masu haquri,

Zai tabbatarda su akan Tafarkin shiriya, Zai Gafarta musu

zunubansu, sannan kuma Zai musu Rahama a duniya da

lahira.. Babban misa li akan wannan shi ne (cikin Suratul -

Baqara, ayah ta 155 - 157) inda Allah  Yake cewa:

[

ﭠ ﭡ ﭢ ﭣ ﭤ ﭥ ﭦ ﭧ ﭨ ﭩ ﭪ ﭫ

البقرة: { ]

155

}

‚Kuma lallai ne, za Mu jarabce ku da wani abu na tsoro da

yunwa, da tawaya daga dukiya, da (asarar) rayuka da na

‘ya’yan itace (amfanin gona). Don haka kayi bishara ga

masu haquri‛

[

ﭮ ﭯ ﭰ ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ

]

:البقرة{

156

}

‚Su ne waxanda suka kasance idan wata masifa ta same su,

sais u ce: lalle mu daga Allah  muke, kuma lallai zuwa

gareShi za mu koma‛

[

ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ

]

البقرة{:

157

}

71

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

71

‚Waxannan lallai akwai Albarkatu da kuma Rahma (da za

su riqa sauka) akansu daga Ubangijinsu, kuma waxannan su

ne shiryayyu‛.

Rashin Lafiya

Idan Musulmi ya kamu da rashin lafiya, wannan ciwo zai

zama kaffarah gareshi (za a kankare masa laifinsa) ma tuqar

ya maida lamari ga Allah , ya yarda da hukuncin Allah ,

ya yarda cewa Allah  ne ya xora masa.

Allah  Yana xora wa bawa irin waxannan nau’uka na

jarrabawa ne, saboda Ya kankare masa zunubansa dasu,

sannan kuma Ya bashi lada mai yawa, kuma Ya xaga

darajarsa.

Manzon Allah  yana cewa: ‚Babu wani abinda zai sami

Musulmi (a rayuwarsa) na yunwa ko rashin lafiya ko

damuwa ko baqin ciki ko wata cutarwa ko wani qunci –har

ma da qayar da za ta soke shi - fahce Allah Ya kankare masa

laifukansa da su86‛

A ciki n wani hadisin (riwayar Tirmidhiy daga Sahabi Abu -

Huraira ) Manzon Allah  yace: ‚Jarrabawa ba za ta

gushe ba (tana sauka) ga mumini [da kuma mumina] a cikin

jikinsa ko ‘ya’yansa ko dukiyarsa, har sai gamu da Allah 

(a lahira) babu wani laifi akansa (dom in kuwa Zai kankare

masa zunubansa sakamakon raxaxin da yayi ta ji a yayinda

wannan jarrabawa ta same shi)‛.

Ashe idan mumini ya kamu da rashin lafiya, wannan wata

dam ace da Allah  Yake bashi don ya tuba ya koma ga

Allah, kuma ya samu ladan haquri, sanna n kuma ciwon ya

zama kaffara gareshi gameda zunuban da ya aikata. Shi yasa

86 Bukhari ( 5643 ), da Muslim ( 2573 ) Daga Abu -huraira t da Abu -Sa’id Al -khudri 

72

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

72

Manzon Allah  ya kasance idan yaje duba mara lafiya

musulmi, daga cikin addu’o’inda yake masa akwai:

َلَ بَأْسَ طَيُورٌ إِن شَاءَالماوُ

‚Babu laifi, ciwon naka mai tsarkakewa ne ( daga

zunubanka) in Allah Ya Yarda87‛

Haquri gameda rasuwar xa ko xiya:

Idan bawa yayi haquri ya daure kuma ya nemi lada gun

Allah  a yayinda ya rasa xa ko xiya, toh hakan ma

yana daga cikin hanyoyin samun Gafarar Allah (bayan

xumbin ladan da zai samu saka makon hakan)

insha’Allah.

Manzon Allah  yace: ‚Babu wasu musulmi biyu (miji

da matarsa) da za su rasa ‘ya’ya qanana har guda uku

(kuma suyi haquri su mayarda lamarinsu ga Allah )

fahce an Gafarta musu88‛

A wata riwayar ma, Manzon Allah  cewa yayi: ‚Duk

wanda ya nemi lada (haqurinda yayi) gameda rashin har

(‘ya’ya) uku daga cikin tsatsonsa, toh zai shiga Aljannah

(sakamakon hakan)‛. Sai wata mace tace: ‚Har da mai

biyu ma (Y a Manzon Allah)?‛ Yace mata: ‚Har mai

biyu ma89 (shi ma zai samu irin wannan sakamak o)‛.

Wasu hadisai ma sun tabbatar da cewa hatta wanda ya

rasa xa guda ma zai samu irin wannan sakamako

87 Bukhari ( 3616 ) daga Abdullahi xan Abbas Al lah Ya qara musu Yarda (shi da mahaifin

nashi).

88 Nasa’i (Hadithi na 1874 ) daga Sahabi Abu -Dharrin Al -Ghifariy 

89 Musnad na Imamu Ahmad (Hadithi na 27429 ) Daga Sayyida Ummu -Sulaim (Mahaifiyar

Anas xan Malik) Allah Ya qara musu yarda.. Akwai ma’anar wanna n hadithi cikin Sahihul -

Bukhari da kuma Sahih Muslim a wurare daban daban.

73

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

73

insha’Allah. Da sharaxin dai za ayi haquri tun a farkon

fari, a mayar da lamari ga Allah , kuma a nemi ladan

wannan haquri da juriya awajenSa. Toh idan har bawa

ya rasa xansa kuma yayi haquri ya maida komai ga

Ubangijinsa, Allah  Zai ce wa Mala’iku: ‚Ku gina wa

bawa Na gida a cikin Aljannah, kuma ku sanya wa

gidan suna بَيْتُ الْحَمْدِ (gidan godiya, wanda sai masu

godiya ga Allah akan komai ne kaxai zas u sami

irinta)90‛

Manzon Allah  yace: ‚Babu wani wata kyautar da za

baiwa wani (daga cikin bayi) wacce take cike da

Alkhairi kuma wadatacciya irin kyautar haquri91‛.

Saboda girman matsayin haquri, babu wanda yasan

yawan ladan da bawa zai samu idan yayi haqu ri sai

Allah  kaxai.

A cikin Suratuz -Zumar (ayah ta 10) Allah  Yana cewa:

[

ﰓ ﰔ ﰕ ﰖ ﰗ ﰘ ﰙ

الزمر: { ]

10

}

‚Masu haquri ne kaxai ake cika musu ladan sub a tare da

qididdiga ba‛

Renon ‘ya’ya mata, da kuma kyautata Tarbiyyarsu har

su girma.

Wannan ma yana dag a cikin muhimman hanyoyin samun

Gafarar Allah , da RahamarSa da AljannarSa.

Manzon Allah  yace: ‚Duk wanda aka jarabce shi da

(renon wani adadi daga cikin) waxannan ‘ya’ya mata, kuma

90 Tirmizi (1021) daga Abu -Musa Al -Ash’ari . Hadithi ne mai kyau. Duba As -Sahiha

(1408 ).

91 Bukhari (6470) da Muslim (1053) daga Sahabi Abu -Sa’id Al -khudri 

74

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

74

ya kyautata musu (tarbiyyah), toh za su kasance gareshi

shamaki tsakani nsa da wuta (a gobe qiyamah)92‛.

A wata riwayar Imam Ahmad da Ibnu Majah kuma,

Manzon Allah  cewa yayi: ‚Duk wanda ya kasance yana

da ‘ya’ya mata har uku, kuma yayi haquri (ya daure ya

tarbiyyantar dasu) ya ciyar dasu ya shayar dasu ya kuma

tufatar dasu da ga abinda ya mallaka; toh za su kasance

shamaki gareshi daga wuta a ranar tashin qiyamah‛.

Daurewa a kyautata Ibada a yayinda ake cikin tashe -

tashen hankula da kashe -kashe

Sau da dama (musamman a wannan zamani) ana samun

tashe -tashen hankula a yankunan da muke yaruwa. Mutane

za su lalace suyi ta varna, kuma babu mai hana su. Za a

wayi gari ana ta’addanci iri -iri. Masu Mulki su kangare suyi

ta cin zalin talakawansu. Kuma sau da dama babu waxanda

aka fi cutarwa a irin waxannan lokuta irin masu riqo da

addini.

Toh idan bawa yayi haquri ya daure ya jajirce ya tsaya ya

bauta wa Allah a irin wannan lokaci, toh hakan yana daga

cikin hanyoyin samun Gafarar Allah .

Domin kuwa Manzon Allah  yana cewa: ‚Bautar Allah

acikin lokaci na haraj (wato kashe -kashe da yaqe -yaqe)

kamar hijira ce zuwa gareni93‛.

Sanannen abu ne kuma Hijira ma tana shafe abinda ya

gabaceta na laifuka, kamar yadda Imam Muslim y a ruwaito

(hadisi na 121) daga Sahabi Abdul lahi xan ‘Amru xan As,

Allah qara Yarda dasu baki xayansu.

92 Bukhari (5995), Muslim (2629), Dukkansu daga Nana A’isha Allah Ya qara Yarda da

ita.

93 Sahih Muslim (Hadithi na 2948) daga Sahabi Ma’aqili xan Yasaar 

75

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

75

Ko shakka babu idan har bawa ya jajirce ya tsaya akan

gaskiya a irin lokacinnan da mutanen banza sukayi yawa

hatta cikin al’ummar Musulmi, toh zai samu babbar daraja

awajen Allah . Allah  Zai bashi ladan haquri, kuma Zai

sanya shi cikin bayinSa nagari (mas u rabauta a duniy a da

lahira).

Shi yasa a cikin Suratu -Hud (ayah ta 11) Allah  Yake

cewa:

[

ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﯟ ﯠ ﯡ ﯢ ﯣ

]

‚Sai waxanda sukayi Imani kuma suka aikata ayuka na

qwarai, waxannan kam suna da Gafara da kuma Lada

mai Girma‛

Haka kuma idan bawa yayi haquri saboda wata cutarwar

da akayi masa (aka ci masa mutunci, akayi masa izgili

ko qage da yarfe da qazafi da kuma vata suna) ba don

komai ba sai don kaxai ya yi riqo da addin Allah, Toh

hakan yana daga cikin hanyoyin samun Gafarar Allah,

da AljannarSa.

Allah  Yace irin bayin nan naShi waxanda aka cutar dasu

(akayi ta musu izgilanci a duniya sakamakon riqon su da

addini), toh zai saka musu a lahira saboda haqurinda sukayi.

Zai saka musu da Aljannah, kuma Zai goranta wa masu yi

musu izgili (bayan su kuma masu izgilin suna cikin wuta).

Acikin Suratul -Muminun (ayah ta 109 - 111) Allah  Yana

cewa:

[

ﭱ ﭲ ﭳ ﭴ ﭵ ﭶ ﭷ ﭸ ﭹ ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ

‚Lallai wani kaso daga cikin bayiNa sun kasance suna cewa

Ya Ubangijin mu munyi imani, saboda haka Ka Gafarta

76

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

76

mana kuma Kayi mana Rahma, domin kuwa Kai ne Mafi

Jinqan Masu Jinqai.

ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ

Sai ku kuma kuka riqe su ababen yiwa izgili (kuna ta

tsokanarsu saboda sunyi riqo da addini), har (suka shagaltar

daku) suka mantar daku ambato Na, kun kasance kuna ta

musu dariya (saboda kawai sunyi ima ni).

ﮉ ﮊ ﮋ ﮌ ﮍ ﮎ ﮏ ﮐ ﮑ

]

Toh lallai Ni Na saka musu yau (Na basu Aljannah) saboda

haqurinda sukayi (akan cutarwar da kukayi ta musu a

duniya), lallai kuwa su xinnan su ne masu babban rabo‛.

Shi ma wanda akayiwa qazafi don neman ganin bayansa

saboda kawa i ya yi riqo da addini, Allah  Ya yi masa

alqawarin Gafara da kuma girmamawa. Ya faxi hakan ne a

cikin Suratun -Nur (qarshen ayah ta 26, cikin ayoyinda Ya

wanke Uwar mu Nana -A’isha daga qazafinda munafukai

sukayi mata94).

Allah  Yace:

[

ﯥ ﯦ ﯧ ﯨ ﯩ ﯪ ﯫ ﯬ ﯭ ﯮ

]

‚Irin waxannan su ne waxanda ake barrantarwa daga

abinda (masharranta) suke faxa. Suna kuma da Gafara

da kuma wani irin Arziki na girmamawa‛

94 Hadisin wannan qazafi ya zo cikin littatafan hadisi da kuma sirah masu yawa. Babban

misali akan wannan, shi ne hadisi na 4141 cikin Sahihul -Bukhariy, hadithin Nana -A’isha

xin (ita da kanta ta bayar da wannan labara). Waxanda suka kitsa wannan qazafi dai sunyi

ne saboda cin mutunci ga Manzon Allah  gameda iyalansa. Kuma abin takaici, ‘yan shi’a

suna ci gaba da zargin ta da wann an laifi, bayan Allah  Ya wanke ta a cikin Al -Qur’ani.

Kuma daga baya su saxaxo su ce wai su ma suna qaunar Manzon Allah . wallahi qarya

sukeyi. Su cikakkun maqiya ne ga Allah da ManzonSa da kuma AddininSa.

77

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

77

Idan aka zartar da haddi (irin na shari’a) akan bawa

saboda wani laifinda ya aikata:

Haddin da akayi wa bawa y ana shafe wannan laifinda yayi.

Zai zamto kaffarah gareshi, ta yadda ba za ayi masa uquba

akan wannan laifin ba a lahira. Saboda haka haddi ma yana

daga cikin hanyoyin samun Gafarar Allah  kenan.

Za mu ga shaidar hakan a cikin hadisin wata matar da aka

tsayar mata haddin rajamu (jifa da tsakuwa sakamakon an

kama ta da laifin zina alhalin ta tava aure) a zamanin

Manzon Allah .

Bayan ta mutu ai Manzon Allah  ne yayi mata Sallah. A

lokacinda ya shige gaba don ya jagoranci Sallar ma, har

Sayyiduna Umar  yake cewa: ‚Y a Ma’aikin Allah ta yaya

kuma (kai da kanka) za ka sallaci wannan mata alhali kuma

zina tayi?‛ Sai Manzon Allah  yace masa: "Haqiqa ta yi

wani irin tuba wanda ko da za raba wa mutum saba’in daga

cikin mutanen wannan birni na Madinah, da zai is he su95‛

Fitintinun Qabari (Allah Ya tsare mu)

Daga cikin Musulmi ma akwai waxanda za a fitinesu a cikin

qaburburansu. Za a fitini kowa daga cikinsu ne

gwargwadon aikinsa, sai wanda Allah Ya kuvutar dashi

kawai .

Manzon Allah  yace Shahidi ne kaxai ba za a fitine shi ba

a cikin qabarinsa96. Har ma yace: ‚Da ace akwai xaya (daga

cikin mutane) da zai kuvuta daga matsa irinta qabari, da

kuwa (Sahabi) Sa’adu xan Mu’azu  ne zai tsira97‛

95 Muslim (Hadisi na 1696) daga Sahabi Imran xan Husain .

96 Imam An -Nasa’iy (hadisi na 2053 ). Yana ma cikin littafin At -Ta’liq ar -Raghib ( 2/197 )

97 Imam Ahmad, daga Abdullahi xan Umar (Allah Ya qara yarda da su). Shaykh Albaniy

yace hadisin ya inganta (duba As -Saheeha, hadithi na 1695 )

78

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

78

Mutane sun kasu har wajen kashi biyar daban -daban a cikin

rayuwar su ta qaba ri:

a. Akwai waxanda su kam azaba ce zallah iri -iri zasu yi ta sha

tun daga cikin qabari har zuwa lahira, kuma za su dawwama

a wuta.. Waxannan su ne Kafirai da kuma Munafukai.

b. Akwai kuma waxanda su ma za su sha azabah a cikin

qabari, kuma a lahira za su shiga wuta su daxe a ciki.

Amma su ba za su dawwama a cikinta ba, saboda ba akan

kafirci suka mutu ba. Illa iyaka za a musu uquba ne

sakamakon zunubansu masu yawa sosai (waxanda har suka

mutu basu tuba sun daina ba), kuma ba’a ga damar yafe

musu ba. Daga baya z a a fitar dasu daga wutar, a wanke su,

a shigar dasu Aljannah.

c. Akwai wanda ni’ima zai ta sha tun daga farko har qarshe a

qabarinsa. Wani ma ko tambaya ba za ayi mas aba. Idan

kuma yaje lahira zai shige totar zuwa Aljannah. Allah Yasa

mu ne.

d. Akwai wani kuma matsa guda kawai za ayi masa na wani

xan lokaci, daga nan shi kenan, babu wata fitina. Kuma a

lahira Aljannah zai shiga.

e. Akwai kuma wanda za ayi masa azaba a Qabarinsa na wani

lokaci don a wanke shi a tsaftace shi daga zunubansa.. Daga

baya sai a xauke wa nnan azabar, a sanyaya masa a musanya

masa da ni’ima.. Irin waxannn ne babban Malami

(Shaykhul -Islam) Ibnu Taymiyyah Rahimahullah yake

cewa: ‚Abindfa yake faruwa a cikin qabari na fitina da shan

matsa da kuma firgici da razani, waxannan suna cikin

ababenda ake kankare laifuka da su98‛

98 Fataawa (juz’i na 7, shafi na 308), bugun Daarul -wafaa’i, Tahqiqi da Takhrijin Aamir

Al-Jazzar da kuma Anwar Al -baaz

79

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

79

Allah Ya tsare mu daga fitina da kuma azabar qabari, da

kuma azabar wuta. Allah Yasa Aljannah ce makomar mu a

gobe Qiyamah.

Allah  Yana karvar addu’ar da mumini yayi w a xan -

uwansa mumini, musamman ma wacce akayi masa a bayan

idonsa (ba tareda ya sani ba).

Malamai suka ce ko wanne Musulmi yana da wasu haqqoqi

akan xan -uwansa Musulmi. Daga cikin waxannan haqqoqin

dai, dol e ne a roqa masa gafara (sawa’un yana raye ne ko

bayan ya mutu).

Akwai ayoyin Qur’ani da ingantattun hadithai da suka

tabbatar da wannan qa’idar da suka ambata . Daga cikinsu

akwai faxin Allah  (akan harshen bayinSa na qwarai masu

yiwa magabatansu addu’a):

80

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

80

[

ﭖ ﭗ ﭘ

ﭙ ﭚ ﭛ ﭜ ﭝ ﭞ

ﭡ ﭢ

ﭣ ﭤ ﭥ

ﭦ ﭧ ﭨ

احلرش: { ]

10

}

‚Ya Ubangijinmu Ka gafarta mana, mu da ‘yan -uwanmu da

suka riga mu da imani (bayinKa na qwarai waxanda suka

shuxe). Kada Ka sanya wani qulli (na qiyayya da gaba) a

cikin zukatanmu gameda waxanda suka yi imani. Ya

Ubangijinmu lallai Kai ne Mai Tausayawa kuma Mai

Jinqai‛

Sannan kuma sanannen abu ne cewa duk wani Musulmin da

ya mutu, toh dole ne sauran ‘yan -wansa Musulmi su yi

masa jana’iza kuma su binne shi. Wannan haqqi ne

tabbatacce a cikin shari’ar Mu sulunci.

Kuma Manzon Allah  Ya tabbatar mana cewea matuqar

Musulmi ya sauke wannan hakki, toh fa yana da xumbin

lada wajen Ubangiji .

Yace: ‚Idan har bawa ya halarci Sallar jinaza ta xan -uwansa

Musulmi, toh yana da lada kwatankwacin qiraxi99 guda.

Idan kuma ya tsaya ya raka gawar har aka binne ta, toh yana

da Qiraxi biyu na lada‛

Sannan kuma wannan Sallah da za ayi wa mamaci, tana ma

da amfani gareshi sosai. Saboda tana daga cikin hanyoyin

samun gafara gareshi.

Manzon Allah  yana cewa: ‚Babu wani mamaci (cikin

Musulmi) da wani kaso na al’ummar Musulmi za su sallace

shi su kimanin mutum xari, kuma kowanne daga cikinsu

99 Malamai suka ce Kalmar Qiraxi yana nufin: tsauni mai girma, wanda qaraminsa ma ya

kai kamar girman dutsen uhudu (duba Musnad na imam Ahmad, hadisi na 10079 , daga

Sahabi Abu -Huraira ).

81

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

81

yana neman a b ashi ceton sa, fahce sai an b asu ceton

nashi100‛.

A wata riwaya kuma101, Manzo  cewa yayi: ‚Babu wani

mutum musulmi da zai mutu , kuma a samu har mutum

arba’in waxanda basu shirka su tsaya su sallaci gawarsa

fahce sai Allah  Ya basu ceton sa (zai gafarta masa

sakamakon wannan addu’ar da sukayi masa, matuqar shi

xin ma ba ya shirka)‛.

Allah  Zai yafe masa duk laifukanda yayi masa. Sauran

abinda yake tsakaninsa da mutane kuma, wannan shi dasu.

Sai mu kiyaye sosai gameda haqqin mutane.

Shi yasa ma malamai suka ce yana da kyau mu riqa

rubutawa mu ajiye, saboda wata rana. Amma fa lallai ne

muyi qoqarin biya da kanmu ne. Idan kuma hakan bai samu

ba har lokaci yayi, toh magadanmu za su sani ta hanyar

abinda muka rubuta muka ajiye.

Mu da Allah  Yasa muke raye a halin yanzu, ya kamata

mu sani ba fa iyawar mu ba ce. Dole wata rana mu ma za

mu mutu. Kuma na tabbata kowa daga cikinmu yana

buqatar a riqa sanya shi cikin addu’a bayan ya mutu. Toh

yana da kyau mu ma yawaita roqa wa mamatanmu Gafarar

Allah  (musamman iyayenmu da sauran makusanta).

Mu gaggauta biya musu basussukan da ake binsu don su

samu sauqi. Tabbas yin hakan yana daga cikin ka yutatawa

garesu a matsayinsu na waxanda suka riga suka rasu.

Idan ma akwai bashin azumi akansu (musammanma na

bakance) mu daure mu rama musu. Idan ma mun samu ikon

zuwa muyi musu aikin Hajji ko Umrah (ko dukka biyun),

toh muyi musu (bayan mu munyi n amu). Waxannan

dukkansu suna cikin kyautatawa garesu. Kuma zasu amfa na

100 Muslim (Hadithi na 947) daga Sayyida Nana A’isha da Anas xan Malik, Allah Ya qara

musu yarda.

101 Muslim (Hadithi na 948) daga Sahabi Abdullahi xan Abbas Allah Ya qara musu Yarda.

82

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

82

da hakan sosai insha’Allah. Mu ma kuma za mu samu lada

insha’Allah.

Babban abinda yafi dacewa dai shi ne; kowa ya dage

yayiwa kansa da kansa. Wannan shi yafi dacewa.

Kar mutum ya tsaya wai y a dogara da abinda magada zasu

yi masa bayan ya mutu. Domin kuwa duk yadda za su tuna

da kai, ba za su tuna ka kamar yadda suke tuna kawunansu

ba. Kuma da ma ba akan komai da komai za su iya maka

wani abu ba (sai cikin wasu ‘yan taqaitattun al’amura ne

kawai). Duk kuma abinda za sum aka xin ma, toh fa wakilci

ne kawai, ba zai kai abinda kai za ka yiwa kanka da kanka

ba. Bahaushe kuma yace zuwa da kai ya fi saqo.

Saboda haka mu dage wajen ganin mun amfana da wannan

damar rayuwa da Allah  Ya bamu kafin mu m a ta kuvce

mana. Domin kuwa babu makawa za ta qare.

Allah Ya rufa mana asiri, kuma Yasa mu cika da imani.

Ceton Manzon Allah  gaskiya ne. Imani da shi ku ma dole

ne. Babu mai musun hakan sai mara rabo.

Ceton da Allah  Yayi izni, kala biyu ne (xaya Ya kevance

ManzonSa Muhammadu  shi kaxai, xaya kuma shi da

sauran manyan abyin Allah):

1. An kevance Manzon Allah  wajen bashi ceton duk bayi

(mutane da aljanu), don ayi hisabi a baiwa kowa sakamakon

abinda ya aikata a rayuwarsa ta duniya.

-Sannan kuma an kevance shi da ceton ‘yan Aljannah ma. Su

ma zai cece su a gobe qiyamah. Domin kuwa dole sai ya

qwanqwasa qofar Aljannah tukunna kafin a buxe wa bayi su

shiga.

83

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

83

-Haka nan kuma akwai ceton sa ga baffan sa Abu -Talib.

Domin an rage masa raxaxin azabar da ake masa a cikin wuta,

sakamakon irin matsayinsa wajen Manzon Allah . Wannan

dai shi ne iyaka amfanin da zai masa, tunda ya mutu bai

musulunta ba. Allah Yasa mu cika da imani.

2. Sannan akwai ceton da aka bashi amma ba a kevance shi shi

kaxai ba. Hatta Mala’iku da sauran Annabawa da Manzanni

da kuma sauran salihan bayi ma za a basu irin wannan c eto na

biyu; shi ne ceton da za ayi wa masu laifi (wasu za a cece su

daga shiga wuta, wasu kuma sai an shigar da su wuta an fara

musu azaba na wani lokaci sai a bada iznin cetonsu ga masu

ceto daga baya ).

Sannan kuma ceto yana da sharuxa guda biyu ne, waxanda

dole sai sun cika kafin ya tabbata.

a. Dole sai wanda Allah Yayi wa izni ne kaxai zai yi ceto.

b. Kuma dole sai wanda Allah  Ya ga dama kaxai za a ceto

daga cikin bayinSa (kuma a lokacinda Ya ga dama).

Ya tabbata cikin littafin Imam At -tirmidhi, Manzon Allah 

yana c ewa: ‚Akwai ceto na ga ma’abota kaba’irai (manyan

laifuka) daga cikin Al -ummah ta102‛

Idan fa akace masu aikata kaba’ irai anan; ana nufin masu

aikata sauran kaba’irai ne (banda shirka103a ciki). Dom in shi

kam duk wanda ya mutu bai tuba daga gareshi ba, toh babu

wani ceton da zai amfane shi. Allah  yace:

[

ﭑ ﭒ ﭓ ﭔ ﭕ

املدثر: { ]

48

}

‚Saboda haka ceton masu ceto ba zai amfane shi ba (saboda

ya mutu bai tuba ba daga kafircinsa ba )‛

102 Tirmidhi ne ya ruwaito shi, daga Sahabi Jabir xan Abdullahi, da kuma Anas xan Malik,

Allah Ya qara musu Yarda su dukansu.

103 Duba Kitabut -Tauhid na Al -Imam Ibnu -khuzaimah (Allah Ya Gafarta masa).

84

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

84

Don haka dai ceton da Manzao  ya ambata a cikin wannan

hadisi, yana nufi cetonsa ga ma’abota kaba’irai ne waxanda

suka mutu basu tuba ba, sannan kuma babu shirka a cikin duk

laifukan nasu. Toh su ne wannan ceto zai shafa Insha’Allah.

Sahabi Auf xan Malik  yace wata rana ya ji Manzo  yana

cewa: ‚Wani mai tahowa ya taho gareni daga gun Ubangijina,

ya bani zavi tsakanin (ko dai) a shigar da rabin Al -ummah ta

Aljannah ko kuma a bani ceto. Sai na zavi a bani ceton nan.

Kuma shi (ceton) zai kasance ne ga wanda ya mutu (daga

cikin Al’ummah ta) alhalin ba ya haxa Allah da komai a cikin

bauta‛104.

Munyi Imani da ceton Manzon Allah . Kuma muna roqon

Allah  Ya arzuqta mu da samun cetonsa a gobe Qiyamah.

Daga cikin Yalwatacciyar Rahamar Allah , akwai wasu

daga cikin bayinSa waxanda Zai Yafe musu a gobe

qiyamah, tareda kuma sun je sun same Shi da t arin zunubai,

amma a cikin laifukan nasu dai babu shirka. Domin kuwa

Allah  ba Ya yafewa duk wanda ya mutu bai tuba daga

shirka ba.

A cikin Suratun -Nisa’i ayah ta 48 Allah  Yana cewa:

104 Musnad na Imaam Ahmad (Hadithi na 24023), Tirmidhi (Hadithi na 2441), Ibnu Majah

(Hadithi na 4317). Dukkansu daga Sahabi Auf xan Malik .

85

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

85

[

ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵

]

‚Lallai Shi fa Allah ba Ya Gafarta wa idan aka y i masa

shirka (kuma har aka mutu aka ba’a tuba ba), amma Yana

yafe wa (idan aka aikata) koma bayan wannan ga wanda Ya

ga dama. Toh duk wanda Ya haxa Allah da wani a yayin

bauta, haqiqa ya qirqiri laifi mai girma‛.

A can gaba kuma (aya ta 116), sai Ya rufe ayar da cewa:

[

ﮒ ﮓ ﮔ ﮕ ﮖ ﮗ ﮘ ﮙ

]

{

النساء

:

116

}

‚…Kuma duk wanda ya haxa Allah da wani a yayin bauta,

haqiqa ya vata vata mai nisa‛

Saboda haka ma ya haramta Aljannah kwata -kwata ga

wanda Ya mutu yana shirka. Haka Ya faxa a can cikin

Suratul -Ma’idah (a qar shen ayah ta 72) inda Yake cewa:

[

ﭺ ﭻ ﭼ ﭽ ﭾ ﭿ ﮀ ﮁ ﮂ ﮃ ﮄ ﮅ ﮆ ﮇ ﮈ ﮉ

]

‚Lallai duk wand a ya haxa Allah  da wani a wajen bauta

(kuma har ya mutu bai tuba ba), toh haqiqa Allah  Ya

haramta mishi Aljannah, kuma makomarsa it ace wuta,

kuma waxannnan azzalumai (masu shirka) basu da wasu

mataimaka (babu wanda zai taimake su ya kyvutar dasu

daga wannan madawwamiyar azaba)‛

Saboda haka babban sharaxin samun Gafara ta Allah  (a

ko da yaushe) shi ne kuvuta daga shirka. Mannzon Allah 

yace: Allah  Yana cewa: ‚Duk wanda ya same Ni da

zunubai (masu yawa, ko d a kuwa yawan su ya kai) kusan

yawan qassai, amma kuma ya kasance ba ya haxa ni da

86

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

86

komai wajen bauta, toh Ni kuma Zan zo masa da

kwatankwacin ta na gafara105‛.

Akwai waxanda Allah  Zai Yafe musu tun a filin hisabi.

Zai rufa musu asiri Yace su shige kawai, tareda kuma suna

da zunubai masu yawa, amma da Yake babu shirka aciki sai

Yayi musu afuwa.

Su ne waxanda Allah  Zai musu hisabi mai sauqi inji

Manzon Allah .

Hadithi ya tabbata kan wannan al’amari a cikin Musnad na

Imamu Ahmad, Hadithi na 6944 , daga Sahabi Abdullahi

xan Amru xan As Allah Ya Qara musu yarda (shi da

mahaifin n ashi dukka).

Akwai kuma waxanda za su shiga wuta sakamakon

zunzurutun zunubansu, kuma duk waxanda aka baiwa izinin

yin ceto sunyi sun gama am ma banda su cikin waxanda za a

ceto xin, sai daga baya Shi kuma Allah  Yayi musu afwa

Ya fitar dasu daga wutar, Ya wanke su da wani ruwa mai

suna Ma’ul-Hayati (ruwan rayuwa), sannan Ya shigar da su

Aljannah. Su ne ma talakawan Aljannah, kamar yadda

ingant attun hadithai masu yawa suka tabbatar.

Akwai ma waxanda za a fara ajiye su akan wasu tuddai

dake tsakanin Aljannah da wuta (inda ake kira Tozon

la’arafi a hausance). Za a ajiye su a wajen su zauna na wani

lokaci (suna ganin Aljannah kuma suna ganin wuta, amma

basu shiga kowacce daga ciki ba) har zuwa wani lokacinda

Allah Ya ga dama, sannan daga qarshe su ma Ya shigar

dasu aljannah. Allah  Ya bada labarin waxannan bayi

naShi a cikin Suratul -A’araf (wajen ayah ta 46 zuwa 49

haka).

105 Sahih Muslim (Hadithi na 2687) daga Sahabi Abu -Dharrin Al -Ghifaariy 

87

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

87

Ba don komai yasa duk wan nan yake faruwa ba, sai don

kasancewar da ma can Allah  ba Ya nufin Ya azabtar da

bayinSa. Ba Ya kuma xora wa bawa sai abinda shi bawan

zai iya xauka.

Babu wanda za a azabtar a lahira fahce shi da kansa ya

tabbatarwa kansa cewa lallai ya cancanci hakan. D omin

kuwa shi ya jawo wa kansa. Saboda haka dole yayi kuka da

kansa, ba da wani ba.

Shi yasa a wani Hadithi Manzon Allah  yace: Allah 

Yana cewa: ‚Ya ku bayi na! Ku sani duk ayukan nan naku

dai (da kuke aikatawa) ina nan ina kiyaye muku su (babu

abinda z ai salwanta daga ciki). Sannan zan cika wa kowa su

(ta hanyar bashi littafin ayukansa a lahira). Saboda haka duk

wanda ya sami Alkhairi, toh ya godewa Allah  (saboda

Shi ne Ya datar dashi da wannan aiki nagari). Wanda kuma

ya samu kishiyar hakan, toh kar ya zargi kowa sai kansa

(saboda shi ya zava wa kansa bin tafarkin shaixan)106‛

Saboda haka duk wanda ya shiga wuta a gobe qiyamah, toh

fa shi ya saya wa kanshi wannan azabah da kuxinsa. Amma

Allah  kam, ba Ya nufin wata wahala da bayinSa. Allah 

Yace:

[

ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ

البقرة: { ]

185

}

‚Allah  Yana nufinku da sauqi, ba Ya nufinku da wahala‛

Saboda haka ne ma Ya sauqaqa mana nau’ukan Ibadah Ya

kuma yawaita mana su, Ya sanya wahala cikin ayukan savo,

Ya yawaita mana hanyoyin samun RahamarSa, Ya buxe

mana qofofi masu yawa na tsira saboda tausayinmu da

Yakeyi.

o Yana ruvanya mana Lada idan muka aikata wani aiki

nagari..

106 Sahih Muslim (Hadithi na 2577 ) daga Sahabi Abu -Dharrin Al -Ghifaariy 

88

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

88

o Yana Gafarta mana zunubanmu107

o A kullum kuma Yana kiranmu zuwa ga neman GafararSa,

don mu rabauta a duniya da l ahira.

A cikin Suratuz -Zumar (daga aya h ta 53 har zuwa ta 55)

Allah  Yana cewa:

[

ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳

﮴ ﮵ ﮶ ﮷ ﮸ ﮹ ﮺

]

Allah  Yana cewa: ‚(Ya Muhammadu) kace musu (Allah

 Yana cewa): Y a ku bayi na waxanda suka yi varna kan

rayukansu (suka zalunci kawunansu ta hanyar aikata

laifuka, sakamakon haka suka tara zunubai masu yawa)!

Toh kada ku yanke qauna daga Rahamar Allah (kada ku

xebe tsammani). Domin kuwa lallai Allah  Yana Gafarta

(wa bawa) zunubai gaba xaya. Saboda lallai Shi, Shi ne

kaxai mMai gafara, kuma Mai Jinqai‛

A cikin ayah ta gaba sai Ya cigaba da cewa:

[

﮻ ﮼ ﮽ ﮾ ﮿ ﯀ ﯁ ﯂ ﯃ ﯄ ﯅ ﯆ ﯇ ﯈

]

‚Kuma ku mayar da lamari zuwa ga Ubangijinku, kuma ku

miqa wuya gareShi (kada ku aikata abinda Ya hane ku,

kuma kar ku sava wa umurnin Sa), tun kafin azaba ta zo

muku, sa’annan kuwa ba za a taimake ku ba‛

Sanna kuma sai Yace:

[

﯉ ﯊ ﯋ ﯌ ﯍ ﯎ ﯏ ﯐ ﯑ ﯒ ﯓ ﯔ ﯕ

ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ

]

107 Ta hanyar Tuba da Istighfari, ko wani aiki nagari, ko wata hanya ta dab an cikin

waxanda aka ambata a wannan xan littafin (da sauran manyan littattafai na manyan

Malamai, Allah Ya Saka musu da Alkhairi).

89

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

89

‚Kuma ku bi mafi kyawun abinda aka saukar zuwa gareku

daga Ubangijinku tun gabanin azaba ta zo muku ba tare da

kunyi aune ba, kuma baku sani ba‛

Waxannan ayoyi dai suna nun a mana lallai ne mu gaggauta

tuba daga zunubanmu, mu gyara halayenmu, mu koma ga

Mahaliccinmu, tun kafin wannan dama ta kuvce mana (tun

kafin lokacin karvan tuba ya wuce).

Shi yasa ma Manzon Allah  yake cewa: ‚Lallai Allah 

Yana shimfixa HannunSa da da re saboda Karvar Tuban

wanda yayi laifi da rana, Yana kuma Shimfixa HannunSa

da rana saboda Karvar Tuban wanda yay laifi da dare, har

zuwa sa’anda rana za ta fito ta mafaxarta108‛

Ya kai/ke mai karatu mai daraja! Inai mana wasiyyah da

tsare dokokin Allah  da kuma jin tsoronsa.

Wannan it ace wasiyyar Allah  zuwa ga b aki xaya

bayinSa (tun daga kan mutanen farko har zuwa kanmu, ha

ma zuwa na qarshen zuwa duniya) kamar yadda Yake cewa

(cikin Suratun -Nisa’i daga ayah ta 131 zuwa ta 134):

[

ﮘ ﮙ ﮚ ﮛ ﮜ ﮝ ﮞ ﮟ ﮠ ﮡ ﮢ ﮣ ﮤ ﮥ ﮦ ﮧ

ﮨ ﮩ ﮪ ﮫ

ﮬ ﮭ ﮮ ﮯ ﮰ ﮱ ﮲ ﮳ ﮴ ﮵ ﮶ ﮷ ﮸ ﮹ ﮺ ﮻

]

‚Kuma Allah  Shi Yake da Mulkin (baki xaya) abinda ke

cikin sammai da (baki xaya) abinda yake cikin qassai.

Kuma lallai haqiqa Munyi wasici ga waxanda aka baiwa

littafi gabaninku (har ma) da ku (kanku) akan cewa (dole)

ku tsare dokokin Allah (ku ji tsoronSa). Idan kuma kuka

kafirce (kuka kangare kuka qi bin wannan umurni), toh fa

(ku sani) duk abinda yake cikin sammai da qassai baki xaya

108 Sahih Muslim (Hadithi na 2759) daga Sahabi Abu -Musa Al -Ash’ariy 

90

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

90

na Allah ne. Saboda haka Allah Ya kasance Mawadaci

kuma Godajje Ab in godiya (yadda imaninku ya kasance ba

zai qare Shi da komai ba, haka nan rashin imaninku ma ba

zai rage Shi da komai ba).

Ya qara tabbatar da cikar MulkinSa da kuma cikakken

ikonSa akan komai, da kuma cikar wadatarsa, da kuma

buqatuwar baki xaya halittu zuwa gareShi Shi kaxai, inda

Yake cewa (cikin ayah ta gaba):

[

﮼ ﮽ ﮾ ﮿ ﯀ ﯁ ﯂ ﯃ ﯄ ﯅ ﯆ ﯇

]

‚Kuma lallai Allah  Shi Yake da Mulkin (baki xaya)

abinda ke cikin sammai da (baki xaya) abinda yake cikin

qassai. Saboda haka Allah  Ya isa Ya zamto abin dogaro

(Shi kaxai ne Abin nufi da buqata ga baki xaya halittunsa,

Jallah Buwayi Gagara misali).

Saboda haka duk abinda muka aikata, toh fa kanmu mukayi

wa. Shi kam Allah cikakken Mawadaci ne. Idan ma Ya ga

dama cikin qasa da qiftawar ido Zai kawar da mu baki

xaya nmu Ya kawo wasu.

Hakan kuma ba komai ba ne a wajenShi. Domin kuwa Shi

Mai cikakken iko ne akan dukkan komai.

Shi ne a ayah ta gaba sai Allah  Ya qara da cewa:

[

﯈ ﯉ ﯊ ﯋ ﯌ ﯍ ﯎ ﯏ ﯐ ﯑ ﯒ ﯓ ﯔ ﯕ

]

‚Idan Ya ga dama Yana iya tafiyar da ku (Ya kawar da ku)

ku dai waxannan mutane, sannan kuma Ya taho da wasu

(mutanen) na daban (Ya maye gurbinku da su). Kuma Allah

 Ya kasance Mai (cikakken) iko ne akan hakan‛

KasancewarSa Mai cikakken iko akan komai da komai, Shi

kaxai Yake da ikon baiwa duk wanda Ya ga dama cik in

bayinSa abinda Yake nema na duniya da lahira.

91

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

91

Da ma daga cikin bayi akwai wasu Salihan bayi waxanda

lahira suke so, ko da kuwa sun samu wani abu a duniya, toh

suna amfani da shi wajen neman lahira. Irin waxannan su ne

masu tsira..

Akwai kuma waxanda d uniya kaxai suke so. Ba su da rabo

a lahira, saboda basu yi imani ba.

Toh duk wanda ka nema dai, babu wanda zai baka sai Allah

. Domin kuwa naShi ne Shi kaxai, Bai da abokin tarayya.

Kuma Yana bayarwa ne ga wanda Ya ga dama cikin

bayinSa.

Wannan yake qara tabbatar da tavewar masu dogaro akan

wanin Allah.

Allah Ta’ala Ya tabbatar mana cewa komai da komai naShi

ne, kuma Shi Yake baiwa wanda Yaga dama cikin bayinSa.

Sannan kuma Ya qara tabbatar mana lallai duk wanda yayi

aiki don duniya kaxai, toh fa bai da r abo a lahira. Zai iya

baiwa wanda Ya ga dama wani abu na duniya xin.

Wanda kuma yake neman lahira, toh sh i ma sakamakonsa

na Hannun Shi. Shi yasa a ayah ta gaba sai Yace:

[

ﯖ ﯗ ﯘ ﯙ ﯚ ﯛ ﯜ ﯝ ﯞ ﰀ ﰁ ﰂ ﰃ ﰄ ﰅ ﰆ

]

‚Duk wanda ya kasance yana nufin (samun) sakamak on

duniya ne, toh fa a wurin Allah  (kaxai) sakamakon

duniya (har ma) da na lahira yake. Kuma Allah  Ya

kasance Mai (cikakken) ji, kuma Mai (cikakken) gani (Yana

jin duk abinda kuke faxa, kuma Yana ganin duk abinda

kuke aikatawa, Yana kuma sane da duk ab inda kuke

qudurcewa a zukatanku, saboda haka Zai saka muku da duk

abinda kuka aikata)‛.

Waxannan ayoyi masu daraja suna qunshe da darusa

masu yawa. Kaxan daga cikinsu su ne kamar haka:

92

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

92

Suna qara tabbatar mana lallai Allah  Ya halicce mu ne ba

don komai ba sai don mu kaxaita Shi da bauta. Wannan

bauta kuma dole ne muyi ta Yadda Shi Ya tsara kuma Yayi

umurni, ba yadda muka ga dama ba.

Suna qara tabbatar mana lallai Shi fa Allah  ba wai Yana

buqatan wani abu ba ne daga garemu. Imanin masu imani

ba zai qare S hi da komai ba. Haka nan ma duk kafircin

kafir ai ba zai rage Shi da komai ba. Shi cikakken mawadaci

ne, mu ne muke buqatan komai daga gareShi.

Sannan duk kyakkyawan aikinda muka aikata, toh fa

garemu amfanin zai dawo. Haka kuma duk mumunan aikin

da muka ai kata, to akanmu sakamakon zai dawo. Kenan duk

abinda muka shuka a nan duniya, to fa shi za mu girba a

lahira. Saboda haka idan bawa ya samu Alkhairi a can, toh

ya gode wa Allah d omin kuw a Shi Ya datar da shi. Idan

kuma Ya je ya tarar da sharri, toh kar ya z argi kowa sai

kansa (domin kuwa s hi ne haqiqanin s akamakon abinda ya

vata lokacinsa a duniya yana ta aik atawa ).

Saboda haka lallai ne mu zama masu taka -tsan-tsan a

kullum. Mu tsare dokokin Allah, mu dage wajen aikata

ayuka nagari (tun daga farillai har zu wa nafilfilu), mu

nisanci sava wa Allah , mu gaggauta tuba mu koma

gareShi, mu kuma yawaita Istighfari a kullum, saboda fatan

samun Rahamar Allah .

Da fatan Allah Yasa mu dace da aikata abinda Zai Yarda da

mu, Ya qara tabbatar da mu akan Tafarki madaidai ci har

mutuwa, yasa mu cika da imani, Ya kuma sa Aljannah

Firdausi ce makomar mu a gobe qiyamah.

93

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

93

Haqiqa mai babban rabo a wajen Allah  daga cikin

mutane, shi ne wanda zai yi tanadin guzuri tun yana da

sauran dama.

Shi ne wanda zai shirya wa lahira tun k afin mutuwa ta

sauko masa. Yana amfani da damar da Allah  Ya bashi

don ganin ya shuka wa kansa Alkhairi kafin ya bar duniya.

Mara rabo a wajen Allah shi ne wanda yake wasa da damar

da Allah ya bashi, shi ne wanda yake shagaltuwa da wasu

al’amura na duniya (ya qi tsayawa ya bautawa Allah har

lokaci Ya qure masa). Sai ya ga azaba ido da ido sannan

yace wai zai tuba, a lokacinda hakan ba zai amfane shi da

komai ba.

Da ma kuma bahaushe yace ba a fafe gora ranar tafiya,

kamar yadda kuma ba a kiwon kare ranar fa rauta.

Sanannen abu ne garemu lallai mafi Alkhairin guzuri shi ne

Tsoron Allah . Da Tsoron Allah ne kaxai bawa zai samu

tsira a ranar tashin qiyama, ranar da dukiya da ‘ya’yan da

mutum ya tara ba za su amfane shi da komai ba.

Saboda haka lallai ne mu ji Tsoron Allah matuqar jin

tsoronSa, mu tsare dokokinSa, mu qara qaimi wajen

yawaita ayukan xa'a, mu nisanci savo. Muyi riqo da

karantarwar Manzon Allah . Mu yawaita Istighfari, mu

Tuba mu koma ga Alla . Shi kuma Allah  Ya yi

Alqawarin Zai mana Rahama mat uqar munyi hakan. Shi

kuma Allah  ba Ya sava Alqawari.

Idan har mun yarda cewa Alqawarin Allah  gaskiya ne,

toh fa lallai ne mu nemi YardarSa ta hanyar bin UmurninSa

da kuma nisantar abinda Ya hanemu. Wannan kuma shi zai

tabbatar da lallai ashe muna kyau tata wa Allah  zato.

Manzon Allah  yace: ‚Kada xayanku ya mutu fahce (ya

94

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

94

dage ya y aqi shaixan har ya zamto) yana mai kyautata zato

ga Allah ‛.

Ya faxi wannan magana ana sauran kwana uku kacal ya bar

duniya (kamar yadda Sahabi J abir xan Abdullahi ya faxa ,

Allah Ya q ara Yarda da su baki xaya). Wannan magana

tana daga cikin manyan wasiyoyinda dole ne muyi riqo

dasu sosai don mu samu tsira a duniya da lahira. Domin

kuwa tana cikin maganganun Manzon Allah  na qarshe -

qarshe.

Allah Yasa nu dace.

Dukkan Yabo da Godiya marasa misaltuwa sun tabbata ga

Allah Maxaukaki, wanda Ya nuna mana qarshen wannan

xan littafi cikin qoshin lafiya kamar yadda Ya nuna mana

farkonsa.

Muna roqon Allah  cikin RahmarSa Ya sanya mu cikin

bayin nan naShi masu gaskiya cikin imaninsu, m asu

kyautata niyyah cikin furucinsu da ayukansu, masu yawan

godiya gareShi gameda ni'imominSa, masu haquri da

dangana gameda duk jarrabawar da ta same su, masu Tuban

gaske zuwa gareShi daga dukkan laifukansu, kuma masu

neman GafararSa daga dukkan zunubai.

Da fatan Allah Mai Jinqai Ya karvi Tuban mu, Ya Gafarta

mana, Ya yafe mana, Yayi mana Jinqai, mu da iyayenmu da

'ya'yanmu da Malamanmu da sauran 'yan -uwanmu Musulmi

baki xaya. Allah Ya Gafarta mana, domin kuwa Shi Mai

yawan Gafara ne kuma Mai Jinqai.

Ya A llah Ka sanya mu cikin yardaddun bayinKa masu

kyautata Ibada. Ka qara tabbatar damu akan Tafarki

95

HANYOYIN SAMUN GAAFARA

95

Madaidaici har muutuwa, Ka tsare mu daga fitintinu da

kuma azabar qabari, Ka tsare mu daga azabar wuta, Ka sa

Aljannah ce makomar mu a gobe qiy amah.

Ya Allah K ayi daxin Tsira da Aminci ga wannan bawa

naKa kuma ManzonKa Annabi Muhammadu , shi da

Iyalansa da dukkan Sahabbansa, da sauran duk waxanda

suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

Ameeen.

وَالسَّالَمُ عَلَيُْكُْ وَرَْحَْةُاَّللَِّ وَبَرََكَتُهُ

— Ƙarshen Littafi —

H - HANYOYIN SAMUN GAFARA [b0de7885]

← Koma ga Bayani